< Ayyukan Manzanni 2 >

1 Da ranar Fentikos ta zo, dukansu suna tare wuri daya.
Now when the day of Pentecost had come, they were all together in one place.
2 Nan da nan sai ga wata kara daga sama kamar ta babbar iska, kuma ta sauko ta cika duka gidan inda suke zaune.
Suddenly there came from the sky a sound like the rushing of a mighty wind, and it filled all the house where they were sitting.
3 Sai ga wasu harsuna kamar na wuta sun bayyana a garesu aka rarraba su, kuma suka zauna bisa kowannensu.
Tongues like fire appeared and were distributed to them, and one sat on each of them.
4 Dukansu suka cika da Ruhu Mai Tsarki suka fara magana da wadansu harsuna, yadda Ruhu ya ba su iko su yi magana.
They were all filled with the Holy Spirit, and began to speak in other languages, as the Spirit enabled them to speak out.
5 A lokacin akwai Yahudawa dake zaune a Urushalima, mutanen Allah, daga kowace kasa karkashin sama.
Now there were dwelling in Jerusalem Jews, devout people from every nation under the sky.
6 Da suka ji wannan kara jama'a duk suka taru suka rude saboda kowannensu ya ji suna magana da harshensa.
When this sound was heard, the crowd came together, and were bewildered, because everyone heard them speaking in his own language.
7 Suka yi mamaki matuka; suka ce, ''Lallai, wadannan duka ba Galiliyawa ba ne?
They were all amazed and marveled, saying, "Look, are not all these who speak Galileans?
8 Yaya mu ke jinsu duka, kowannensu na magana a cikin harshen da aka haife mu?
How do we hear, everyone in our own native language?
9 Fisiyawa da Mediyawa da Elimawa, da Yahudawa da Kafadokiya, cikin Fontus da Asiya,
Parthians, Medes, Elamites, and people from Mesopotamia, Judea, Cappadocia, Pontus, Asia,
10 cikin Firgia da Bamfiliya, cikin Masar da yankunan Libiya ta wajen Sur, da baki daga Roma,
Phrygia, Pamphylia, Egypt, the parts of Libya around Cyrene, visitors from Rome, both Jews and proselytes,
11 Yahudawa da tubabbun cikin Yahudanci, Kiretawa da Larabawa, duk munji su suna fadi a harshenmu game da manyan ayyukan Allah.''
Cretans and Arabians: we hear them speaking in our tongues the mighty works of God."
12 Dukansu suka yi mamaki suka rikice; suka ce da junansu, ''Menene ma'anar wannan?''
They were all amazed, and were perplexed, saying one to another, "What does this mean?"
13 Amma wasu suka yi ba'a suka ce, ''Sun bugu ne da sabon ruwan inabi.''
Others, mocking, said, "They are filled with new wine."
14 Amma Bitrus ya tashi tare da sha dayan, ya daga murya ya ce da su, ''Mutanen Yahuda da dukanku dake zaune a Urushalima, bari ku san wannan; ku saurari maganata.
But Peter, standing up with the eleven, lifted up his voice, and spoke out to them, "You men of Judea, and all you who live in Jerusalem, let this be known to you, and listen to my words.
15 Domin wadannan mutanen ba buguwa suka yi ba yadda kuke zato, domin yanzu karfe tara ne na safe kawai.
For these are not drunk, as you suppose, seeing it is only nine in the morning.
16 Amma wannan shine abinda aka fada ta wurin annabi Yowel.
But this is what has been spoken through the prophet Joel:
17 Allah ya ce, 'Haka zai kasance a kwanakin karshe, zan zubo Ruhuna a kan dukan mutane, 'ya'yanku maza da mata za su yi anabci, kuma samarinku za su ga wahayoyi, kuma tsofaffinku za su yi mafarkai.
'And it will be in the last days, says God, that I will pour out my Spirit on all flesh; and your sons and your daughters will prophesy, and your young men will see visions, and your old men will dream dreams.
18 Haka kuma a bisa bayi na maza da mata, a kwanakin nan zan zubo da Ruhuna, kuma za su yi anabci.
And even on my servants, both men and women, I will pour out my Spirit in those days, and they will prophesy.
19 Zan nuna al'ajibai a sararin sama da kuma alamu a bisa duniya, jini da wuta, da girgije.
And I will show wonders in the sky above, and signs on the earth beneath; blood, and fire, and billows of smoke.
20 Rana zata juya ta koma duhu kuma wata ya koma jini, kafin Babbar ranan nan ta Ubangiji ta zo.
The sun will be turned into darkness, and the moon into blood, before the great and glorious day of the Lord comes.
21 Zai kuma zama dukan wanda ya kira ga sunan Ubangiji zai sami ceto.
And it will be that whoever will call on the name of the Lord will be saved.'
22 Mutanen Isra'ila, ku saurari wadannan magana. Yesu Banazare, mutumin da Allah ya tabbatar da shi gareku ta wurin manyan ayyuka da ban mamaki da alamu da Allah ya yi ta wurinsa a tsakiyarku, kamar yadda ku da kanku kuka sani.
"Men of Israel, hear these words. Jesus the Nazorean, a man approved by God to you by mighty works and wonders and signs which God did by him in the midst of you, even as you yourselves know,
23 Saboda tabbataccen shiri da riga sani na Allah, aka bayar dashi, ku kuma, ta hannun mutane 'yan tawaye, kuka gicciye shi kuma kuka kashe shi.
him, being delivered up by the determined counsel and foreknowledge of God, by the hand of lawless men, crucified and killed;
24 Wanda Allah ya tayar, bayan ya cire zafin mutuwa daga gareshi, saboda ba zai yiwu ba ta rike shi.
whom God raised up, having freed him from the pains of death, because it was not possible that he should be held by it.
25 Gama, game da shi, 'Ina ganin Ubangiji a gabana ko yaushe, domin yana gefen hannun damana saboda kada in firgita.
For David says concerning him, 'I saw the Lord always before me, for he is at my right hand, that I should not be shaken.
26 Saboda haka zuciyata na farin ciki harshena yana yin murna. Kuma, jikina zai zauna gabagadi.
Therefore my heart was glad, and my tongue rejoiced, and moreover my flesh also will dwell in hope;
27 Gama ba za ka watsar da raina a lahira ba, ba kuwa za ka bar Mai Tsarkinka ya ga ruba ba. (Hadēs g86)
because you will not abandon my soul in Sheol, neither will you allow your Holy One to see decay. (Hadēs g86)
28 Ka bayyana mani hanyar rai; da fuskarka zaka cika ni da farin ciki.
You made known to me the paths of life. You will make me full of joy in your presence.'
29 'Yan'uwa, zan yi magana da ku gabagadi game da baba Dauda: ya mutu kuma aka bizne shi, kuma kabarinsa na nan tare da mu har yau.
"Brothers, I may tell you freely of the patriarch David, that he both died and was buried, and his tomb is with us to this day.
30 Domin haka, don shi annabi ne kuma ya san Allah ya yi masa alkawari da rantsuwa cewa daga cikin zuriyarsa zai sanya wani bisa kursiyinsa.
Therefore, being a prophet, and knowing that God had sworn with an oath to him that one of his descendants would sit on his throne,
31 Ya hango wannan al'amari kuma ya yi magana game da tashin Almasihu, 'Ba ayi watsi da shi ba a lahira, kuma jikinsa bai ga rubewa ba.' (Hadēs g86)
he foreseeing this spoke about the resurrection of the Christ, that neither was he left in Sheol, nor did his flesh see decay. (Hadēs g86)
32 Wannan Yesun - Allah ya tashe shi, wanda dukanmu shaidu ne.
This Jesus God raised up, to which we all are witnesses.
33 Saboda haka yadda aka tashe shi zuwa hannun dama na Allah kuma ya karbi alkawarin Ruhu Mai Tsarki daga wurin Uba, shine ya zubo mana wannan da kuke gani kuma kuke ji.
Being therefore exalted by the right hand of God, and having received from the Father the promise of the Holy Spirit, he has poured out this, which you see and hear.
34 Dauda bai hau zuwa sama ba, amma ya ce, ''Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna hannun dama na,
For David did not ascend into the heavens, but he says himself, 'The Lord said to my Lord, "Sit by my right hand,
35 har sai na maida makiyanka abin takawar sawunka.'''
until I make your enemies a footstool for your feet."'
36 Saboda haka, bari gidan Isra'ila su sani tabbas wannan Yesun wanda kuka gicciye, Allah ya maishe shi Ubangiji da kuma Almasihu.
"Let all the house of Israel therefore know certainly that God has made him both Lord and Christ, this Jesus whom you crucified."
37 Da suka ji haka sai suka soku a zukatansu, suka cewa Bitrus da sauran manzanni, '''Yan'uwa me za mu yi?''
Now when they heard this, they were acutely distressed, and said to Peter and the rest of the apostles, "Brothers, what should we do?"
38 Sai Bitrus ya ce masu, ''Ku tuba ayi wa kowannenku baftisma, cikin sunan Yesu Almasihu domin gafarar zunubanku, kuma za ku karbi baiwar Ruhu Mai Tsarki.
Peter said to them, "Repent, and be baptized, every one of you, in the name of Jesus Christ for the forgiveness of your sins, and you will receive the gift of the Holy Spirit.
39 Domin alkawarin a gareku ne da 'ya'yanku da duk wadanda ke nesa, dukan iyakar mutanen da Ubangiji Allahnmu zai kira.''
For to you is the promise, and to your children, and to all who are far off, even as many as the Lord our God will call to himself."
40 Da maganganu da yawa ya ba da shaida kuma ya karfafa su; ya ce, ''Ku ceci kan ku daga wannan muguwar tsara.''
With many other words he testified, and he urged them, saying, "Save yourselves from this crooked generation."
41 Sai suka karbi maganar sa kuma aka yi ma su baftisma, a wannan rana kuma aka sami karin rayuka wajen dubu uku.
Then those who received his word were baptized. There were added that day about three thousand souls.
42 Su ka cigaba cikin koyarwar manzanni da zumunta, cikin kakkaryawar gurasa da kuma cikin addu'o'i.
They continued steadfastly in the apostles' teaching and fellowship, in the breaking of bread, and prayer.
43 Tsoro ya sauko bisa kowane rai, kuma aka yi abubuwan ban mamaki da alamu da yawa ta wurin manzannin.
Fear came on every soul, and many wonders and signs were done through the apostles.
44 Duka wadanda suka ba da gaskiya suna tare kuma komai nasu na kowanensu ne,
All who believed were together, and had all things in common.
45 kuma suka saida kadarorinsu da mallakarsu kuma suka rarrabawa kowa, bisa ga irin bukatar da kowannensu yake da ita.
They sold their possessions and goods, and distributed them to all, according as anyone had need.
46 A kowace rana suka cigaba tare da nufi daya a cikin haikali, suna kakkarya gurasa a gidaje, kuma suna raba abinci tsakaninsu cikin farin ciki da tawali'u a zuciya;
Day by day, continuing steadfastly with one accord in the temple, and breaking bread at home, they took their food with gladness and singleness of heart,
47 Suna yabon Allah kuma suna da tagomashi a gaban dukan mutane. Ubangiji kuma kullum yana kara masu wadanda suke samun ceto.
praising God, and having favor with all the people. The Lord added to their number day by day those who were being saved.

< Ayyukan Manzanni 2 >