< Ayyukan Manzanni 5 >
1 Sai wani mai suna Hananiya da matarsa Safiratu, suka sayar da filinsu,
But a man named Ananias who, with his wife Sapphira, sold a farm of his,
2 Hananiya kuwa ya boye wasu daga cikin kudin filin, (kuma da sanin matarsa), sa'annan suka kawo ragowar kudin a gaban manzannin.
kept back some of the purchase price, with the connivance of his wife. He brought only a part and laid it at the apostles’ feet.
3 Amma Bitrus ya ce, ''Hananiya don me shaidan ya cika zuciyarka, har ka yi wa Ruhu Mai Tsarki karya? Har ka boye wasu daga kudin filin?
"Ananias," said Peter, "why has Satan so filled your heart that you are lying to the Holy Spirit, and keeping back part of the price of the land?
4 Sa'adda ba ka sayar da filin ba, ba mallakarka bane? Bayan da ka sayar ma, ba naka bane? Don me kayi irin wannan tunanin a zuciyarka? To ba mutane ka yi wa karya ba, Allah ka yi wa.”
"While it remained unsold, was it not your own? And after it was sold, was not the price at your own disposal? How could you conceive this act in your heart? You have not lied unto men, but unto God."
5 Nan take da jin haka, Hananiya ya fadi ya ja numfashinsa na karshe. Dukan mutanen da suka ji labarin kuwa tsoro mai girma ya afko masu
As Ananias heard these words he fell down and expired, and all who heard were awe-struck.
6 Matasa suka zo suka nannade gawarsa, suka fitar da shi waje suka binne shi.
But the younger men rose, wrapped the body up, and carried it out to bury it.
7 Bayan wajen sa'a uku, sai matarsa ta iso, ba tare da sanin abin da ya faru ba.
About three hours later his wife came in, not knowing what had happened;
8 Sai Bitrus ya ce mata, ''ki gaya mini ko nawa kuka sayar da filin?'' Sai ta amsa, ''ta ce kaza ne.”
and Peter said to her, "Tell me if you got so much for the land." "Yes," she said, "so much."
9 Sa'annan Bitrus ya ce mata, ''Don me kuka shirya wannan makidar tare da mijinki don ku gwada Ruhun Ubangiji? Kiji tafiyar wadanda suka bizne mijinki a bakin kofa, kuma za su dauke ki yanzu.''
"Why was it," said Peter, "that you both agreed to tempt the Spirit of the Lord? Lo, the feet of those who buried your husband are at the door, and they shall carry you out."
10 Nan take sai ta fadi a gabansa, ta ja numfashinta na karshe, matasan kuwa suka zo suka same ta ta mutu; sai suka dauki gawarta suka kai waje suka kuma bizne ta kusa da mijinta.
Instantly she fell down at his feet and expired, and when the young men came in they found her dead, and carried her out and buried her husband.
11 Tsoro mai girma kuwa ya afko wa iklisiyar gaba daya da dakan wadanda suka ji wadan nan al'amura.
And great fear fell on all the church and upon all who had heard it.
12 Ayyukan alamu da ban mamaki masu yawa kuwa sun faru ga mutane, ta hannun manzannin. Dukansu kuma suna nan tare a dakalin Sulaimanu,
Many signs and wonders continued to be wrought among the people by the hands of the apostles, and by common consent they all would meet in Solomon’s Porch,
13 Sai dai babu mai karfin halin ya hada kai tare dasu; amma suna da kwarjini sosai a gaban jama'a.
but none of the rest dared to associate with them.
14 Har wa yau aka rika samun karin masu ba da gaskiya, dinbin jama'a, maza da mata,
Yet the people continued to hold them in high honor, and more and more believers in the Lord were joining them, both men and women.
15 har sukan dauki marasa lafiya su kai su bakin titi, suna kwantar da su a bisa gadaje da shinfidu, domin idan Bitrus ya zo wucewa ko da inuwarsa ma ta taba wasunsu.
In consequence people would even bring out their sick into the streets, and place them upon beds and pallets as Peter was passing, that at least his shadow might fall upon some of them.
16 Mutane dayawa kuwa sukan zo daga garuruwan da ke kewaye da Urushalima, suna kuma kawo masu rashin lafiya, da wadanda aljannu ke damunsu, aka kuma warkar da su duka.
The people of the towns near Jerusalem also continued to come in crowds, bringing their sick and those who were harried by unclean spirits, and all of them were healed.
17 Amma babban firist ya taso tare da duk wadanda ke tare da shi (wato 'yan darikar Sadukiyawa); suka cika da kishi matuka
This aroused bitter indignation among the high priest and his followers who were of the sect of the Sadducees,
18 suka kama manzannin suka kuma jefasu a kurkuku.
and they apprehended the apostles, and threw them into the public prison.
19 A cikin dare sai mala'ikan Ubangiji ya bude kofofin kurkukun ya kuma fito da su waje, ya ce,
But an angel of the Lord opened the prison doors during the night, and let them out.
20 “Kuje ku tsaya a gaban haikali ku kuma gaya wa mutane maganar wannan rai.”
He said to them, "Go take your stand in the Temple, and continue to tell the people all the words of this Life."
21 Sa'adda suka ji haka, sai suka tafi haikalin da wayewar gari suka yi koyarwa. Amma babban firist da jama'arsa suka zo suka kuma kira taro da kuma dukan yan majalisa, da dattawan jama'ar Isra'ilawa suka fito suka kuma ba da umarni, a fito masu da manzannin.
When they heard this they went at early dawn to the Temple, and began to teach. Meantime when the high priest and his followers arrived, they summoned the Sanhedrin and all the Council of the Elders of the sons of Israel, and sent to the prison to fetch the apostles.
22 Amma ma'aikatan da suka je kurkukun basu sami kowa, a kurkukunba, sai suka dawo suka ba da rahoto,
But the officers who went did not find them in the prison; so they came back and reported,
23 Su ka ce kurkukun a rufe gam da masu gadi suna nan a tsaye a bakin kofar amma da muka shiga, bamu sami kowa a ciki ba.
"The prison we found locked fast, with the guards stationed at the doors, but when they were opened we found no one inside."
24 Yanzu sa'adda shugaban haikalin da manyan firistoci suka ji wadannan kalamai, sai suka rikice sosai game da su, suka ce yanzu me wannan zai haifar.
When the officer in charge of the Temple and the high priest heard these words, they were perplexed concerning them, wondering what would come of it.
25 Sai wani ya zo ya ce masu, ''Wadannan mutanen da kuka jefa a kurkuku suna can a cikin haikali suna koyar da jama'a.''
And some one came and told them that the very men whom they had put in prison were standing in the Temple, and teaching to the people.
26 Sai shugaban haikalin ya je da ma'aikatansa suka kawosu, ba tare da tashin hankali ba, domin gudun kada jama'a su jejjefesu.
On this the officer went off with his men and fetched them, not, however, by force, for they were afraid that the people would stone them.
27 Da suka kawo su, sai suka gabatar da su gaban majalisa, babban firist kuwa ya tuhume su,
So they brought them, and stood them before the Sanhedrin. Then the high priest questioned them.
28 cewa ''Ba mun yi maku kashedi da karfi kada ku yi koyarwa cikin wannan sunan ba? Amma ga shi duk kun cika Urushalima da koyarwarku, kuna kuma neman kusa jinin mutumin nan ya sauko kanmu.”
"We strictly forbade you, did we not, to teach about this Name, and here you have filled Jerusalem with your teaching, and intend to bring this man’s blood upon us."
29 Amma Bitrus da manzannin suka amsa suka ce, ''Dole mu yi wa Allah biyayya ba mutane ba.
But Peter and the apostles said in reply.
30 Allah na ubanenmu ya ta da Yesu, wanda kuka kashe, ta wurin rateye shi a bisa itace,
"We must obey God rather than man. The God of our fathers has raised up Jesus, whom you slew by hanging him on a tree.
31 Allah kuwa ya daukaka shi a hannun damarsa, domin ya zama sarki da kuma mai ceto, ya ba Isra'ila tuba da gafarar zunubai.
"Him God has exalted at his right hand as Prince and Saviour, to give Israel repentance and forgiveness of sins.
32 Mu kuwa shaidu ne ga wadannan al'amura, haka ma Ruhu Mai Tarki, wanda Allah ya bayar ga dukan wadanda suka yi biyayya a gareshi.''
"And we are witnesses of these things, and so is the Holy Spirit whom God has given to those who obey him."
33 Da yan majalisa suka ji haka sai suka fusata kwarai da gaske, har suka nemi su kashe manzannin.
When they heard this they were infuriated, and were minded to kill the apostles;
34 Amma wani Bafarise mai suna Gamaliel, malami ne kuma na attaura wanda dukan jama'a suna martabawa, sai ya mike ya ba da umarni cewa a fid da manzannin waje na dan lokaci.
but Gamaliel, a Pharisee, a teacher of the law, and held in honor by all the people, rose from his seat, and ordered the apostles to be put outside for a little while.
35 Sai ya ce masu ''Ya ku mutanen Isra'ila, ku lura sosai da a binda kuke niyyar yi wa mutanen nan,
He said. "Men of Israel, take care what you are about to do with these men.
36 A kwanakin baya wani ya zo mai suna Tudas ya dauki kansa wani abu, kimanin mutane dari hudu ne suka bishi, amma da aka kashe shi jama'arsa baki daya sai suka watse, ba wanda ya kara jin labarinsu.
"Years ago Theudas arose, claiming to be somebody, and was joined by about four hundred men. He was killed, and all of his followers dispersed and annihilated.
37 Bayansa kuma, aka yi wani mai suna Yahuza na Galili wanda a kwanakin kidaya, ya zo ya rinjayi mutane da yawa, shima ya lalace, duk wadanda suka bi shi kuwa suka watse.
"After him Judas of Galilee rose up in the days of the enrollment, and drew away some of the people after him. He also perished, and all his followers were scattered.
38 Don haka ina gaya maku ku rabu da mutanen nan, domin idan shirinsu ko kuma ayyukansu na mutane ne za su lalace.
"And now, I say to you, hold aloof from these men. Let them alone; for if this scheme or work be of human origin it will come to nothing;
39 Amnma idan abin nan daga Allah yake baza ku iya lalata su ba; kada ya zama kuna gaba da Allah.'' Sai suka rinjayu.
"but if it is from God, you cannot put it down; you may even find yourselves fighting against God."
40 Da suka kira manzannin ciki suka yi masu duka, sai suka umarce su da cewa kada su sake koyarwa a cikin sunan Yesu, sai suka barsu suka tafi.
They gave in to him; and called the apostles in, and after flogging them, released them, with instructions not to speak about the name of Jesus.
41 Suka fita daga cikin majalisar, suna murna domin sun cancanta su sha wulakanci saboda sunan.
So they left Sanhedrin, rejoicing that they had been deemed worthy to suffer disgrace for the sake of the Name;
42 Bayan haka kullayomin suna zuwa haikali, suna bi gida gida, suna wa'azi, suna kuma koyarwa ba fasawa cewa Yesu shine Almasihu.
but not for a single day did they desist from teaching and preaching in the Temple, and in private houses, the Gospel of Jesus, the Messiah.