< Ayyukan Manzanni 2 >
1 Da ranar Fentikos ta zo, dukansu suna tare wuri daya.
Og da Pinsefestens Dag kom, vare de alle endrægtigt forsamlede.
2 Nan da nan sai ga wata kara daga sama kamar ta babbar iska, kuma ta sauko ta cika duka gidan inda suke zaune.
Og der kom pludseligt fra Himmelen en Lyd som af et fremfarende vældigt Vejr og fyldte hele Huset, hvor de sade.
3 Sai ga wasu harsuna kamar na wuta sun bayyana a garesu aka rarraba su, kuma suka zauna bisa kowannensu.
Og der viste sig for dem Tunger som af Ild, der fordelte sig og satte sig på hver enkelt af dem.
4 Dukansu suka cika da Ruhu Mai Tsarki suka fara magana da wadansu harsuna, yadda Ruhu ya ba su iko su yi magana.
Og de bleve alle fyldte med den Helligånd, og de begyndte at tale i andre Tungemål, efter hvad Ånden gav dem at udsige.
5 A lokacin akwai Yahudawa dake zaune a Urushalima, mutanen Allah, daga kowace kasa karkashin sama.
Men der var Jøder, bosiddende i Jerusalem, gudfrygtige Mænd af alle Folkeslag under Himmelen.
6 Da suka ji wannan kara jama'a duk suka taru suka rude saboda kowannensu ya ji suna magana da harshensa.
Da denne Lyd kom, strømmede Mængden sammen og blev forvirret; thi hver enkelt hørte dem tale på hans eget Mål.
7 Suka yi mamaki matuka; suka ce, ''Lallai, wadannan duka ba Galiliyawa ba ne?
Og de forbavsedes alle og undrede sig og sagde: "Se, ere ikke alle disse, som tale, Galilæere?
8 Yaya mu ke jinsu duka, kowannensu na magana a cikin harshen da aka haife mu?
Hvor kunne vi da høre dem tale, hver på vort eget Mål, hvor vi ere fødte,
9 Fisiyawa da Mediyawa da Elimawa, da Yahudawa da Kafadokiya, cikin Fontus da Asiya,
Parthere og Medere og Elamiter, og vi, som høre hjemme i Mesopotamien, Judæa og Happadokien. Pontus og Asien,
10 cikin Firgia da Bamfiliya, cikin Masar da yankunan Libiya ta wajen Sur, da baki daga Roma,
i Frygien og Pamfylien, Ægypten og Libyens Egne ved Kyrene, og vi her boende Romere,
11 Yahudawa da tubabbun cikin Yahudanci, Kiretawa da Larabawa, duk munji su suna fadi a harshenmu game da manyan ayyukan Allah.''
Jøder og Proselyter, Kretere og Arabere, vi høre dem tale om Guds store Gerninger i vore Tungemål?"
12 Dukansu suka yi mamaki suka rikice; suka ce da junansu, ''Menene ma'anar wannan?''
Og de forbavsedes alle og, vare tvivlrådige og sagde den ene til den anden: "Hvad kan dette være?"
13 Amma wasu suka yi ba'a suka ce, ''Sun bugu ne da sabon ruwan inabi.''
Men andre sagde spottende: "De ere fulde af sød Vin."
14 Amma Bitrus ya tashi tare da sha dayan, ya daga murya ya ce da su, ''Mutanen Yahuda da dukanku dake zaune a Urushalima, bari ku san wannan; ku saurari maganata.
Da stod Peter frem med de elleve og opløftede sin Røst og talte til dem: "I jødiske Mænd og alle I, som bo i Jerusalem! dette være eder vitterligt, og låner Øre til mine Ord!
15 Domin wadannan mutanen ba buguwa suka yi ba yadda kuke zato, domin yanzu karfe tara ne na safe kawai.
Thi disse ere ikke drukne, som I mene; det er jo den tredje Time på Dagen;
16 Amma wannan shine abinda aka fada ta wurin annabi Yowel.
men dette er, hvad der et sagt ved Profeten Joel:
17 Allah ya ce, 'Haka zai kasance a kwanakin karshe, zan zubo Ruhuna a kan dukan mutane, 'ya'yanku maza da mata za su yi anabci, kuma samarinku za su ga wahayoyi, kuma tsofaffinku za su yi mafarkai.
"Og det skal ske i de sidste Dage, siger Gud, da vil jeg udgyde af min Ånd over alt Kød; og eders Sønner og eders Døtre skulle profetere, og de unge iblandt eder skulle se Syner, og de gamle iblandt eder skulle have Drømme.
18 Haka kuma a bisa bayi na maza da mata, a kwanakin nan zan zubo da Ruhuna, kuma za su yi anabci.
Ja, endog over mine Trælle og over mine Trælkvinder vil jeg i de Dage udgyde af min Ånd, og de skulle profetere.
19 Zan nuna al'ajibai a sararin sama da kuma alamu a bisa duniya, jini da wuta, da girgije.
Og jeg vil lade ske Undere på Himmelen oventil og Tegn på Jorden nedentil, Blod og Ild og rygende Damp.
20 Rana zata juya ta koma duhu kuma wata ya koma jini, kafin Babbar ranan nan ta Ubangiji ta zo.
Solen skal forvandles til Mørke og Månen til Blod, førend Herrens store og herlige Dag kommer.
21 Zai kuma zama dukan wanda ya kira ga sunan Ubangiji zai sami ceto.
Og det skal ske, enhver, som påkalder Herrens Navn, skal frelses."
22 Mutanen Isra'ila, ku saurari wadannan magana. Yesu Banazare, mutumin da Allah ya tabbatar da shi gareku ta wurin manyan ayyuka da ban mamaki da alamu da Allah ya yi ta wurinsa a tsakiyarku, kamar yadda ku da kanku kuka sani.
I israelitiske Mænd! hører disse Ord: Jesus af Nazareth, en Mand, som fra Gud var godtgjort for eder ved kraftige Gerninger og Undere og Tegn, hvilke Gud gjorde ved ham midt iblandt eder, som I jo selv vide,
23 Saboda tabbataccen shiri da riga sani na Allah, aka bayar dashi, ku kuma, ta hannun mutane 'yan tawaye, kuka gicciye shi kuma kuka kashe shi.
ham, som efter Guds bestemte Rådslutning og Forudviden var bleven forrådt, ham have I ved lovløses Hånd korsfæstet og ihjelslået.
24 Wanda Allah ya tayar, bayan ya cire zafin mutuwa daga gareshi, saboda ba zai yiwu ba ta rike shi.
Men Gud oprejste ham, idet han gjorde Ende på Dødens Veer, eftersom det ikke var muligt, at han kunde fastholdes af den.
25 Gama, game da shi, 'Ina ganin Ubangiji a gabana ko yaushe, domin yana gefen hannun damana saboda kada in firgita.
Thi David siger med Henblik på ham: "Jeg havde altid Herren for mine Øjne; thi han er ved min højre Hånd, for at jeg ikke skal rokkes,
26 Saboda haka zuciyata na farin ciki harshena yana yin murna. Kuma, jikina zai zauna gabagadi.
Derfor glædede mit Hjerte sig, og min Tunge jublede, ja, også mit Kød skal bo i Håb;
27 Gama ba za ka watsar da raina a lahira ba, ba kuwa za ka bar Mai Tsarkinka ya ga ruba ba. (Hadēs )
thi du skal ikke lade min Sjæl tilbage i Dødsriget, ikke heller tilstede din hellige at se Forrådnelse, (Hadēs )
28 Ka bayyana mani hanyar rai; da fuskarka zaka cika ni da farin ciki.
Du har kundgjort mig Livets Veje; du skal fylde mig med Glæde for dit Åsyn."
29 'Yan'uwa, zan yi magana da ku gabagadi game da baba Dauda: ya mutu kuma aka bizne shi, kuma kabarinsa na nan tare da mu har yau.
I Mænd Brødre! Jeg kan sige med Frimodighed til eder om Patriarken David, at han er både død og begraven, og hans Grav er hos os indtil denne Dag.
30 Domin haka, don shi annabi ne kuma ya san Allah ya yi masa alkawari da rantsuwa cewa daga cikin zuriyarsa zai sanya wani bisa kursiyinsa.
Da han nu var en Profet og vidste, at Gud med Ed havde tilsvoret ham, at af hans Lænds Frugt skulde en sidde på hans Trone,
31 Ya hango wannan al'amari kuma ya yi magana game da tashin Almasihu, 'Ba ayi watsi da shi ba a lahira, kuma jikinsa bai ga rubewa ba.' (Hadēs )
talte han, forudseende, om Kristi Opstandelse, at hverken blev han ladt tilbage i Dødsriget, ej heller så hans Kød Forrådnelse. (Hadēs )
32 Wannan Yesun - Allah ya tashe shi, wanda dukanmu shaidu ne.
Denne Jesus oprejste Gud, hvorom vi alle ere Vidner.
33 Saboda haka yadda aka tashe shi zuwa hannun dama na Allah kuma ya karbi alkawarin Ruhu Mai Tsarki daga wurin Uba, shine ya zubo mana wannan da kuke gani kuma kuke ji.
Efter at han nu ved Guds højre Hånd er ophøjet og af Faderen har fået den Helligånds Forjættelse, har han udgydt denne, hvilket I både se og høre.
34 Dauda bai hau zuwa sama ba, amma ya ce, ''Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna hannun dama na,
Thi David for ikke op til Himmelen; men han siger selv: "Herren sagde til min Herre: Sæt dig ved min højre Hånd,
35 har sai na maida makiyanka abin takawar sawunka.'''
indtil jeg får lagt dine Fjender som en Skammel for dine Fødder."
36 Saboda haka, bari gidan Isra'ila su sani tabbas wannan Yesun wanda kuka gicciye, Allah ya maishe shi Ubangiji da kuma Almasihu.
Derfor skal hele Israels Hus vide for vist, at denne Jesus, hvem I korsfæstede, har Gud gjort både til Herre og til Kristus,"
37 Da suka ji haka sai suka soku a zukatansu, suka cewa Bitrus da sauran manzanni, '''Yan'uwa me za mu yi?''
Men da de hørte dette, stak det dem i Hjertet, og de sagde til Peter og de øvrige Apostle: "I Mænd, Brødre! hvad skulle vi gøre?"
38 Sai Bitrus ya ce masu, ''Ku tuba ayi wa kowannenku baftisma, cikin sunan Yesu Almasihu domin gafarar zunubanku, kuma za ku karbi baiwar Ruhu Mai Tsarki.
Men Peter sagde til dem: "Omvender eder, og hver af eder lade sig døbe på Jesu Kristi Navn til eders Synders Forladelse; og I skulle få den Helligånds Gave.
39 Domin alkawarin a gareku ne da 'ya'yanku da duk wadanda ke nesa, dukan iyakar mutanen da Ubangiji Allahnmu zai kira.''
Thi for eder er Forjættelsen og for eders Børn og for alle dem, som ere langt borte, så mange som Herren vor Gud vil tilkalde."
40 Da maganganu da yawa ya ba da shaida kuma ya karfafa su; ya ce, ''Ku ceci kan ku daga wannan muguwar tsara.''
Også med mange andre Ord vidnede han for dem og format dem, idet han sagde: "Lader eder frelse fra denne vanartede Slægt!"
41 Sai suka karbi maganar sa kuma aka yi ma su baftisma, a wannan rana kuma aka sami karin rayuka wajen dubu uku.
De, som nu toge imod hans Ord, bleve døbte; og der føjedes samme Dag omtrent tre Tusinde Sjæle til.
42 Su ka cigaba cikin koyarwar manzanni da zumunta, cikin kakkaryawar gurasa da kuma cikin addu'o'i.
Og de holdt fast ved Apostlenes Lære og Samfundet, Brødets Brydelse og Bønnerne.
43 Tsoro ya sauko bisa kowane rai, kuma aka yi abubuwan ban mamaki da alamu da yawa ta wurin manzannin.
Men der kom Frygt over en hver Sjæl, og der skete mange Undere og Tegn ved Apostlene.
44 Duka wadanda suka ba da gaskiya suna tare kuma komai nasu na kowanensu ne,
Og alle de troende holdt sig sammen og havde alle Ting fælles.
45 kuma suka saida kadarorinsu da mallakarsu kuma suka rarrabawa kowa, bisa ga irin bukatar da kowannensu yake da ita.
Og de solgte deres Ejendom og Gods og delte det ud iblandt alle, efter hvad enhver havde Trang til.
46 A kowace rana suka cigaba tare da nufi daya a cikin haikali, suna kakkarya gurasa a gidaje, kuma suna raba abinci tsakaninsu cikin farin ciki da tawali'u a zuciya;
Og idet de hver Dag vedholdende og endrægtigt kom i Helligdommen og brød Brødet hjemme, fik de deres Føde med Fryd og i Hjertets Enfold,
47 Suna yabon Allah kuma suna da tagomashi a gaban dukan mutane. Ubangiji kuma kullum yana kara masu wadanda suke samun ceto.
idet de lovede Gud og havde Yndest hos hele Folket. Men Herren føjede daglig til dem nogle, som lode sig frelse.