< Ayyukan Manzanni 5 >

1 Sai wani mai suna Hananiya da matarsa Safiratu, suka sayar da filinsu,
There was a man of the name of Ananias who, with his wife Sapphira, sold some property but,
2 Hananiya kuwa ya boye wasu daga cikin kudin filin, (kuma da sanin matarsa), sa'annan suka kawo ragowar kudin a gaban manzannin.
with her full knowledge and consent, dishonestly kept back part of the price which he received for it, though he brought the rest and gave it to the Apostles.
3 Amma Bitrus ya ce, ''Hananiya don me shaidan ya cika zuciyarka, har ka yi wa Ruhu Mai Tsarki karya? Har ka boye wasu daga kudin filin?
"Ananias," said Peter, "why has Satan taken possession of your heart, that you should try to deceive the Holy Spirit and dishonestly keep back part of the price paid you for this land?
4 Sa'adda ba ka sayar da filin ba, ba mallakarka bane? Bayan da ka sayar ma, ba naka bane? Don me kayi irin wannan tunanin a zuciyarka? To ba mutane ka yi wa karya ba, Allah ka yi wa.”
While it remained unsold, was not the land your own? And when sold, was it not at your own disposal? How is it that you have cherished this design in your heart? It is not to men you have told this lie, but to God."
5 Nan take da jin haka, Hananiya ya fadi ya ja numfashinsa na karshe. Dukan mutanen da suka ji labarin kuwa tsoro mai girma ya afko masu
Upon hearing these words Ananias fell down dead, and all who heard the words were awe-struck.
6 Matasa suka zo suka nannade gawarsa, suka fitar da shi waje suka binne shi.
The younger men, however, rose, and wrapping the body up, carried it out and buried it.
7 Bayan wajen sa'a uku, sai matarsa ta iso, ba tare da sanin abin da ya faru ba.
About three hours had passed, when his wife came in, knowing nothing of what had happened.
8 Sai Bitrus ya ce mata, ''ki gaya mini ko nawa kuka sayar da filin?'' Sai ta amsa, ''ta ce kaza ne.”
Peter at once questioned her. "Tell me," he said, "whether you sold the land for so much." "Yes," she replied, "for so much."
9 Sa'annan Bitrus ya ce mata, ''Don me kuka shirya wannan makidar tare da mijinki don ku gwada Ruhun Ubangiji? Kiji tafiyar wadanda suka bizne mijinki a bakin kofa, kuma za su dauke ki yanzu.''
"How was it," replied Peter, "that you two agreed to try an experiment upon the Spirit of the Lord? The men who have buried your husband are already at the door, and they will carry you out."
10 Nan take sai ta fadi a gabansa, ta ja numfashinta na karshe, matasan kuwa suka zo suka same ta ta mutu; sai suka dauki gawarta suka kai waje suka kuma bizne ta kusa da mijinta.
Instantly she fell down dead at his feet, and the young men came in and found her dead. So they carried her out and buried her by her husband's side.
11 Tsoro mai girma kuwa ya afko wa iklisiyar gaba daya da dakan wadanda suka ji wadan nan al'amura.
This incident struck terror into the whole Church, and into the hearts of all who heard of it.
12 Ayyukan alamu da ban mamaki masu yawa kuwa sun faru ga mutane, ta hannun manzannin. Dukansu kuma suna nan tare a dakalin Sulaimanu,
Many signs and marvels continued to be done among the people by the Apostles; and by common consent they all met in Solomon's Portico.
13 Sai dai babu mai karfin halin ya hada kai tare dasu; amma suna da kwarjini sosai a gaban jama'a.
But none of the others dared to attach themselves to them. Yet the people held them in high honour--
14 Har wa yau aka rika samun karin masu ba da gaskiya, dinbin jama'a, maza da mata,
and more and more believers in the Lord joined them, including great numbers both of men and women--
15 har sukan dauki marasa lafiya su kai su bakin titi, suna kwantar da su a bisa gadaje da shinfidu, domin idan Bitrus ya zo wucewa ko da inuwarsa ma ta taba wasunsu.
so that they would even bring out their sick friends into the streets and lay them on light couches or mats, in order that when Peter came by, at least his shadow might fall on one or other of them.
16 Mutane dayawa kuwa sukan zo daga garuruwan da ke kewaye da Urushalima, suna kuma kawo masu rashin lafiya, da wadanda aljannu ke damunsu, aka kuma warkar da su duka.
The inhabitants, too, of the towns in the neighbourhood of Jerusalem came in crowds, bringing sick persons and some who were harassed by foul spirits, and they were cured, one and all.
17 Amma babban firist ya taso tare da duk wadanda ke tare da shi (wato 'yan darikar Sadukiyawa); suka cika da kishi matuka
This roused the High Priest. He and all his party--the sect of the Sadducees--were filled with angry jealousy
18 suka kama manzannin suka kuma jefasu a kurkuku.
and laid hands upon the Apostles, and put them into the public jail.
19 A cikin dare sai mala'ikan Ubangiji ya bude kofofin kurkukun ya kuma fito da su waje, ya ce,
But during the night an angel of the Lord opened the prison doors and brought them out, and said,
20 “Kuje ku tsaya a gaban haikali ku kuma gaya wa mutane maganar wannan rai.”
"Go and stand in the Temple, and go on proclaiming to the people all this Message of Life."
21 Sa'adda suka ji haka, sai suka tafi haikalin da wayewar gari suka yi koyarwa. Amma babban firist da jama'arsa suka zo suka kuma kira taro da kuma dukan yan majalisa, da dattawan jama'ar Isra'ilawa suka fito suka kuma ba da umarni, a fito masu da manzannin.
Having received that command they went into the Temple, just before daybreak, and began to teach: So when the High Priest and his party came, and had called together the Sanhedrin as well as all the Elders of the descendants of Israel, they sent to the jail to fetch the Apostles.
22 Amma ma'aikatan da suka je kurkukun basu sami kowa, a kurkukunba, sai suka dawo suka ba da rahoto,
But the officers went and could not find them in the prison. So they came back and brought word,
23 Su ka ce kurkukun a rufe gam da masu gadi suna nan a tsaye a bakin kofar amma da muka shiga, bamu sami kowa a ciki ba.
saying, "The jail we found quite safely locked, and the warders were on guard at the doors, but upon going in we found no one there."
24 Yanzu sa'adda shugaban haikalin da manyan firistoci suka ji wadannan kalamai, sai suka rikice sosai game da su, suka ce yanzu me wannan zai haifar.
When the Commander of the Temple Guards and the High Priests heard this statement, they were utterly at a loss with regard to it, wondering what would happen next.
25 Sai wani ya zo ya ce masu, ''Wadannan mutanen da kuka jefa a kurkuku suna can a cikin haikali suna koyar da jama'a.''
And some one came and brought them word, saying, "The men you put in prison are actually in the Temple, standing there, teaching the people."
26 Sai shugaban haikalin ya je da ma'aikatansa suka kawosu, ba tare da tashin hankali ba, domin gudun kada jama'a su jejjefesu.
Upon this the Commander went with the officers, and brought the Apostles; but without using violence; for they were afraid of being stoned by the people.
27 Da suka kawo su, sai suka gabatar da su gaban majalisa, babban firist kuwa ya tuhume su,
So they brought them and made them stand in front of the Sanhedrin. And then the High Priest questioned them.
28 cewa ''Ba mun yi maku kashedi da karfi kada ku yi koyarwa cikin wannan sunan ba? Amma ga shi duk kun cika Urushalima da koyarwarku, kuna kuma neman kusa jinin mutumin nan ya sauko kanmu.”
"We strictly forbad you to teach in that name--did we not?" he said. "And see, you have filled Jerusalem with your teaching, and are trying to make us responsible for that man's death!"
29 Amma Bitrus da manzannin suka amsa suka ce, ''Dole mu yi wa Allah biyayya ba mutane ba.
Peter and the other Apostles replied, "We must obey God rather than man.
30 Allah na ubanenmu ya ta da Yesu, wanda kuka kashe, ta wurin rateye shi a bisa itace,
The God of our forefathers has raised Jesus to life, whom you crucified and put to death.
31 Allah kuwa ya daukaka shi a hannun damarsa, domin ya zama sarki da kuma mai ceto, ya ba Isra'ila tuba da gafarar zunubai.
God has exalted Him to His right hand as Chief Leader and as Saviour, to give Israel repentance and forgiveness of sins.
32 Mu kuwa shaidu ne ga wadannan al'amura, haka ma Ruhu Mai Tarki, wanda Allah ya bayar ga dukan wadanda suka yi biyayya a gareshi.''
And we--and the Holy Spirit whom God has given to those who obey Him--are witnesses as to these things."
33 Da yan majalisa suka ji haka sai suka fusata kwarai da gaske, har suka nemi su kashe manzannin.
Infuriated at getting this answer, they were disposed to kill the Apostles.
34 Amma wani Bafarise mai suna Gamaliel, malami ne kuma na attaura wanda dukan jama'a suna martabawa, sai ya mike ya ba da umarni cewa a fid da manzannin waje na dan lokaci.
But a Pharisee of the name of Gamaliel, a teacher of the Law, held in honour by all the people, rose from his seat and requested that they should be sent outside the court for a few minutes.
35 Sai ya ce masu ''Ya ku mutanen Isra'ila, ku lura sosai da a binda kuke niyyar yi wa mutanen nan,
"Israelites," he said, "be careful what you are about to do in dealing with these men.
36 A kwanakin baya wani ya zo mai suna Tudas ya dauki kansa wani abu, kimanin mutane dari hudu ne suka bishi, amma da aka kashe shi jama'arsa baki daya sai suka watse, ba wanda ya kara jin labarinsu.
Years ago Theudas appeared, professing to be a person of importance, and a body of men, some four hundred in number, joined him. He was killed, and all his followers were dispersed and annihilated.
37 Bayansa kuma, aka yi wani mai suna Yahuza na Galili wanda a kwanakin kidaya, ya zo ya rinjayi mutane da yawa, shima ya lalace, duk wadanda suka bi shi kuwa suka watse.
After him, at the time of the Census, came Judas, the Galilaean, and was the leader in a revolt. He too perished, and all his followers were scattered.
38 Don haka ina gaya maku ku rabu da mutanen nan, domin idan shirinsu ko kuma ayyukansu na mutane ne za su lalace.
And now I tell you to hold aloof from these men and leave them alone--for if this scheme or work is of human origin, it will come to nothing.
39 Amnma idan abin nan daga Allah yake baza ku iya lalata su ba; kada ya zama kuna gaba da Allah.'' Sai suka rinjayu.
But if it is really from God, you will be powerless to put them down--lest perhaps you find yourselves to be actually fighting against God."
40 Da suka kira manzannin ciki suka yi masu duka, sai suka umarce su da cewa kada su sake koyarwa a cikin sunan Yesu, sai suka barsu suka tafi.
His advice carried conviction. So they called the Apostles in, and--after flogging them--ordered them not to speak in the name of Jesus, and then let them go.
41 Suka fita daga cikin majalisar, suna murna domin sun cancanta su sha wulakanci saboda sunan.
They, therefore, left the Sanhedrin and went their way, rejoicing that they had been deemed worthy to suffer disgrace on behalf of the NAME.
42 Bayan haka kullayomin suna zuwa haikali, suna bi gida gida, suna wa'azi, suna kuma koyarwa ba fasawa cewa Yesu shine Almasihu.
But they did not desist from teaching every day, in the Temple or in private houses, and telling the Good News about Jesus, the Christ.

< Ayyukan Manzanni 5 >