< Ayyukan Manzanni 21 >

1 Da muka rabu da su, muka shiga jirgin ruwa muka mike hanya zuwa birnin Kos, washegari sai birnin Rodusa, daga nan sai kuma zuwa birnin Batara.
Or il arriva qu’ayant fait voile, après nous être arrachés d’eux, nous vînmes droit à Cos, et le jour suivant à Rhodes, et de là à Patare.
2 Da muka sami jirgi mai hayewa zuwa Fonisiya sai muka shiga.
Et ayant rencontré un vaisseau qui allait en Phénicie, nous y montâmes, et mîmes à la voile.
3 Da muka hango tsibirin Kubrus muka bar shi a hagun mu muka nufi Suriya, muka sauka a birnin Taya domin a nan ne jirgin ruwan zai sauke kayansa.
Quand nous fûmes en vue de Chypre, la laissant à gauche, nous naviguâmes vers la Syrie et vînmes à Tyr, car c’est là que le vaisseau devait déposer sa charge.
4 Bayan mun sami almajirai sai muka zauna can kwana bakwai. Al'majiran suka ce ma Bulus, ta wurin Ruhu, kada ma ya je Urushalima.
Or, y ayant trouvé les disciples, nous y demeurâmes sept jours; et les disciples disaient par l’Esprit-Saint à Paul, de ne point monter à Jérusalem.
5 Bayan 'yan kwanaki muka cigaba da tafiyarmu. Dukansu da matansu da 'ya'yansu suka raka mu har bayan birnin. Sa'annan muka durkusa a bakin gacci muka yi addu'a muka yi sallama da juna.
Et ces jours écoulés, nous partîmes, et ils vinrent tous, avec leurs femmes et leurs enfants, nous conduire jusque hors de la ville; et nous étant agenouillés sur le rivage, nous priâmes.
6 Sai muka shiga jirgin ruwa, su kuma suka koma gida.
Et après nous être dit adieu les uns aux autres, nous montâmes sur le vaisseau, et ils s’en retournèrent chez eux.
7 Da muka gama tafiyarmu a Taya muka iso Talamayas. A nan ne muka gaisa da 'yan'uwa, muka zamna kwana daya da su.
Pour nous, terminant notre navigation de Tyr, nous descendîmes à Ptolémaïde, et, les frères salués, nous demeurâmes un jour avec eux.
8 Washegari muka tashi muka tafi Kaisariya. Muka shiga gidan Filibus mai shaida bishara, daya daga cikin bakwai din, muka zauna da shi.
Le lendemain, étant partis, nous vînmes à Césarée; et, entrant dans la maison de Philippe, l’évangéliste, qui était un des sept, nous demeurâmes chez lui.
9 Wannan mutum yana da 'ya'ya hudu mata, budurwai masu yin annabci.
Il avait quatre filles vierges qui prophétisaient.
10 Sa'anda muka zauna can 'yan kwanaki, wani annabi ya zo daga Yahudiya mai suna Agabus.
Et comme nous y demeurâmes quelques jours, il arriva de Judée un prophète nommé Agabus.
11 Ya zo wurinmu ya dauki damarar Bulus ya daure tasa kafar da hannayensa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki ya ce, 'Haka Yahudawa za su daure mai wannan damarar, zasu kuma bashe shi ga al'ummai.'”
Or, étant venu nous voir, il prit la ceinture de Paul, et, se liant les pieds et les mains, il dit: Voici ce que dit l’Esprit-Saint: L’homme à qui est cette ceinture, les Juifs le lieront ainsi à Jérusalem, et ils le livreront entre les mains des gentils.
12 Da muka ji wannan sakon, sai dukanmu da mazaunan wurin muka roki Bulus kada ya tafi Urushalima.
Ce qu’ayant entendu, nous conjurions Paul, nous et ceux qui étaient en cet endroit, de ne point monter à Jérusalem.
13 Sai Bulus ya amsa ya ce, “Me kuke yi, kuna kuka kuna karya mani zuciya? Bama a shirye don dauri kadai nake ba har ma da mutuwa a Urushalima, sabili da sunan Ubangiji Yesu.”
Alors Paul répondit et dit: Que faites-vous, pleurant et affligeant mon cœur? Car moi, je suis prêt, non seulement à être lié, mais à mourir à Jérusalem pour le nom du Seigneur Jésus.
14 Tun da Bulus bashi da niyyar a rinjaye shi, muka daina kuka muka ce, “Bari nufin Ubangiji ya tabbata.”
Mais ne pouvant le persuader, nous nous tînmes en repos, disant: Que la volonté du Seigneur soit faite.
15 Bayan wadannan kwanaki, muka dauki jakkunanmu muka haura Urushalima.
Après ces jours, ayant fait nos préparatifs, nous partîmes pour Jérusalem.
16 Wadansu almjirai daga Kaisariya suka bi mu. Sun zo ne tare da wani ana ce da shi Manason, mutumin Kuburus mai bi na farko, wanda za mu zauna da shi.
Or avec nous vinrent aussi quelques disciples de Césarée, amenant avec eux un certain Mnason, de Chypre, ancien disciple, chez qui nous devions loger.
17 Da muka isa Urushalima, 'yan'uwa suka marabce mu da farin ciki.
Quand nous fûmes arrivés à Jérusalem, les frères nous reçurent avec joie.
18 Washegari Bulus ya tafi tare da mu zuwa wurin Bitrus, dukan dattawa kuma suna nan.
Le jour suivant, Paul entrait avec nous chez Jacques, et tous les anciens s’assemblèrent.
19 Bayan ya gaishe su, sai ya shaida masu daya bayan daya abubuwan da Allah ya yi cikin al'ummai ta wurin hidimarsa.
Après les avoir salués, il racontait en détail ce que Dieu avait fait pour les gentils par son ministère.
20 Da suka ji haka, suka yabi Ubangiji suka ce masa, “Ka gani, dan'uwa, dubban Yahudawa sun bada gaskiya suna kuma da niyyar kiyaye shari'a.
Or eux, l’ayant entendu, glorifiaient Dieu; et ils lui dirent: Tu vois, mon frère, combien de milliers de Juifs ont cru; cependant tous sont zélés pour la loi.
21 An kuma gaya masu a kanka cewa, kana koya wa Yahudawan da suke zaune cikin al'ummai su yi watsi da Musa. Kana koya masu kada su yi wa 'ya'yansu kaciya, kada kuma su bi tsofaffin al'adu.
Or ils ont ouï dire de toi que tu enseignes aux Juifs qui sont parmi les gentils, d’abandonner Moïse, disant qu’ils ne doivent point circoncire leurs fils, ni marcher selon les coutumes.
22 Me ya kamata mu yi? Hakika za su ji ka zo.
Que faire donc? Certainement la multitude devra s’assembler, car ils apprendront que tu es arrivé.
23 Sabo da haka ka yi abin da muka fada maka yanzu. Muna da maza hudu da suka dauki wa'adi.
Fais donc ce que nous te disons: Nous avons ici quatre hommes qui sont liés par un vœu.
24 Tafi da wadannan ka tsarkake kanka tare da su, ka dauki dukan dawainiyar su dana askin kai. Ta haka kowanne mutum zai sani abubuwan da ake fadi a kanka karya ne. Za su sani cewa kai mai kiyaye shari'a ne.
Prends-les avec toi, purifie-toi avec eux, et paie pour eux, afin qu’ils se rasent la tête, et tous sauront que ce qu’ils ont entendu dire de toi est faux; mais que toi aussi tu marches observant la loi.
25 Game da al'umman da suka bada gaskiya mun yi masu wasika, mun bada umarni su kaurace kansu daga sadakokin da aka mika wa gumaku, da jini, da abin da aka makare da kuma fasikanci.
Quant à ceux qui ont cru d’entre les gentils, nous avons écrit qu’ils devaient s’abstenir de ce qui a été immolé aux idoles, du sang, des animaux étouffés et de la fornication.
26 Sai Bulus ya dauki mazannan, washegari ya tsarkake kansa tare da su, suka shiga haikali, domin ya sanar da cikar ranakun tsarkakewarsu, wato ranar ba da sadaka domin kowanne dayansu.
Alors Paul ayant pris ces hommes, et s’étant le lendemain purifié avec eux, entra dans le temple, indiquant les jours où s’accomplirait la purification, et quand l’offrande serait présentée pour chacun d’eux.
27 Da kwanakin nan bakwai suka yi gab da cika, wadansu Yahudawa daga Asiya suka ga Bulus a haikali, sai suka zuga taro, suka danke shi.
Mais comme les sept jours s’écoulaient, les Juifs d’Asie l’ayant vu dans le temple, émurent tout le peuple, et mirent la main sur lui, criant:
28 Suna ta kururuwa, “Mutanen Isra'ila ku taimaka mana. Wannan shine mutumin da ke koya wa dukan mutane ko'ina abubuwa gaba da mutane, da shari'a da kuma wannan wurin. Banda haka ya kawo Helenawa cikin haikalin nan ya kazantar da wannan wuri tsatsarka.”
Hommes d’Israël, au secours! Voici l’homme qui enseigne partout contre le peuple, contre la loi, et contre ce lieu; et qui, de plus, a introduit des gentils dans le temple, et a ainsi violé le saint lieu.
29 Domin dama sun ga Tarofimas mutumin Afisa tare da Bulus cikin birni, suka yi zaton ya kawo shi cikin haikali.
Ils avaient vu, en effet, Trophime, d’Ephèse, dans la ville avec Paul, et ils pensèrent que Paul l’avait introduit dans le temple.
30 Sai duk gari ya rude, mutane suka runtuma suka danke Bulus. Suka ja shi waje daga cikin haikalin, nan da nan aka rufe kofofin.
Aussitôt toute la ville s’émut, et il se fit un grand concours de peuple. S’étant donc saisis de Paul, ils l’entraînèrent hors du temple; et aussitôt les portes furent fermées.
31 Suna kokarin kashe shi kenan, sai labari ya kai wurin hafsan sojoji cewa Urushalima duk ta yamutse da tarzoma.
Comme ils cherchaient à la tuer, on vint dire au tribun de la cohorte: Tout Jérusalem est en confusion.
32 Nan take ya dauki mayaka da jarumawa, suka sheka da gudu wurin taron. Da mutane suka ga hafsan sojoji da rundunansa sai suka daina dukan Bulus.
Celui-ci ayant pris, sur le champ, des soldats et des centurions, courut à eux. Dès qu’ils virent le tribun et les soldats, ils cessèrent de frapper Paul.
33 Sai hafsan ya tafi ya danke Bulus ya sa aka daure shi da sarkoki biyu. Ya tambaya ko shi wanene da kuma laifinsa.
Alors s’approchant, le tribun le prit, et le fit lier de deux chaînes; et il demandait qui il était, et ce qu’il avait fait.
34 Wadansu cikin taron suna ta kururuwa wadansu su ce wannan, wadansu su ce, wancan. Tunda hafsan bai fahimci abin da suke fadi ba, sabo da ihunsu, ya dokaci a shigar da Bulus farfajiyar sojoji.
Mais, dans la foule, l’un criait une chose, l’autre une autre. Ne pouvant rien savoir de certain à cause du tumulte, il le fit conduire au camp.
35 Da suka kai matakala, sojoji suka dauki Bulus sabo da tsananin husatar taron jama'a.
Lorsque Paul fut arrivé sur les degrés, les soldats le portèrent, à cause de la violence du peuple.
36 Domin taron suka biyo baya suna ihu suna cewa, “A kashe shi.”
Car une multitude de peuple le suivait, criant: Ôte-le du monde.
37 An kusa shigar da shi farfajiyan kenan sai Bulus ya ce wa babban hafsan, “Ko ka yarda inyi magana da kai?” Hafsan ya ce, “Ka iya Helenanci?
Comme il allait entrer dans le camp, Paul demanda au tribun: M’est-il permis de vous dire quelque chose? Le tribun lui répondit: Sais-tu le grec?
38 Ashe ba kai ne Bamasaren nan da kwanakin baya ka haddasa tawaye, ka dauki 'yan ta'adda dubu hudu ka kai su jeji ba?”
N’es-tu pas cet Egyptien qui a excité, il y a quelques jours, une sédition, et qui a conduit au désert quatre mille sicaires?
39 Bulus ya ce, “Ni Ba'ibrane ne daga birnin Tarsus a Kilikiya. Ni dan kasar babban birni ne. Ka amince mani in yi magana da mutanen.”
Et Paul lui répondit: Je vous assure que je suis Juif, de Tarse en Cilicie, et citoyen de cette ville qui n’est pas inconnue. Permettez-moi, je vous prie, de parler au peuple.
40 Da hafsan ya bashi izni, Bulus ya mike a kan matakala ya daga hannayensa sama ya yi nuni su yi shuru. Da wuri ya yi tsit, Bulus ya yi masu magana da Ibraniyanci. Ya ce,
Le tribun l’ayant permis, Paul se tenant debout sur les degrés, fit signe de la main au peuple, et en grand silence s’étant fait, il leur parla en langue hébraïque, disant:

< Ayyukan Manzanni 21 >