< Ayyukan Manzanni 3 >

1 Sa'adda Bitrus da Yahaya suna hanya zuwa haikali a lokacin addu'ar karfe uku.
Men Peter og Johannes gik op i Helligdommen ved Bedetimen, den niende Time.
2 Wani mutum, gurgu ne tun daga haihuwa, ana daukar sa kulluyomi zuwa kofar haikali da ake kira Kyakkyawa, domin bara gun mutanen da ke shiga haikalin.
Og en Mand, som var lam fra Moders Liv af, blev baaren frem; ham satte de daglig ved den Dør til Helligdommen, som kaldtes den skønne, for at han kunde bede dem, som gik ind i Helligdommen, om Almisse.
3 Da ya ga Bitrus da Yahaya suna shiga haikalin, sai ya roke su sadaka.
Da han saa Peter og Johannes, idet de vilde gaa ind i Helligdommen, bad han om at faa en Almisse.
4 Bitrus da Yahaya kuwa suka zuba masa ido, Bitrus ya ce, ''Ka dube mu.''
Da saa Peter tillige med Johannes fast paa ham og sagde: „Se paa os!”
5 Gurgun nan kuwa ya dube su, yana tsammanin zai sami wani abu a wurin su.
Og han gav Agt paa dem, efterdi han ventede at faa noget af dem.
6 Amma Bitrus ya ce, “Azurfa da Zinariya ba ni da su, amma abin da nake da shi, zan baka. A cikin sunan Yesu Almasihu Banazare, Yi tafiya''
Men Peter sagde: „Sølv og Guld ejer jeg ikke, men hvad jeg har, det giver jeg dig: I Jesu Kristi Nazaræerens Navn staa op og gaa!”
7 Bitrus ya kama hannun damarsa, ya daga shi; nan da nan kafafunsa da kashin idon sawayensa suka samu karfi.
Og han greb ham ved den højre Haand og rejste ham op.
8 Da gurgun ya yunkura, ya mike tsaye sai ya fara takawa; ya shiga haikali tare da Bitrus da Yahaya, yana takawa, yana tsalle, yana kuma girmama Allah.
Men straks bleve hans Ben og Ankler stærke, og han sprang op og stod og gik omkring og gik med dem ind i Helligdommen, hvor han gik omkring og sprang og lovede Gud.
9 Dukan mutane suka gan shi yana tafiya yana kuma yabon Allah.
Og hele Folket saa ham gaa omkring og love Gud.
10 Sun lura cewa, shine mutumin da ke zama yana bara a Kyakyawar kofar haikali; sai suka cika da mamaki domin abin da ya faru.
Og de kendte ham som den, der havde siddet ved den skønne Port til Helligdommen for at faa Almisse; og de bleve fulde af Rædsel og Forfærdelse over det, som var timedes ham.
11 Yayin da yake rike da Bitrus da Yahaya, dukan jama'a suka matso wurinsu, a gefen dakalin Sulaimanu, suna ta mamaki kwarai.
Medens han nu holdt fast ved Peter og Johannes, løb alt Folket rædselsslaget sammen om dem i den Søjlegang, som kaldes Salomons.
12 Da Bitrus ya ga haka ya amsa wa jama'ar, “Ya ku mutanen Isra'ila, don me ku ke mamaki?” Don me ku ka zura mana ido, kamar mu ne muka sa shi ya yi tafiya da ikon kanmu ko adalcin mu?
Men da Peter saa det, talte han til Folket: „I israelitiske Mænd! Hvorfor undre I eder over dette? eller hvorfor stirre I paa os, som om vi af egen Magt eller Gudfrygtighed havde gjort, at han kan gaa?
13 Allah na Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, Allah na iyayenmu ya girmama bawansa Yesu. Shi kuka ki kun kuma bashe shi a gaban Bilatus da ya so ya sake shi.
Abrahams og Isaks og Jakobs Gud, vore Fædres Gud, har herliggjort sin Tjener Jesus, hvem I prisgave og fornægtede for Pilatus, da han dømte, at han skulde løslades.
14 Kuka ki Mai Tsarkin nan, Mai Adalcin, maimakon haka kuka ce a sakkar maku mai kisan kai.
Men I fornægtede den hellige og retfærdige og bade om, at en Morder maatte skænkes eder.
15 Kun kashe mai ba da rai, wanda Allah ya tayar daga matattu, mu kuwa shaidu ne ga wannan al'amari.
Men Livets Fyrste sloge I ihjel, hvem Gud oprejste fra de døde, hvorom vi ere Vidner.
16 Yanzu, ta bangaskiya ga sunansa - wannan mutum da kuke gani kuma kun san shi - ta wurin wannan sunan ne ya sami karfi. Bangaskiya cikin Yesu ta ba shi cikakkiyar lafiya, a gabanku duka.
Og i Troen paa hans Navn har hans Navn styrket denne, hvem I se og kende, og Troen, som virkedes ved ham, har givet denne hans Førlighed i Paasyn af eder alle.
17 Ya ku 'yan'uwa, na san kun yi haka ne cikin rashin sani, yadda shugabaninku suka yi.
Og nu, Brødre! jeg ved, at I handlede i Uvidenhed, ligesom ogsaa eders Raadsherrer.
18 Amma duk abubuwan da Allah ya fada ta bakin dukan anabawansa, cewa Almasihunsa zai sha wahala, yanzu ya cika.
Men Gud har saaledes fuldbyrdet, hvad han forud forkyndte ved alle Profeternes Mund, at hans Salvede skulde lide.
19 Saboda haka, Ku tuba, ku juyo, domin a shafe zunubanku, domin lokacin sabuntuwa daga wurin Ubangiji ya zo;
Derfor fatter et andet Sind og vender om, for at eders Synder maa blive udslettede, for at Vederkvægelsens Tider maa komme fra Herrens Aasyn,
20 domin a aiko maku da Almasihu wanda aka kaddara wato, Yesu.
og han maa sende den for eder bestemte Kristus, Jesus,
21 Shine wanda dole sama ta karbe shi har zuwa lokacin komo da dukan abubuwa, game da abubuwan da Allah ya fada tun da ta bakin annabawansa tsarkaka. (aiōn g165)
hvem Himmelen skal modtage indtil alle Tings Genoprettelses Tider, hvorom Gud har talt ved sine hellige Profeters Mund fra de ældste Dage. (aiōn g165)
22 Musa hakika ya ce, 'Ubangiji Allah zai tayar maku da wani annabi kamar ni daga cikin, 'yan'uwanku. Za ku saurari dukan abin da zai fada maku.
Moses sagde: „En Profet skal Herren eders Gud oprejse eder af eders Brødre ligesom mig; ham skulle I høre i alt, hvad han end vil tale til eder.
23 Zai kasance kowanne mutum da bai saurari annabin nan ba za a kau da shi gabadaya daga cikin mutanensa.'
Men det skal ske, hver Sjæl, som ikke hører den Profet, skal udryddes af Folket.”
24 I, dukan annabawa tun daga Sama'ila da wadanda suka zo bayansa, sun yi magana sun ambaci wadannan kwanaki.
Men ogsaa alle Profeterne, fra Samuel af og derefter, saa mange som talte, have ogsaa forkyndt disse Dage.
25 Kune 'ya'yan annabawa da na alkawari wanda Allah ya yi da kakanninku, yadda ya ce wa Ibrahim, 'Daga zuriyarka dukan al'uman duniya za su sami albarka.'
I ere Profeternes Sønner og Sønner af den Pagt, som Gud sluttede med vore Fædre, da han sagde til Abraham: „Og i din Sæd skulle alle Jordens Slægter velsignes.”
26 Bayan da Allah ya ta da bawansa, a gareku ne ya fara aiko shi, domin ya albarkace ku tawurin juyadda kowannenku daga muguntarsa.”
For eder først har Gud oprejst sin Tjener og sendt ham for at velsigne eder, naar enhver af eder vender om fra sin Ondskab.”

< Ayyukan Manzanni 3 >