< Ayyukan Manzanni 26 >

1 Sai Agaribas ya ce wa Bulus, “Za ka iya kare kan ka.” Sai Bulus ya daga hannunsa ya fara kare kansa.
Potom Agrippa řekl Pavlovi: Dopouštíť se, abys sám za sebe promluvil. Tedy Pavel vztáh ruku, mluvil:
2 “Ina farinciki, ya sarki Agaribas, game da saran da Yahudawa ke kawowa a kaina yau;
Na všecky ty věci, z kterýchž mne viní Židé, králi Agrippo, za šťastného se počítám, že dnes před tebou odpovídati mám,
3 musamman ma don kai masani ne game da al'adun Yahudawa da al'amuransu. Don haka, ina rokanka ka yi hakuri ka saurare ni.
A zvláště proto, poněvadž jsi ty povědom všech těch, kteříž u Židů jsou, obyčejů a otázek. Protož prosím tebe, vyslyšiž mne trpělivě.
4 Hakika, dukan Yahudawa sun san yadda na yi rayuwa ta daga kurciyata a kasa ta, da kuma Urushalima.
O životu mém hned od mladosti mé, jaký byl od počátku v národu mém v Jeruzalémě, vědí všickni Židé,
5 Sun san ni tun farko, kuma yakamata su yarda cewa na yi rayuwa kamar Bafarase, darikan nan mai tsatsauran ra'ayi ta addininmu.
Měvše mne prve zdávna v dobré známosti, (kdyby chtěli svědectví vydati, ) kterak vedle nejjistší sekty v našem náboženství byl jsem živ farizeus.
6 Yanzu ina tsaye a nan dominn a shari'anta ni, saboda alkawalin da Allah ya yi wa ubanninmu.
A nyní pro naději toho zaslíbení, kteréž se stalo otcům našim od Boha, teď stojím, soudu jsa poddán,
7 Domin wannan shine alkawalin da kabilunmu goma sha biyu suka sa zuciya su karba, yayin da suke yin sujada da himma ga Allah dare da rana. Saboda wanan bege, Sarki Agaribas, Yahudawa ke tuhuma ta.
K kterémužto zaslíbení dvanáctero pokolení naše, sloužíce Bohu ustavičně dnem i nocí, naději má, že přijde; pro kteroužto naději žalují na mne Židé, ó králi Agrippo.
8 Me ya sa wani zai yi tunani cewa abin mamaki ne Allah ya ta da mattatu?
A tak-liž se to od vás za nepodobné k víře soudí, že Bůh křísí mrtvé?
9 Da, na yi tunanin yin abubuwa gaba da sunan Yesu Banazarat.
Ačť i mně se zdálo, že by mi náležité bylo, proti jménu Ježíše Nazaretského mnoho odporného činiti,
10 Na yi wadanan a Urshalima. Na kulle masu bi da yawa a kurkuku, sanadiyar iko da na samu daga wurin manyan firistoci, kuma da ake kashe su ma, ina ba da goyon baya.
Jakož jsem i činil v Jeruzalémě, a mnohé z svatých já jsem do žalářů dával, vzav moc od předních kněží. A když měli mordováni býti, já jsem pomáhal ortele vynášeti.
11 Na wahalshe su sau dayawa a cikin dukan majamiu ina kuma yin kokari in tilasta masu su yi sabo. Na yi gaba mai zafi da su kuma na tsananta masu har zuwa birane na wadansu kasashe.
A po všech školách často trápě je, přinucoval jsem, aby se rouhali; a náramně rozlítiv se na ně, protivil jsem se jim, až i do jiných měst na to jsem jezdil.
12 A sa'anda nake yin wannan, na tafi Dimashku da izinin manyan firistoci;
A v tom, když jsem šel do Damašku, s mocí a s poručením předních kněží,
13 a cikin tafiyata kuma, da tsakar rana, ya sarki, na ga haske daga sama da ya fi rana sheki, ya haskaka kewaye da ni da kuma wadanda ke tafiya tare da ni.
O poledni na cestě, ó králi, uzřel jsem, ano světlo s nebe, jasnější nad blesk slunečný, obklíčilo mne, i ty, kteříž se mnou šli.
14 Da dukanmu muka fadi kasa, na ji wata murya na magana da ni a harshen Ibraniyawa tana cewa, 'Shawulu, Shawulu, don me kake tsananta mani? Yana da wuya ka hauri abin da ke mai tsini.'
A když jsme my všickni na zem padli, slyšel jsem hlas mluvící ke mně a řkoucí Židovským jazykem: Saule, Saule, proč mi se protivíš? Tvrdoť jest tobě proti ostnům se zpěčovati.
15 Sai na ce, 'Wanene kai ya Ubangiji?' Ubangiji ya amsa, 'Ni ne Yesu wanda kake tsanantawa.
A já řekl: I kdo jsi, Pane? A on řekl: Já jsem Ježíš, kterémuž ty se protivíš.
16 Yanzu ka tashi tsaye domin saboda wannan dalili ne na bayyana gare ka in sanya ka, ka zama bawa da mashaidi na game da abubuwan da ka sani a kaina yanzu da wadanda zan bayyana maka daga bisani;
Ale vstaň a stůj na nohách svých; nebo protoť jsem se tobě ukázal, ať bych tebe učinil služebníkem a svědkem i těch věcí, kteréž jsi viděl, i těch, v kterýchžto ukazovati se budu tobě,
17 Zan kubutar da kai daga wurin mutane da kuma al'ummai da zan aike ka wurinsu,
Vysvobozuje tebe z lidu tohoto, i z pohanů, k nimž tě nyní posílám,
18 domin ka bude idanunsu ka juyo su daga duhu zuwa haske da daga ikon Shaidan zuwa ga Allah, domin su karbi gafarar zunubai da gado da zan ba wadanda na kebe wa kaina ta wurin bangaskiya gare ni.'
Otvírati oči jejich, aby se obrátili od temností k světlu a z moci ďábelské k Bohu, aby tak hříchů odpuštění a díl s posvěcenými vzali skrze víru, kteráž jest ve mne.
19 Saboda haka, sarki Agaribas, ban yi rashin biyayya da wahayin da na gani daga sama ba;
A protož, ó králi Agrippo, nebyl jsem nevěřící nebeskému vidění.
20 amma, da farko ga wadanda ke a Dimashku, sa'annan a Urushalima da kasar Yahudiya gaba daya, da dukan Al'ummai, na yi wa'azi domin su tuba su kuma juyo ga Allah, su yi ayyukan da suka chanchanci tuba.
Ale hned nejprv těm, kteříž jsou v Damašku a v Jeruzalémě, i po vší krajině Judské, potom i pohanům zvěstoval jsem evangelium, aby pokání činili a obrátili se k Bohu, skutky hodné pokání činíce.
21 Domin wannan dalili ne Yahudawa suka kama ni a cikin haikali kuma suke kokari su kashe ni.
A pro tu příčinu Židé javše mne v chrámě, pokoušeli se rukama svýma zamordovati.
22 Allah ya taimake ni har wa yau, domin in iya tsayawa gaban mutane kanana da manya, in bada shaida game da iyakar abin da annabawa da Musa suka fada zai faru;
Ale s pomocí Boží ještě až do dnešního dne stojím, vydávaje svědectví i malému i velikému, nic jiného nevypravuje, než to, což jsou Proroci a Mojžíš zvěstovali, že se mělo státi:
23 wato lallai Almasihu zai sha wahala, ya kuma zama na farko da za'a rayar daga matattu ya kuma yi shelar haske zuwa ga mutanen Yahudawa da Al'ummai.”
Totiž, že měl Kristus trpěti, a z mrtvých vstana první, zvěstovati světlo lidu tomuto i pohanům.
24 Da Bulus ya gama kare kansa, Festas ya yi magana da babban murya, “Bulus, kana hauka; yawan iliminka yasa ka hauka.”
To když od sebe promluvil Pavel, Festus hlasem velikým řekl: Blázníš, Pavle. Mnohé tvé umění k bláznovství tebe přivodí.
25 Amma Bulus ya ce, “Ba na hauka, ya mai girma Festas; amma da karfin zuciya nake fadi kalmomin gaskiya da na natsuwa.
On pak řekl: Nebláznímť, výborný Feste, ale slova pravdy a středmosti mluvím.
26 Saboda sarkin ya san wadannan abubuwa duka; shi ya sa nake magana gabagadi, don na hakikance cewa, ba abin da ke a boye gare shi; gama ba a yi wadannan abubuwa a boye ba.
Víť zajisté o těch věcech král, před kterýmž směle a svobodně mluvím; nebo mám za to, žeť ho nic z těchto věcí tajno není, poněvadž se toto nedálo pokoutně.
27 Ko ka gaskanta da annabawa, Sarki Agaribas? Na sani ka gaskanta.”
Věříš-li, králi Agrippo, Prorokům? Vím, že věříš.
28 Agaribas ya ce wa Bulus, “A cikin karamin lokaci kana so ka rinjaye ni ka mai da ni Krista?”
Tedy Agrippa řekl Pavlovi: Téměř bys mne k tomu naklonil, abych byl křesťanem.
29 Bulus ya ce, “Ina roko ga Allah, domin ko a karamin lokaci ko a dogon lokaci, ba kai kadai ba, amma har da wadanda ke sauraro na yau su zama kamar ni, amma ban da wadannan sarkokin.”
A Pavel řekl: Žádalť bych od Boha, abyste i poněkud i z cela, netoliko ty, ale všickni, kteříž slyší mne dnes, byli takoví, jakýž já jsem, kromě okovů těchto.
30 Sai sarki ya tashi tsaye tare da gwamna da Barniki da dukan wadanda ke zaune tare da su;
A když to Pavel promluvil, vstal král, i vladař a Bernice, i ti, kteříž s nimi seděli.
31 da suka bar dakin taron, suka ci gaba da magana da juna suna cewa, “Wannan mutum bai yi wani abin da ya chanchanci mutuwa ko kuma dauri ba.”
A odšedše na stranu, mluvili spolu, řkouce: Nic hodného smrti neb vězení nečiní člověk tento.
32 Agaribas ya ce wa Fastos, “Da mutumin nan bai daukaka kara zuwa ga Kaisar ba da an sake shi.”
Agrippa pak Festovi řekl: Mohl propuštěn býti člověk tento, kdyby se byl neodvolal k císaři.

< Ayyukan Manzanni 26 >