< Ayyukan Manzanni 5 >
1 Sai wani mai suna Hananiya da matarsa Safiratu, suka sayar da filinsu,
Now a man named Ananias, along with his wife Sapphira, sold a piece of property
2 Hananiya kuwa ya boye wasu daga cikin kudin filin, (kuma da sanin matarsa), sa'annan suka kawo ragowar kudin a gaban manzannin.
and kept back some of the proceeds, with his wife also being aware of it. He brought a portion of the proceeds and laid it at the apostles' feet.
3 Amma Bitrus ya ce, ''Hananiya don me shaidan ya cika zuciyarka, har ka yi wa Ruhu Mai Tsarki karya? Har ka boye wasu daga kudin filin?
But Peter said, “Ananias, why has Satan filled yoʋr heart to lie to the Holy Spirit and keep back some of the proceeds of the plot of land?
4 Sa'adda ba ka sayar da filin ba, ba mallakarka bane? Bayan da ka sayar ma, ba naka bane? Don me kayi irin wannan tunanin a zuciyarka? To ba mutane ka yi wa karya ba, Allah ka yi wa.”
While it remained unsold, did it not remain yoʋrs? And once it was sold, was it not under yoʋr control? How is it that yoʋ have put this thing in yoʋr heart? Yoʋ have not lied to men but to God.”
5 Nan take da jin haka, Hananiya ya fadi ya ja numfashinsa na karshe. Dukan mutanen da suka ji labarin kuwa tsoro mai girma ya afko masu
When Ananias heard these words, he fell down and breathed his last breath. And great fear came upon all who heard about it.
6 Matasa suka zo suka nannade gawarsa, suka fitar da shi waje suka binne shi.
Then the young men rose, wrapped up his body, carried him out, and buried him.
7 Bayan wajen sa'a uku, sai matarsa ta iso, ba tare da sanin abin da ya faru ba.
About three hours later, his wife came in, not knowing what had happened.
8 Sai Bitrus ya ce mata, ''ki gaya mini ko nawa kuka sayar da filin?'' Sai ta amsa, ''ta ce kaza ne.”
Peter said to her, “Tell me if you sold the plot of land for such and such a price.” She said, “Yes, for such a price.”
9 Sa'annan Bitrus ya ce mata, ''Don me kuka shirya wannan makidar tare da mijinki don ku gwada Ruhun Ubangiji? Kiji tafiyar wadanda suka bizne mijinki a bakin kofa, kuma za su dauke ki yanzu.''
Peter said to her, “Why is it that you have agreed to put the Spirit of the Lord to the test? Behold, the feet of those who buried yoʋr husband are at the door, and they will carry yoʋ out.”
10 Nan take sai ta fadi a gabansa, ta ja numfashinta na karshe, matasan kuwa suka zo suka same ta ta mutu; sai suka dauki gawarta suka kai waje suka kuma bizne ta kusa da mijinta.
At once she fell down at his feet and breathed her last breath. When the young men came in, they found her dead, so they carried her out and buried her beside her husband.
11 Tsoro mai girma kuwa ya afko wa iklisiyar gaba daya da dakan wadanda suka ji wadan nan al'amura.
And great fear came upon the whole church and upon all who heard these things.
12 Ayyukan alamu da ban mamaki masu yawa kuwa sun faru ga mutane, ta hannun manzannin. Dukansu kuma suna nan tare a dakalin Sulaimanu,
Now many signs and wonders were taking place among the people by the hands of the apostles, and all the believers were together with one accord in Solomon's portico.
13 Sai dai babu mai karfin halin ya hada kai tare dasu; amma suna da kwarjini sosai a gaban jama'a.
No one else dared to join them, but the people held them in high regard.
14 Har wa yau aka rika samun karin masu ba da gaskiya, dinbin jama'a, maza da mata,
Yet more and more people believed in the Lord and were added to their number, a multitude of both men and women.
15 har sukan dauki marasa lafiya su kai su bakin titi, suna kwantar da su a bisa gadaje da shinfidu, domin idan Bitrus ya zo wucewa ko da inuwarsa ma ta taba wasunsu.
As a result, people carried the sick out into the streets and laid them on beds and mats, so that when Peter came by at least his shadow might fall on one of them.
16 Mutane dayawa kuwa sukan zo daga garuruwan da ke kewaye da Urushalima, suna kuma kawo masu rashin lafiya, da wadanda aljannu ke damunsu, aka kuma warkar da su duka.
A multitude from the towns all around Jerusalem also gathered together, bringing the sick and those harassed by unclean spirits, and they were all healed.
17 Amma babban firist ya taso tare da duk wadanda ke tare da shi (wato 'yan darikar Sadukiyawa); suka cika da kishi matuka
Then the high priest rose up, along with all who were with him (that is, the sect of the Sadducees), and they were filled with jealousy.
18 suka kama manzannin suka kuma jefasu a kurkuku.
So they arrested the apostles and put them in a public jail.
19 A cikin dare sai mala'ikan Ubangiji ya bude kofofin kurkukun ya kuma fito da su waje, ya ce,
But during the night an angel of the Lord opened the doors of the prison, brought them out, and said,
20 “Kuje ku tsaya a gaban haikali ku kuma gaya wa mutane maganar wannan rai.”
“Go stand in the temple courts and tell the people everything about this new life.”
21 Sa'adda suka ji haka, sai suka tafi haikalin da wayewar gari suka yi koyarwa. Amma babban firist da jama'arsa suka zo suka kuma kira taro da kuma dukan yan majalisa, da dattawan jama'ar Isra'ilawa suka fito suka kuma ba da umarni, a fito masu da manzannin.
When they heard this, they entered the temple courts at dawn and began teaching. When the high priest came, along with those who were with him, they called together the Sanhedrin—that is, the entire eldership of the people of Israel—and sent officers to the prison to have the apostles brought before them.
22 Amma ma'aikatan da suka je kurkukun basu sami kowa, a kurkukunba, sai suka dawo suka ba da rahoto,
But when the officers arrived, they did not find them in the prison. So they returned and reported,
23 Su ka ce kurkukun a rufe gam da masu gadi suna nan a tsaye a bakin kofar amma da muka shiga, bamu sami kowa a ciki ba.
“We found the prison locked up in complete security and the guards standing in front of the doors, but when we opened the doors, we found no one inside.”
24 Yanzu sa'adda shugaban haikalin da manyan firistoci suka ji wadannan kalamai, sai suka rikice sosai game da su, suka ce yanzu me wannan zai haifar.
When the high priest, the captain of the temple guard, and the chief priests heard this report, they were greatly perplexed by it, wondering what might come of this.
25 Sai wani ya zo ya ce masu, ''Wadannan mutanen da kuka jefa a kurkuku suna can a cikin haikali suna koyar da jama'a.''
Then someone came and told them, “Behold, the men you put in prison are standing in the temple courts teaching the people!”
26 Sai shugaban haikalin ya je da ma'aikatansa suka kawosu, ba tare da tashin hankali ba, domin gudun kada jama'a su jejjefesu.
So the captain went with the officers and brought the apostles without the use of force, for they were afraid the people might stone them.
27 Da suka kawo su, sai suka gabatar da su gaban majalisa, babban firist kuwa ya tuhume su,
After bringing the apostles in, they had them stand before the Sanhedrin, and the high priest asked them,
28 cewa ''Ba mun yi maku kashedi da karfi kada ku yi koyarwa cikin wannan sunan ba? Amma ga shi duk kun cika Urushalima da koyarwarku, kuna kuma neman kusa jinin mutumin nan ya sauko kanmu.”
“Did we not strictly command you not to teach in this name? Yet behold, you have filled Jerusalem with your teaching, and you are determined to bring the blood of this man upon us.”
29 Amma Bitrus da manzannin suka amsa suka ce, ''Dole mu yi wa Allah biyayya ba mutane ba.
But Peter and the apostles answered, “We must obey God rather than men.
30 Allah na ubanenmu ya ta da Yesu, wanda kuka kashe, ta wurin rateye shi a bisa itace,
The God of our fathers raised up Jesus, whom you murdered by hanging him on a cross.
31 Allah kuwa ya daukaka shi a hannun damarsa, domin ya zama sarki da kuma mai ceto, ya ba Isra'ila tuba da gafarar zunubai.
God exalted him to his right hand as Leader and Savior to grant repentance to Israel and remission of sins.
32 Mu kuwa shaidu ne ga wadannan al'amura, haka ma Ruhu Mai Tarki, wanda Allah ya bayar ga dukan wadanda suka yi biyayya a gareshi.''
Concerning these things we are his witnesses, and so is the Holy Spirit, whom God has given to those who obey him.”
33 Da yan majalisa suka ji haka sai suka fusata kwarai da gaske, har suka nemi su kashe manzannin.
When they heard this, they were furious and resolved to put them to death,
34 Amma wani Bafarise mai suna Gamaliel, malami ne kuma na attaura wanda dukan jama'a suna martabawa, sai ya mike ya ba da umarni cewa a fid da manzannin waje na dan lokaci.
but a Pharisee named Gamaliel, a teacher of the law who was held in honor by all the people, stood up in the Sanhedrin and gave orders to put the apostles outside for a little while.
35 Sai ya ce masu ''Ya ku mutanen Isra'ila, ku lura sosai da a binda kuke niyyar yi wa mutanen nan,
Then he said to the Sanhedrin, “Men of Israel, give careful consideration to what you are about to do to these men.
36 A kwanakin baya wani ya zo mai suna Tudas ya dauki kansa wani abu, kimanin mutane dari hudu ne suka bishi, amma da aka kashe shi jama'arsa baki daya sai suka watse, ba wanda ya kara jin labarinsu.
For before these days Theudas rose up, declaring himself to be somebody, and a number of men, about four hundred, responded to the call to join him. He was put to death, and all his followers were scattered and came to nothing.
37 Bayansa kuma, aka yi wani mai suna Yahuza na Galili wanda a kwanakin kidaya, ya zo ya rinjayi mutane da yawa, shima ya lalace, duk wadanda suka bi shi kuwa suka watse.
After this man, Judas the Galilean rose up in the days of the census and drew away many people after him. He also perished, and all his followers were scattered.
38 Don haka ina gaya maku ku rabu da mutanen nan, domin idan shirinsu ko kuma ayyukansu na mutane ne za su lalace.
So I say to you now, keep away from these men and leave them alone, for if this plan or this undertaking is of men, it will be stopped;
39 Amnma idan abin nan daga Allah yake baza ku iya lalata su ba; kada ya zama kuna gaba da Allah.'' Sai suka rinjayu.
but if it is of God, you cannot put a stop to it. You will only find yourselves fighting against God.”
40 Da suka kira manzannin ciki suka yi masu duka, sai suka umarce su da cewa kada su sake koyarwa a cikin sunan Yesu, sai suka barsu suka tafi.
They were persuaded by him, and after calling in the apostles, they beat them, commanded them not to speak in the name of Jesus, and released them.
41 Suka fita daga cikin majalisar, suna murna domin sun cancanta su sha wulakanci saboda sunan.
So the apostles went out from the presence of the Sanhedrin, rejoicing that they had been considered worthy to suffer dishonor for the name of Jesus.
42 Bayan haka kullayomin suna zuwa haikali, suna bi gida gida, suna wa'azi, suna kuma koyarwa ba fasawa cewa Yesu shine Almasihu.
And every day, in the temple courts and from house to house, they did not cease teaching and preaching the good news that Jesus is the Christ.