< Ayyukan Manzanni 5 >

1 Sai wani mai suna Hananiya da matarsa Safiratu, suka sayar da filinsu,
But a certain man named Ananias, with Sapphira his wife, sold a possession,
2 Hananiya kuwa ya boye wasu daga cikin kudin filin, (kuma da sanin matarsa), sa'annan suka kawo ragowar kudin a gaban manzannin.
And kept back [part] of the price, (his wife also being privy [to it] ) and brought a certain part, and laid [it] at the apostles' feet.
3 Amma Bitrus ya ce, ''Hananiya don me shaidan ya cika zuciyarka, har ka yi wa Ruhu Mai Tsarki karya? Har ka boye wasu daga kudin filin?
But Peter said, Ananias, Why hath Satan filled thy heart to lie to the Holy Spirit, and to keep back [part] of the price of the land?
4 Sa'adda ba ka sayar da filin ba, ba mallakarka bane? Bayan da ka sayar ma, ba naka bane? Don me kayi irin wannan tunanin a zuciyarka? To ba mutane ka yi wa karya ba, Allah ka yi wa.”
While it remained, was it not thy own? and after it was sold, was it not in thy own power? why hast thou conceived this thing in thy heart? thou hast not lied to men, but to God.
5 Nan take da jin haka, Hananiya ya fadi ya ja numfashinsa na karshe. Dukan mutanen da suka ji labarin kuwa tsoro mai girma ya afko masu
And Ananias hearing these words, fell down, and expired. And great fear came on all them that heard these things.
6 Matasa suka zo suka nannade gawarsa, suka fitar da shi waje suka binne shi.
And the young men arose, wound him up, and carried [him] out, and buried [him].
7 Bayan wajen sa'a uku, sai matarsa ta iso, ba tare da sanin abin da ya faru ba.
And it was about the space of three hours after, when his wife, not knowing what was done, came in.
8 Sai Bitrus ya ce mata, ''ki gaya mini ko nawa kuka sayar da filin?'' Sai ta amsa, ''ta ce kaza ne.”
And Peter answered to her, Tell me whether ye sold the land for so much? And she said, Yes, for so much.
9 Sa'annan Bitrus ya ce mata, ''Don me kuka shirya wannan makidar tare da mijinki don ku gwada Ruhun Ubangiji? Kiji tafiyar wadanda suka bizne mijinki a bakin kofa, kuma za su dauke ki yanzu.''
Then Peter said to her, How is it that ye have agreed together to tempt the Spirit of the Lord? behold the feet of them who have buried thy husband [are] at the door, and shall carry thee out.
10 Nan take sai ta fadi a gabansa, ta ja numfashinta na karshe, matasan kuwa suka zo suka same ta ta mutu; sai suka dauki gawarta suka kai waje suka kuma bizne ta kusa da mijinta.
Then she fell down immediately at his feet, and expired. And the young men came in, and found her dead, and carrying [her] forth, buried [her] by her husband.
11 Tsoro mai girma kuwa ya afko wa iklisiyar gaba daya da dakan wadanda suka ji wadan nan al'amura.
And great fear came upon all the church, and upon as many as heard these things.
12 Ayyukan alamu da ban mamaki masu yawa kuwa sun faru ga mutane, ta hannun manzannin. Dukansu kuma suna nan tare a dakalin Sulaimanu,
And by the hands of the apostles were many signs and wonders wrought among the people; (and they were all with one accord in Solomon's porch.
13 Sai dai babu mai karfin halin ya hada kai tare dasu; amma suna da kwarjini sosai a gaban jama'a.
And of the rest durst no man join himself to them: but the people magnified them.
14 Har wa yau aka rika samun karin masu ba da gaskiya, dinbin jama'a, maza da mata,
And believers were the more added to the Lord, multitudes both of men and women.)
15 har sukan dauki marasa lafiya su kai su bakin titi, suna kwantar da su a bisa gadaje da shinfidu, domin idan Bitrus ya zo wucewa ko da inuwarsa ma ta taba wasunsu.
So that they brought forth the sick into the streets, and laid [them] on beds and couches, that at the least the shadow of Peter passing by might overshadow some of them.
16 Mutane dayawa kuwa sukan zo daga garuruwan da ke kewaye da Urushalima, suna kuma kawo masu rashin lafiya, da wadanda aljannu ke damunsu, aka kuma warkar da su duka.
There came also a multitude [out] of the cities around to Jerusalem, bringing sick persons, and them who were afflicted with unclean spirits: and they were healed every one.
17 Amma babban firist ya taso tare da duk wadanda ke tare da shi (wato 'yan darikar Sadukiyawa); suka cika da kishi matuka
Then the high priest rose up, and all they that were with him; (which is the sect of the Sadducees) and were filled with indignation,
18 suka kama manzannin suka kuma jefasu a kurkuku.
And laid their hands on the apostles, and put them in the common prison.
19 A cikin dare sai mala'ikan Ubangiji ya bude kofofin kurkukun ya kuma fito da su waje, ya ce,
But the angel of the Lord by night opened the prison-doors, and brought them forth, and said,
20 “Kuje ku tsaya a gaban haikali ku kuma gaya wa mutane maganar wannan rai.”
Go, stand and speak in the temple to the people all the words of this life.
21 Sa'adda suka ji haka, sai suka tafi haikalin da wayewar gari suka yi koyarwa. Amma babban firist da jama'arsa suka zo suka kuma kira taro da kuma dukan yan majalisa, da dattawan jama'ar Isra'ilawa suka fito suka kuma ba da umarni, a fito masu da manzannin.
And when they heard [that], they entered into the temple early in the morning, and taught. But the high priest came, and they that were with him, and called the council together, and all the senate of the children of Israel, and sent to the prison to have them brought.
22 Amma ma'aikatan da suka je kurkukun basu sami kowa, a kurkukunba, sai suka dawo suka ba da rahoto,
But when the officers came, and found them not in the prison, they returned, and told,
23 Su ka ce kurkukun a rufe gam da masu gadi suna nan a tsaye a bakin kofar amma da muka shiga, bamu sami kowa a ciki ba.
Saying, The prison truly we found shut with all safety, and the keepers standing without before the doors: but when we had opened, we found no man within.
24 Yanzu sa'adda shugaban haikalin da manyan firistoci suka ji wadannan kalamai, sai suka rikice sosai game da su, suka ce yanzu me wannan zai haifar.
Now when the high priest, and the captain of the temple, and the chief priests heard these things, they doubted of them to what this would grow.
25 Sai wani ya zo ya ce masu, ''Wadannan mutanen da kuka jefa a kurkuku suna can a cikin haikali suna koyar da jama'a.''
Then came one and told them, saying, Behold, the men whom ye put in prison are standing in the temple, and teaching the people.
26 Sai shugaban haikalin ya je da ma'aikatansa suka kawosu, ba tare da tashin hankali ba, domin gudun kada jama'a su jejjefesu.
Then went the captain with the officers, and brought them without violence: for they feared the people, lest they should have been stoned.
27 Da suka kawo su, sai suka gabatar da su gaban majalisa, babban firist kuwa ya tuhume su,
And when they had brought them, they set [them] before the council: and the high priest asked them,
28 cewa ''Ba mun yi maku kashedi da karfi kada ku yi koyarwa cikin wannan sunan ba? Amma ga shi duk kun cika Urushalima da koyarwarku, kuna kuma neman kusa jinin mutumin nan ya sauko kanmu.”
Saying, Did we not strictly command you, that ye should not teach in this name? and behold, ye have filled Jerusalem with your doctrine, and intend to bring this man's blood upon us.
29 Amma Bitrus da manzannin suka amsa suka ce, ''Dole mu yi wa Allah biyayya ba mutane ba.
Then Peter and the [other] apostles answered and said, We ought to obey God rather than men.
30 Allah na ubanenmu ya ta da Yesu, wanda kuka kashe, ta wurin rateye shi a bisa itace,
The God of our fathers raised up Jesus, whom ye slew and hanged on a tree:
31 Allah kuwa ya daukaka shi a hannun damarsa, domin ya zama sarki da kuma mai ceto, ya ba Isra'ila tuba da gafarar zunubai.
Him hath God exalted with his right hand [to be] a Prince and a Savior, to give repentance to Israel, and forgiveness of sins.
32 Mu kuwa shaidu ne ga wadannan al'amura, haka ma Ruhu Mai Tarki, wanda Allah ya bayar ga dukan wadanda suka yi biyayya a gareshi.''
And we are his witnesses of these things; and [so is] also the Holy Spirit, whom God hath given to them that obey him.
33 Da yan majalisa suka ji haka sai suka fusata kwarai da gaske, har suka nemi su kashe manzannin.
When they heard [that], they were cut [to the heart], and took counsel to slay them.
34 Amma wani Bafarise mai suna Gamaliel, malami ne kuma na attaura wanda dukan jama'a suna martabawa, sai ya mike ya ba da umarni cewa a fid da manzannin waje na dan lokaci.
Then stood up one in the council, a Pharisee, named Gamaliel, a doctor of the law, had in reputation among all the people, and commanded to put the apostles forth a little time.
35 Sai ya ce masu ''Ya ku mutanen Isra'ila, ku lura sosai da a binda kuke niyyar yi wa mutanen nan,
And said to them, Ye men of Israel, take heed to yourselves what ye intend to do concerning these men:
36 A kwanakin baya wani ya zo mai suna Tudas ya dauki kansa wani abu, kimanin mutane dari hudu ne suka bishi, amma da aka kashe shi jama'arsa baki daya sai suka watse, ba wanda ya kara jin labarinsu.
For before these days rose Theudas, boasting himself to be somebody; to whom a number of men, about four hundred, joined themselves: who was slain; and all, as many as obeyed him, were scattered, and brought to naught.
37 Bayansa kuma, aka yi wani mai suna Yahuza na Galili wanda a kwanakin kidaya, ya zo ya rinjayi mutane da yawa, shima ya lalace, duk wadanda suka bi shi kuwa suka watse.
After this man rose Judas of Galilee, in the days of the taxing, and drew away many people after him: he also perished; and all, [even] as many as obeyed him, were dispersed.
38 Don haka ina gaya maku ku rabu da mutanen nan, domin idan shirinsu ko kuma ayyukansu na mutane ne za su lalace.
And now I say to you, Refrain from these men, and let them alone: for if this counsel or this work is from men, it will come to naught:
39 Amnma idan abin nan daga Allah yake baza ku iya lalata su ba; kada ya zama kuna gaba da Allah.'' Sai suka rinjayu.
But if it is from God, ye cannot overthrow it; lest haply ye be found even to fight against God.
40 Da suka kira manzannin ciki suka yi masu duka, sai suka umarce su da cewa kada su sake koyarwa a cikin sunan Yesu, sai suka barsu suka tafi.
And to him they assented: and when they had called the apostles, and beaten [them], they commanded that they should not speak in the name of Jesus, and let them go.
41 Suka fita daga cikin majalisar, suna murna domin sun cancanta su sha wulakanci saboda sunan.
And they departed from the presence of the council, rejoicing that they were counted worthy to suffer shame for his name.
42 Bayan haka kullayomin suna zuwa haikali, suna bi gida gida, suna wa'azi, suna kuma koyarwa ba fasawa cewa Yesu shine Almasihu.
And daily in the temple, and in every house, they ceased not to teach and preach Jesus Christ.

< Ayyukan Manzanni 5 >