< Ayyukan Manzanni 23 >
1 Bulus ya kura wa yan majalisa ido yace, '''Yan'uwa, na yi rayuwa tare da Allah da lamiri mai kyau har wannan ranan.''
Paul, regardant en face le Sanhédrin, dit: «Frères, «C'est en toute bonne conscience que je me suis conduit devant Dieu jusqu'à aujourd'hui...»
2 Babban firist Hannaniya ya ba wandanda suke tsaye tare da shi urmarni su buge bakinsa.
Le grand-prêtre Hananias ordonna alors aux assistants de souffleter Paul sur la bouche.
3 Bulus ya ce, “Allah zai buge ka, kai munafiki. Kana zama domin ka shari'anta ni da shari'a, kuma ka umarce a buge ni, gaba da sharia?''
«Dieu te frappera à ton tour, muraille blanchie!» répondit Paul en se tournant vers lui, «tu sièges pour me juger selon la Loi, et c'est au mépris de la Loi que tu ordonnes de me frapper!»
4 Wanda suka tsaya a gefe suka ce, ''Kada ka zage babban firis na Allah.'' Bulus yace, ''Ban sani ba, 'yan'uwa, cewa shi babban firis ne.
— «Quoi! tu injuries le grand-prêtre de Dieu!» dirent les assistants.
5 Domin a rubuce yake, Ba za ku zargi shugaban mutanenku ba.''
Mais Paul: «Je ne savais pas, frères, que ce fût le grand-prêtre, car il est écrit: «Tu n'insulteras pas le chef de ton peuple.»
6 Da Bulus ya ga cewa, daya bangaren Sadukiyawa ne dayan kuma Farisawa, ya yi magana da karfi a majalisa, '''Yan'uwa, ni Bafarise ne, dan Farisawa. Don tabbacin tashin matattu ne kuna shari'anta ni.''
Paul, sachant que l'assemblée était composée en partie de Sadducéens, en partie de Pharisiens, s'écria en plein Sanhédrin: «Frères, je suis Pharisien, fils de Pharisiens, c'est pour mon espérance, c'est pour la résurrection des morts qu'on me met en jugement!»
7 Daya fadi haka, mahawara ta fara a tsakanin Farisawa da Sadukiyawa, sai taron ya rabu kashi biyu.
Ces paroles provoquèrent une scission entre les Pharisiens et les Sadducéens et l'assemblée se divisa.
8 Don Sadukiyawa suka ce babu tashin matattu, babu mala'iku, babu kuma ruhohi, amma Farisawa suka ce dukan abubuwan nan sun kasance.
En effet, les Sadducéens nient la résurrection, l'existence des anges et des Esprits; les Pharisiens admettent tout cela.
9 Sai mahawara ta tashi, wadansu marubutan Farisawa suka tashi da mahawara cewa, ''Ba mu same mutumin nan da laifi ba sam. Ko mala'iku da ruhohi ne suka yi masa magana?''
Il s'ensuivit une discussion tumultueuse; certains Scribes du parti pharisien se levèrent, prirent la défense de Paul et dirent: «Nous ne trouvons rien à reprocher à cet homme... Si un Esprit lui a parlé! un ange, peut-être!»...
10 Da jayayya ta tashi, babban hafsa ya ji tsoro kada su yayaga Bulus, sai ya umarce sojoji suje su kwato shi da karfi daga 'yan majalisa, su tafi da shi farfajiya.
La dispute s'envenimait, et le tribun craignait que Paul ne fût mis en pièces; il donna ordre à une escouade de soldats de descendre dans la salle, d'arracher Paul de leurs mains et de le reconduire à la Forteresse.
11 Da dare Ubangiji ya tsaya kusa da shi yace, ''Kada ka ji tsoro, kamar yadda ka ba da shaida game da ni a Urushalima, dole zaka sake zama shaida a Roma.''
La nuit suivante, le Seigneur lui apparut et lui dit: «Courage! comme tu as été mon témoin à Jérusalem, il faut aussi que tu sois mon témoin à Rome!»
12 Da gari ya waye, wadansu Yahudawa sun yi yarjejeniya suka dauka wa kansu la'ana: suka ce ba za su ci ba ba za su sha ba sai sun kashe Bulus.
Le lendemain matin, les Juifs formèrent entre eux un complot et s'obligèrent par voeu à ne manger ni boire tant qu'ils n'auraient pas tué Paul.
13 Mutane fiye da arba'in suka kulla wannan makirci.
Ils étaient plus de quarante à avoir fait cette conjuration.
14 Suka je wurin manyan firistoci da dattawa suka ce, ''Mun sa wa kanmu la'ana, ba za mu ci ba, ba za mu sha ba sai mun kashe Bulus.
Ils allèrent trouver les chefs des prêtres et les Anciens et leur dirent: «Nous nous sommes obligés par voeu, sous les plus terribles anathèmes, à ne rien manger que nous n'ayons tué Paul.
15 Yanzu, bari majalisa ta ba wa babban hafsa izini a kawo shi a gaba, kamar zai yanke hukunci. Mu kam, a shirye muke mu kashe shi kafin ya iso nan.
Intervenez donc, avec le Sanhédrin, auprès du tribun pour obtenir une nouvelle comparution, comme si vous vouliez étudier plus à fond son affaire. Quant à nous, nous sommes prêts; nous le tuerons dans le trajet.»
16 Amma dan yar'uwan Bulus ya ji suna labe, sai ya tafi ya shiga farfajiyar ya fada wa Bulus.
Mais le fils de la soeur de Paul entendit parler de ce guet-apens, se rendit à la Forteresse, y entra et révéla tout à Paul.
17 Bulus ya kira daya daga cikin jarumai yace, ''Dauki saurayin nan ka kai shi wurin babban hafsa, don yana da abin da zai fada masa.''
Celui-ci fit alors appeler un des centurions: «Mène ce jeune homme au tribun, lui dit-il, il a quelque chose à lui communiquer.
18 Jarumin ya dauke saurayin ya kai shi wurin babban hafsa yace, ''Bulus dan sarka ne yace in kawo saurayin nan a gaban ka. Yana da abin da zai fada maka.''
Le centurion l'emmena donc chez le tribun et lui dit: «Le prisonnier Paul m'a fait appeler et m'a prié de t'amener ce jeune homme, qui a quelque chose à te dire.»
19 Babban hafsa ya kai shi wani lungu, sai ya tambaye shi, “Menene kake so ka fada mani?''
Le tribun prit le jeune homme par la main, le conduisit à l'écart et lui demanda: «Qu'as-tu à me communiquer?»
20 Saurayin yace, ''Yahudawa sun yarda su roke ka ka kawo Bulus gobe a majalisa, kamar zasu kara bincike a kan al'amarin.
— «Les Juifs, répondit-il, sont convenus de te prier de faire comparaître Paul demain devant le Sanhédrin, comme s'ils voulaient étudier plus à fond son affaire.
21 Amma kada ka yarda da su, mutane fiye da arba'in suna jiransa. Sun sa wa kansu la'anna, ba za su ci ba ba za su sha ba sai dai sun kashe shi. Yanzu a shirye suke; suna jira ka ba su izini.''
Garde-toi de le faire; c'est un guet-apens; ils sont plus de quarante qui se sont obligés par voeu à ne manger ni boire avant de l'avoir tué. Ils sont tout prêts; ils n'attendent que ton consentement.»
22 Sai babban hafsa yace wa saurayin ya tafi, da ya gama masa magana, ''Kar ka fada wa wani al'amuran.''
Le tribun renvoya le jeune homme en lui défendant de parler à personne de ce qu'il venait de lui apprendre.
23 Sai ya kira jarumai biyu yace, ''Ku shirya sojoji dari biyu, yan dawakai saba'in, masu daukar mashi dari biyu su tafi kaisariya karfe uku na dare.''
Puis il fit appeler deux centurions: «Tenez prêts, leur dit-il, à partir de la troisième heure de la nuit, deux cents soldats, soixante-dix cavaliers et deux cents hommes du train pour aller jusqu'à Césarée.»
24 Ya umarta a shirya dabbobin da Bulus zai hawo da zasu kai shi lafiya wurin Filikus gwamna.
Il commanda aussi de se pourvoir de montures pour Paul, afin de le mener sain et sauf au procurateur Félix.
25 Sai ya rubuta wasika a misalin haka:
En même temps il écrivit à celui-ci une lettre, dont voici la teneur:
26 Gaisuwa zuwa Kuludiyas Lisiyas zuwa ga mai martaba gwamna Filikus.
«Claudius Lysias à son excellence le procurateur Félix. Salut.
27 Yahudawa sun kama wannan mutumin suna shirin kashe shi, na abko masu da sojoji na kwace shi, bayan da na ji shi Barome ne.
«Cet homme a été arrêté par les Juifs, et ils allaient le tuer, quand j'arrivai avec la troupe et le leur enlevai; j'avais appris qu'il était citoyen romain.
28 Inna son sani dalilin zarginsa, sai na kai shi majalisa.
Voulant connaître le motif de leurs accusations, je le conduisis au Sanhédrin;
29 Na gane cewa ana zarginsa ne a kan tambayoyi game da shari'ansu, amma ba wani zargi da ya cancanci dauri ko mutuwa.
voici ce que je trouvai: des poursuites sur des questions relatives à leur Loi et aucun grief qui méritât la mort ou la prison.
30 Da aka sanar da ni shirin makircin, sai na tura shi wurinka ba da bata lokaci ba, na umarce masu zarginsa su kawo zarginsu wurinka. Huta lafiya.”
Mais on m'a dénoncé un complot contre cet homme; je te l'ai donc envoyé sans retard et j'ai prévenu les accusateurs qu'ils eussent aussi à prendre la parole contre lui devant toi.»
31 Sai sojoji suka yi biyayya da umarni da aka basu: suka dauki Bulus suka kawo shi dadare a wurin Antibatris.
Les soldats exécutèrent ces ordres; ils prirent Paul et le conduisirent de nuit jusqu'à Antipatris.
32 Da gari ya yawe, yan dawakai suka tafi tare da shi kuma sauran sojoji suka koma farfajiya.
Le lendemain, ils laissèrent les cavaliers continuer le chemin avec lui et rentrèrent à la Forteresse.
33 Bayan da yandawakan suka isa Kaisiririya sun mika wasika ga gwamna, suka kuma danka Bulus a hanunsa.
Ceux-là, arrivés à Césarée, remirent la lettre au procurateur et lui présentèrent Paul.
34 Da gwamna ya karanta wasikar, sai ya tambaye su daga wani yanki ne Bulus ya fito; da ya ji daga yankin kilikiya ne,
Il la lut et s'informa de quel pays il était. Apprenant qu'il était de Cilicie:
35 Yace zan saurare ka sosai lokacin da masu zargin ka sun zo. Sai ya umarta a tsare shi a fadar Hiridus.
«Je t'entendrai, dit-il, quand tes accusateurs seront arrivés.» Puis il ordonna de le garder dans le prétoire d'Hérode.