< Ayyukan Manzanni 5 >
1 Sai wani mai suna Hananiya da matarsa Safiratu, suka sayar da filinsu,
Men en Mand, ved Navn Ananias, tillige med Safira, hans Hustru, solgte en Ejendom
2 Hananiya kuwa ya boye wasu daga cikin kudin filin, (kuma da sanin matarsa), sa'annan suka kawo ragowar kudin a gaban manzannin.
og stak med sin Hustrus Vidende noget af Værdien til Side og bragte en Del deraf og lagde den for Apostlenes Fødder.
3 Amma Bitrus ya ce, ''Hananiya don me shaidan ya cika zuciyarka, har ka yi wa Ruhu Mai Tsarki karya? Har ka boye wasu daga kudin filin?
Men Peter sagde: "Ananias! hvorfor har Satan fyldt dit Hjerte, så du har løjet imod den Helligånd og stukket noget til Side af Summen for Jordstykket?
4 Sa'adda ba ka sayar da filin ba, ba mallakarka bane? Bayan da ka sayar ma, ba naka bane? Don me kayi irin wannan tunanin a zuciyarka? To ba mutane ka yi wa karya ba, Allah ka yi wa.”
Var det ikke dit, så længe du ejede det, og stod ikke det, som det blev solgt for, til din Rådighed? Hvorfor har du dog sat dig denne Gerning for i dit Hjerte? Du har ikke løjet for Mennesker, men for Gud."
5 Nan take da jin haka, Hananiya ya fadi ya ja numfashinsa na karshe. Dukan mutanen da suka ji labarin kuwa tsoro mai girma ya afko masu
Men da Ananias hørte disse Ord, faldt han om og udåndede. Og der kom stor Frygt over alle, som hørte det.
6 Matasa suka zo suka nannade gawarsa, suka fitar da shi waje suka binne shi.
Men de unge Mænd stode op og lagde ham til Rette og bare ham ud og begravede ham.
7 Bayan wajen sa'a uku, sai matarsa ta iso, ba tare da sanin abin da ya faru ba.
Men det skete omtrent tre Timer derefter, da kom hans Hustru ind uden at vide, hvad der var sket.
8 Sai Bitrus ya ce mata, ''ki gaya mini ko nawa kuka sayar da filin?'' Sai ta amsa, ''ta ce kaza ne.”
Da sagde Peter til hende: "Sig mig, om I solgte Jordstykket til den Pris?" Og hun sagde: "Ja, til den Pris."
9 Sa'annan Bitrus ya ce mata, ''Don me kuka shirya wannan makidar tare da mijinki don ku gwada Ruhun Ubangiji? Kiji tafiyar wadanda suka bizne mijinki a bakin kofa, kuma za su dauke ki yanzu.''
Men Peter sagde til hende: "Hvorfor ere I dog blevne enige om at friste Herrens Ånd? Se, deres Fødder, som have begravet din Mand, ere for Døren, og de skulle bære dig ud."
10 Nan take sai ta fadi a gabansa, ta ja numfashinta na karshe, matasan kuwa suka zo suka same ta ta mutu; sai suka dauki gawarta suka kai waje suka kuma bizne ta kusa da mijinta.
Men hun faldt straks om for hans Fødder og udåndede. Men da de unge Mænd kom ind, fandt de hende død, og de bare hende ud og begravede hende hos hendes Mand.
11 Tsoro mai girma kuwa ya afko wa iklisiyar gaba daya da dakan wadanda suka ji wadan nan al'amura.
Og stor Frygt kom over hele Menigheden og over alle, som hørte dette.
12 Ayyukan alamu da ban mamaki masu yawa kuwa sun faru ga mutane, ta hannun manzannin. Dukansu kuma suna nan tare a dakalin Sulaimanu,
Men ved Apostlenes Hænder skete der mange Tegn og Undere iblandt Folket; og de vare alle endrægtigt sammen i Salomons Søjlegang.
13 Sai dai babu mai karfin halin ya hada kai tare dasu; amma suna da kwarjini sosai a gaban jama'a.
Men af de andre turde ingen holde sig til dem; dog priste Folket dem højt,
14 Har wa yau aka rika samun karin masu ba da gaskiya, dinbin jama'a, maza da mata,
og der føjedes stedse flere troende til Herren, Skarer både af Mænd og Kvinder,
15 har sukan dauki marasa lafiya su kai su bakin titi, suna kwantar da su a bisa gadaje da shinfidu, domin idan Bitrus ya zo wucewa ko da inuwarsa ma ta taba wasunsu.
så at de endogså bare de syge ud på Gaderne og lagde dem på Senge og Løjbænke, for at når Peter kom, endog blot hans Skygge kunde overskygge nogen af dem.
16 Mutane dayawa kuwa sukan zo daga garuruwan da ke kewaye da Urushalima, suna kuma kawo masu rashin lafiya, da wadanda aljannu ke damunsu, aka kuma warkar da su duka.
Ja, selv fra Byerne i Jerusalems Omegn strømmede Mængden sammen og bragte syge og sådanne, som vare plagede af urene Ånder, og de bleve alle helbredte.
17 Amma babban firist ya taso tare da duk wadanda ke tare da shi (wato 'yan darikar Sadukiyawa); suka cika da kishi matuka
Men Ypperstepræsten stod op samt alle de, som holdt med ham, nemlig Saddukæernes Parti, og de bleve fulde af Nidkærhed.
18 suka kama manzannin suka kuma jefasu a kurkuku.
Og de lagde Hånd på Apostlene og satte dem i offentlig Forvaring.
19 A cikin dare sai mala'ikan Ubangiji ya bude kofofin kurkukun ya kuma fito da su waje, ya ce,
Men en Herrens Engel åbnede Fængselets Døre om Natten og førte dem ud og sagde:
20 “Kuje ku tsaya a gaban haikali ku kuma gaya wa mutane maganar wannan rai.”
"Går hen og træder frem og taler i Helligdommen alle disse Livets Ord for Folket!"
21 Sa'adda suka ji haka, sai suka tafi haikalin da wayewar gari suka yi koyarwa. Amma babban firist da jama'arsa suka zo suka kuma kira taro da kuma dukan yan majalisa, da dattawan jama'ar Isra'ilawa suka fito suka kuma ba da umarni, a fito masu da manzannin.
Men da de havde hørt dette, gik de ved Daggry ind i Helligdommen og lærte. Men Ypperstepræsten og de, som holdt med ham, kom og sammenkaldte Rådet og alle Israels Børns Ældste og sendte Bud til Fængselet, at de skulde føres frem.
22 Amma ma'aikatan da suka je kurkukun basu sami kowa, a kurkukunba, sai suka dawo suka ba da rahoto,
Men da Tjenerne kom derhen, fandt de dem ikke i Fængselet; og de kom tilbage og meldte det og sagde:
23 Su ka ce kurkukun a rufe gam da masu gadi suna nan a tsaye a bakin kofar amma da muka shiga, bamu sami kowa a ciki ba.
"Fængselet fandt vi tillukket helt forsvarligt, og Vogterne stående ved Dørene; men da vi lukkede op, fandt vi ingen derinde."
24 Yanzu sa'adda shugaban haikalin da manyan firistoci suka ji wadannan kalamai, sai suka rikice sosai game da su, suka ce yanzu me wannan zai haifar.
Men da Høvedsmanden for Helligdommen og Ypperstepræsterne hørte disse Ord, bleve de tvivlrådige om dem, hvad dette skulde blive til.
25 Sai wani ya zo ya ce masu, ''Wadannan mutanen da kuka jefa a kurkuku suna can a cikin haikali suna koyar da jama'a.''
Men der kom en og meldte dem: "Se, de Mænd, som I satte i Fængselet, stå i Helligdommen og lære Folket."
26 Sai shugaban haikalin ya je da ma'aikatansa suka kawosu, ba tare da tashin hankali ba, domin gudun kada jama'a su jejjefesu.
Da gik Høvedsmanden hen med Tjenerne og hentede dem, dog ikke med Magt; thi de frygtede for Folket, at de skulde blive stenede.
27 Da suka kawo su, sai suka gabatar da su gaban majalisa, babban firist kuwa ya tuhume su,
Men da de havde hentet dem, stillede de dem for Rådet; og Ypperstepræsten spurgte dem og sagde:
28 cewa ''Ba mun yi maku kashedi da karfi kada ku yi koyarwa cikin wannan sunan ba? Amma ga shi duk kun cika Urushalima da koyarwarku, kuna kuma neman kusa jinin mutumin nan ya sauko kanmu.”
"Vi bøde eder alvorligt, at I ikke måtte lære i dette Navn, og se, I have fyldt Jerusalem med eders Lære, og I ville bringe dette Menneskes Blod over os!"
29 Amma Bitrus da manzannin suka amsa suka ce, ''Dole mu yi wa Allah biyayya ba mutane ba.
Men Peter og Apostlene svarede og sagde: "Man bør adlyde Gud mere end Mennesker.
30 Allah na ubanenmu ya ta da Yesu, wanda kuka kashe, ta wurin rateye shi a bisa itace,
Vore Fædres Gud oprejste Jesus, hvem I hængte på et Træ og sloge ihjel.
31 Allah kuwa ya daukaka shi a hannun damarsa, domin ya zama sarki da kuma mai ceto, ya ba Isra'ila tuba da gafarar zunubai.
Ham har Gud ved sin højre Hånd ophøjet til en Fyrste og Frelser for at give Israel Omvendelse og Syndernes Forladelse.
32 Mu kuwa shaidu ne ga wadannan al'amura, haka ma Ruhu Mai Tarki, wanda Allah ya bayar ga dukan wadanda suka yi biyayya a gareshi.''
Og vi ere hans Vidner om disse Ting, ligesom også den Helligånd, som Gud har givet dem, der adlyde ham."
33 Da yan majalisa suka ji haka sai suka fusata kwarai da gaske, har suka nemi su kashe manzannin.
Men da de hørte dette, skar det dem i Hjertet, og de rådsloge om at slå dem ihjel.
34 Amma wani Bafarise mai suna Gamaliel, malami ne kuma na attaura wanda dukan jama'a suna martabawa, sai ya mike ya ba da umarni cewa a fid da manzannin waje na dan lokaci.
Men der rejste sig i Rådet en Farisæer ved Navn Gamaliel, en Lovlærer, højt agtet af hele Folket, og han bød, at de skulde lade Mændene træde lidt udenfor.
35 Sai ya ce masu ''Ya ku mutanen Isra'ila, ku lura sosai da a binda kuke niyyar yi wa mutanen nan,
Og han sagde til dem: "I israelitiske Mænd! ser eder vel for, hvad I gøre med disse Mennesker.
36 A kwanakin baya wani ya zo mai suna Tudas ya dauki kansa wani abu, kimanin mutane dari hudu ne suka bishi, amma da aka kashe shi jama'arsa baki daya sai suka watse, ba wanda ya kara jin labarinsu.
Thi for nogen Tid siden fremstod Theudas, som udgav sig selv for at være noget, og et Antal af omtrent fire Hundrede Mænd sluttede sig til ham; han blev slået ihjel, og alle de, som adløde ham, adsplittedes og bleve til intet.
37 Bayansa kuma, aka yi wani mai suna Yahuza na Galili wanda a kwanakin kidaya, ya zo ya rinjayi mutane da yawa, shima ya lalace, duk wadanda suka bi shi kuwa suka watse.
Efter ham fremstod Judas Galilæeren i Skatteindskrivningens Dage og fik en Flok Mennesker til at følge sig. Også han omkom, og alle de, som adløde ham, bleve adspredte.
38 Don haka ina gaya maku ku rabu da mutanen nan, domin idan shirinsu ko kuma ayyukansu na mutane ne za su lalace.
Og nu siger jeg eder: Holder eder fra disse Mennesker, og lader dem fare; thi dersom dette Råd eller dette Værk er af Mennesker, bliver det til intet;
39 Amnma idan abin nan daga Allah yake baza ku iya lalata su ba; kada ya zama kuna gaba da Allah.'' Sai suka rinjayu.
men er det af Gud, kunne I ikke gøre dem til intet. Lader eder dog ikke findes som de, der endog ville stride mod Gud!"
40 Da suka kira manzannin ciki suka yi masu duka, sai suka umarce su da cewa kada su sake koyarwa a cikin sunan Yesu, sai suka barsu suka tafi.
Og de adløde ham; og de kaldte Apostlene frem og lode dem piske og forbøde dem at tale i Jesu Navn og løslode dem.
41 Suka fita daga cikin majalisar, suna murna domin sun cancanta su sha wulakanci saboda sunan.
Så gik de da glade bort fra Rådets Åsyn, fordi de vare blevne agtede værdige til at vanæres for hans Navns Skyld.
42 Bayan haka kullayomin suna zuwa haikali, suna bi gida gida, suna wa'azi, suna kuma koyarwa ba fasawa cewa Yesu shine Almasihu.
Og de holdt ikke op med hver Dag at lære i Helligdommen og i Husene og at forkynde Evangeliet om Kristus Jesus.