< Ayyukan Manzanni 5 >
1 Sai wani mai suna Hananiya da matarsa Safiratu, suka sayar da filinsu,
Keegi mees nimega Ananias ja tema naine Safiira olid samuti müünud maatüki.
2 Hananiya kuwa ya boye wasu daga cikin kudin filin, (kuma da sanin matarsa), sa'annan suka kawo ragowar kudin a gaban manzannin.
Ta hoidis osa rahast naise teadmisel endale, ülejäänu ta tõi ja pani apostlite jalge ette.
3 Amma Bitrus ya ce, ''Hananiya don me shaidan ya cika zuciyarka, har ka yi wa Ruhu Mai Tsarki karya? Har ka boye wasu daga kudin filin?
Aga Peetrus ütles: „Ananias, kuidas on saatan nõnda täitnud su südame, et sa valetasid Pühale Vaimule ja hoidsid enesele osa maa eest saadud rahast?
4 Sa'adda ba ka sayar da filin ba, ba mallakarka bane? Bayan da ka sayar ma, ba naka bane? Don me kayi irin wannan tunanin a zuciyarka? To ba mutane ka yi wa karya ba, Allah ka yi wa.”
Eks see kõik ju kuulunud sulle, enne kui see müüdi? Ja pärastki oli see raha ikka sinu käsutuses. Mis sind on pannud mõtlema, et sellist asja teha? Sa ei ole valetanud inimestele, vaid Jumalale.“
5 Nan take da jin haka, Hananiya ya fadi ya ja numfashinsa na karshe. Dukan mutanen da suka ji labarin kuwa tsoro mai girma ya afko masu
Neid sõnu kuuldes kukkus Ananias maha ja suri. Ja suur hirm haaras kõiki, kes sellest kuulsid.
6 Matasa suka zo suka nannade gawarsa, suka fitar da shi waje suka binne shi.
Noored mehed astusid ette, mähkisid ta linasse, kandsid välja ja matsid maha.
7 Bayan wajen sa'a uku, sai matarsa ta iso, ba tare da sanin abin da ya faru ba.
Umbes kolm tundi hiljem saabus Ananiase naine, kes ei olnud veel kuulnud, mis oli sündinud.
8 Sai Bitrus ya ce mata, ''ki gaya mini ko nawa kuka sayar da filin?'' Sai ta amsa, ''ta ce kaza ne.”
Peetrus küsis ta käest: „Ütle mulle, kas te müüsite maatüki sellise hinnaga?“„Jah, “kostis Safiira, „selle hinnaga.“
9 Sa'annan Bitrus ya ce mata, ''Don me kuka shirya wannan makidar tare da mijinki don ku gwada Ruhun Ubangiji? Kiji tafiyar wadanda suka bizne mijinki a bakin kofa, kuma za su dauke ki yanzu.''
Peetrus ütles talle: „Mispärast on teil üks nõu olnud kiusata Issanda Vaimu? Vaata! Nende jalad, kes su mehe matsid, on ukse taga ja nad kannavad ka sinu välja.“
10 Nan take sai ta fadi a gabansa, ta ja numfashinta na karshe, matasan kuwa suka zo suka same ta ta mutu; sai suka dauki gawarta suka kai waje suka kuma bizne ta kusa da mijinta.
Samal silmapilgul kukkus naine tema jalge ette ja suri. Ja kui noored mehed sisse tulid, leidsid nad ta surnuna. Nad kandsid ta välja ja matsid ta mehe kõrvale.
11 Tsoro mai girma kuwa ya afko wa iklisiyar gaba daya da dakan wadanda suka ji wadan nan al'amura.
Jumalakartus tuli terve koguduse peale ja kõikide peale, kes sellest kuulsid.
12 Ayyukan alamu da ban mamaki masu yawa kuwa sun faru ga mutane, ta hannun manzannin. Dukansu kuma suna nan tare a dakalin Sulaimanu,
Apostlite käte läbi sündis palju tunnustähti ja imesid rahva hulgas. Ja kõik usklikud olid koos ühel meelel Saalomoni sammaskäigus.
13 Sai dai babu mai karfin halin ya hada kai tare dasu; amma suna da kwarjini sosai a gaban jama'a.
Ehkki muudest inimestest ei julgenud keegi nendega ühineda, olid apostlid rahva hulgas kõrgelt hinnatud.
14 Har wa yau aka rika samun karin masu ba da gaskiya, dinbin jama'a, maza da mata,
Siiski lisati nende hulka üha enam mehi ja naisi, kes Issandasse uskusid.
15 har sukan dauki marasa lafiya su kai su bakin titi, suna kwantar da su a bisa gadaje da shinfidu, domin idan Bitrus ya zo wucewa ko da inuwarsa ma ta taba wasunsu.
Nii et haiged toodi tänavatele ja seati vooditele ja asemetele, et Peetruse möödudes kasvõi tema varigi langeks mõne peale neist.
16 Mutane dayawa kuwa sukan zo daga garuruwan da ke kewaye da Urushalima, suna kuma kawo masu rashin lafiya, da wadanda aljannu ke damunsu, aka kuma warkar da su duka.
Ka tuli rahvast kokku Jeruusalemma ümbruse linnadest, tuues haigeid ja kurjadest vaimudest vaevatuid, kes kõik tehti terveks.
17 Amma babban firist ya taso tare da duk wadanda ke tare da shi (wato 'yan darikar Sadukiyawa); suka cika da kishi matuka
Aga ülempreester ja kõik ta kaaslased saduseride sektist muutusid kadedaks.
18 suka kama manzannin suka kuma jefasu a kurkuku.
Nad võtsid apostlid kinni ja heitsid nad üldvanglasse.
19 A cikin dare sai mala'ikan Ubangiji ya bude kofofin kurkukun ya kuma fito da su waje, ya ce,
Öösel tuli aga Issanda ingel, avas vangimaja uksed ja viis nad välja.
20 “Kuje ku tsaya a gaban haikali ku kuma gaya wa mutane maganar wannan rai.”
Ingel ütles neile: „Minge templisse ja kuulutage rahvale kõik selle elu sõnad!“
21 Sa'adda suka ji haka, sai suka tafi haikalin da wayewar gari suka yi koyarwa. Amma babban firist da jama'arsa suka zo suka kuma kira taro da kuma dukan yan majalisa, da dattawan jama'ar Isra'ilawa suka fito suka kuma ba da umarni, a fito masu da manzannin.
Päikesetõusu ajal läksid nad templisse, nagu neile oli öeldud, ja hakkasid õpetama. Aga kui ülempreester ja tema kaaslased saabusid, kutsusid nad kokku Suurkogu – Iisraeli vanematekogu. Ja nad andsid käsu tuua apostlid vangimajast kogu ette.
22 Amma ma'aikatan da suka je kurkukun basu sami kowa, a kurkukunba, sai suka dawo suka ba da rahoto,
Kuid vanglasse jõudes ei leidnud sulased neid sealt. Nad pöördusid tagasi ja teatasid:
23 Su ka ce kurkukun a rufe gam da masu gadi suna nan a tsaye a bakin kofar amma da muka shiga, bamu sami kowa a ciki ba.
„Me leidsime vangla kindlalt lukustatuna ja valvurid ustel valvamas. Aga kui me ukse avasime, ei leidnud seest kedagi.“
24 Yanzu sa'adda shugaban haikalin da manyan firistoci suka ji wadannan kalamai, sai suka rikice sosai game da su, suka ce yanzu me wannan zai haifar.
Seda aruannet kuuldes olid preester, templivalvurite kapten ja ülempreestrid segaduses, mõeldes, mis küll võis juhtuda.
25 Sai wani ya zo ya ce masu, ''Wadannan mutanen da kuka jefa a kurkuku suna can a cikin haikali suna koyar da jama'a.''
Siis tuli keegi ja teatas: „Vaadake! Mehed, kelle te panite vangi, seisavad templis ja õpetavad rahvast!“
26 Sai shugaban haikalin ya je da ma'aikatansa suka kawosu, ba tare da tashin hankali ba, domin gudun kada jama'a su jejjefesu.
Selle peale läks kapten sulastega kaasa ja tõi apostlid ära. Nad ei kasutanud jõudu, sest kartsid, et rahvas viskab nad kividega surnuks.
27 Da suka kawo su, sai suka gabatar da su gaban majalisa, babban firist kuwa ya tuhume su,
Nad tõid siis apostlid Suurkohtu ette ülempreestrile küsitlemiseks:
28 cewa ''Ba mun yi maku kashedi da karfi kada ku yi koyarwa cikin wannan sunan ba? Amma ga shi duk kun cika Urushalima da koyarwarku, kuna kuma neman kusa jinin mutumin nan ya sauko kanmu.”
„Eks me ole teid rangelt keelanud õpetamast selle nimel? Selle asemel te olete Jeruusalemma oma õpetusega täitnud ja kavatsete selle mehe surma tuua meie peale.“
29 Amma Bitrus da manzannin suka amsa suka ce, ''Dole mu yi wa Allah biyayya ba mutane ba.
Peetrus ja teised apostlid vastasid: „Jumalale tuleb rohkem kuuletuda kui inimestele.
30 Allah na ubanenmu ya ta da Yesu, wanda kuka kashe, ta wurin rateye shi a bisa itace,
Meie esiisade Jumal on surnuist üles äratanud Jeesuse, kelle teie olete tapnud, riputades ta ristipuu külge.
31 Allah kuwa ya daukaka shi a hannun damarsa, domin ya zama sarki da kuma mai ceto, ya ba Isra'ila tuba da gafarar zunubai.
Jumal ülendas ta oma paremale käele kui Juhi ja Päästja, andma Iisraelile meeleparandust ja pattude andeksandmist.
32 Mu kuwa shaidu ne ga wadannan al'amura, haka ma Ruhu Mai Tarki, wanda Allah ya bayar ga dukan wadanda suka yi biyayya a gareshi.''
Meie oleme kõige selle tunnistajad ja nõnda on ka Püha Vaim, kelle Jumal on andnud neile, kes talle kuuletuvad.“
33 Da yan majalisa suka ji haka sai suka fusata kwarai da gaske, har suka nemi su kashe manzannin.
Kui nad seda kuulsid, said nad vihaseks ja tahtsid neid hukata.
34 Amma wani Bafarise mai suna Gamaliel, malami ne kuma na attaura wanda dukan jama'a suna martabawa, sai ya mike ya ba da umarni cewa a fid da manzannin waje na dan lokaci.
Aga variser nimega Gamaliel, Seaduse õpetaja, keda kõik inimesed austasid, tõusis Suurkohtus püsti ja käskis mehed hetkeks välja saata.
35 Sai ya ce masu ''Ya ku mutanen Isra'ila, ku lura sosai da a binda kuke niyyar yi wa mutanen nan,
Siis ta pöördus Suurkohtu poole: „Iisraeli mehed, mõelge hästi järele, mida te kavatsete nende meestega teha.
36 A kwanakin baya wani ya zo mai suna Tudas ya dauki kansa wani abu, kimanin mutane dari hudu ne suka bishi, amma da aka kashe shi jama'arsa baki daya sai suka watse, ba wanda ya kara jin labarinsu.
Mõni aeg tagasi ilmus välja Teudas ja väitis enese kellegi olevat ja ligi nelisada inimest järgis teda. Ta tapeti ja kõik tema järgijad aeti laiali ja sellest kõigest ei tulnud midagi.
37 Bayansa kuma, aka yi wani mai suna Yahuza na Galili wanda a kwanakin kidaya, ya zo ya rinjayi mutane da yawa, shima ya lalace, duk wadanda suka bi shi kuwa suka watse.
Pärast teda tõusis rahvaloenduse ajal üles galilealane Juudas ja õhutas inimesi mässama. Ka tema tapeti ja ta järgijad aeti laiali.
38 Don haka ina gaya maku ku rabu da mutanen nan, domin idan shirinsu ko kuma ayyukansu na mutane ne za su lalace.
Seepärast praegusel juhul ma soovitan teile: jätke need mehed rahule! Laske neil minna! Sest kui nende eesmärk või tegevus on inimesest, siis see kukub läbi.
39 Amnma idan abin nan daga Allah yake baza ku iya lalata su ba; kada ya zama kuna gaba da Allah.'' Sai suka rinjayu.
Aga kui see on Jumalast, ei suuda teie neid peatada, vaid teist saavad võitlejad Jumala vastu!“
40 Da suka kira manzannin ciki suka yi masu duka, sai suka umarce su da cewa kada su sake koyarwa a cikin sunan Yesu, sai suka barsu suka tafi.
Tema kõne veenis neid. Nad kutsusid apostlid sisse ja peksid neid. Siis nad keelasid neid rääkida Jeesuse nimel ning lasid neil minna.
41 Suka fita daga cikin majalisar, suna murna domin sun cancanta su sha wulakanci saboda sunan.
Apostlid lahkusid Suurkohtu eest, rõõmustades, et neid oli väärt arvatud kannatama alandust selle Nime pärast.
42 Bayan haka kullayomin suna zuwa haikali, suna bi gida gida, suna wa'azi, suna kuma koyarwa ba fasawa cewa Yesu shine Almasihu.
Ja nad ei lakanud iga päev templis olles ja majast majja käies õpetamast ja kuulutamast evangeeliumi Jeesusest Messiast.