< Ayyukan Manzanni 19 >

1 Sa'adda Afolos yake a Koranti, Bulus ya zagaya kasar tudu ya zo birnin Afisa, a nan kuma ya sami wadansu almajirai.
During the stay of Apollos in Corinth, Paul, after passing through the inland districts, came to Ephesus, where he found a few disciples.
2 Bulus ya ce masu, “Ko kun karbi Ruhu Mai Tsarki sa'anda kuka ba da gaskiya?” Suka amsa, “A'a bamu taba jin labarin Ruhu Mai Tsarki ba.
"Did you receive the Holy Spirit when you first believed?" he asked them. "No," they replied, "we did not even hear that there is a Holy Spirit."
3 Bulus ya ce, “Wacce irin baftisma aka yi maku?” Suka ce, “Baftismar Yahaya”
"Into what then were you baptized?" he asked. "Into John's baptism," they replied.
4 Bulus ya amsa ya ce, “Yahaya ya yi wa mutane baftismar tuba, ya ce su ba da gaskiya wanda zai zo bayansa, wato, Yesu kenan.”
"John," he said, "administered a baptism of repentance, bidding the people believe on One who was to come after him; namely, on Jesus."
5 Da mutanen suka ji haka, sai aka yi masu baftisma cikin sunan Ubangiji Yesu.
On hearing this, they were baptized into the name of the Lord Jesus;
6 Sa'adda Bulus ya dibiya hannu a kansu, Ruhu Mai Tsarki kuma ya sauka a kansu suka yi magana da harsuna da kuma annabci.
and when Paul laid his hands upon them, the Holy Spirit came on them, and they began to speak in tongues and to prophesy.
7 Su wajen mutum goma sha biyu ne.
They numbered in all about twelve men.
8 Bulus ya shiga majami'a ya yi ta koyarwa gabagadi misalin tsawon wata uku. Yana bi da su cikin nazarin maganar yana fahimtar da mutane su gaskanta game da abubuwa da suka shafi mulkin Allah.
Afterwards he went into the synagogue. There for three months he continued to preach fearlessly, explaining in words which carried conviction the truths which concern the Kingdom of God.
9 Amma sa'adda wadansu Yahudawa suka taurare, suka ki yin biyayya, sai suka fara bata hanyar Almasihu a gaban taron. Saboda haka sai Bulus ya janye daga wurinsu tare da wadanda suka ba da gaskiya. Ya fara koyarwa a makarantar Tiranus.
But some grew obstinate in unbelief and spoke evil of the new faith before all the congregation. So Paul left them, and, taking with him those who were disciples, held discussions daily in Tyrannus's lecture-hall.
10 Haka ya cigaba shekaru biyu har duk mazaunan Asiya suka ji maganar Ubangiji, Yahudawa da Helenawa.
This went on for two years, so that all the inhabitants of the province of Asia, Jews as well as Greeks, heard the Lord's Message.
11 Allah ya yi manyan al'ajibai ta hannun Bulus,
God also brought about extraordinary miracles through Paul's instrumentality.
12 har marasa lafiya suka warke, mugayen ruhohi suka fito daga cikin mutane, sa'adda suka karbi kyallaye da mayafai daga jikin Bulus.
Towels or aprons, for instance, which Paul had handled used to be carried to the sick, and they recovered from their ailments, or the evil spirits left them.
13 Amma akwai Yahudawa masu tsubu da suka biyo ta wajen, suka dauka wa kansu su yi amfani da sunan Yesu. Suka ce, “Mun dokace ku cikin sunan Yesu wanda Bulus yake wa'azinsa, ku fita.”
But there were also some wandering Jewish exorcists who undertook to invoke the name of Jesus over those who had the evil spirits, saying, "I command you by that Jesus whom Paul preaches."
14 Wadanda suka yi wannan su bakwai ne 'ya'yan wani babban firist Bayahude mai suna Siba.
There were seven sons of one Sceva, a Jew of high-priestly family, who were doing this.
15 Mugun ruhun ya amsa ya ce, “Na san Yesu, na san Bulus, amma ku, su wanene?”
"Jesus I know," the evil spirit answered, "and Paul I have heard of, but who are you?"
16 Sai mugun ruhun da ke cikin mutumin ya fada a kan matsubatan ya fi karfinsu ya kuma bubuge su. Suka runtuma da gudu suka fice daga dakin tsirara da raunuka.
And the man in whom the evil spirit was sprang on two of them, over-mastered them both, and treated them with such violence, that they fled from the house stripped of their clothes and wounded.
17 Wannan ya zama sanannen abu ga dukan mutane, Yahudawa da Helenawa mazaunan Afisa. Suka ji tsoro kwarai, sunan Ubangiji Yesu ya sami daukaka.
All the people of Ephesus, Jews as well as Greeks, came to know of this. There was widespread terror, and they began to hold the name of the Lord Jesus in high honour.
18 Masu bi da yawa kuma, suka zo suka furta mugayen ayyukan da suka aikata.
Many also of those who believed came confessing without reserve what their conduct had been,
19 Masu sihiri suka kawo littattafansu suka kona a gaban mutane. Da aka yi jimilar tamaninsu, aka samu sun kai dubu hamsin na azurfa.
and not a few of those who had practised magical arts brought their books together and burnt them in the presence of all. The total value was reckoned and found to be 50,000 silver coins.
20 Sai maganar Ubangiji ta yadu da iko ta hanyoyi da yawa.
Thus mightily did the Lord's Message spread and triumph!
21 Da Bulus ya kammala aikinsa na bishara a Afisa, Ruhu ya bishe shi sai ya bi ta Makidoniya da Akiya a kan hanyarsa zuwa Urushalima. Ya ce, “Bayan na je can, dole in je Roma.”
When matters had reached this point, Paul decided in his own mind to travel through Macedonia and Greece, and go to Jerusalem. "After that," he said, "I must also see Rome."
22 Bulus ya aiki almajiransa biyu Timoti da Irastus zuwa Makidoniya, wadanda suka taimake shi. Amma shi da kansa ya jira a Asiya na dan lokaci.
But he sent two of his assistants, Timothy and Erastus, to Macedonia, while he himself remained for a while in Roman Asia.
23 A wannan lokacin sai aka yi babban tashin hankali a Afisa game da wannan Hanyar.
Now just at that time there arose no small commotion about the new faith.
24 Wani Makeri mai suna Damatrayus wanda ke kera sifoffin gunkin azurfa na Dayana, wanda sana'a ce mai kawo wa makera riba sosai.
There was a certain Demetrius, a silversmith, who made miniature silver sanctuaries of Diana, a business which brought great gain to the mechanics in his employ.
25 Ya tattara makera ya ce da su, “Kun sa ni da wanan sana'a ne muke samun kudi mai yawa.
He called his workmen together, and others who were engaged in similar trades, and said to them, "You men well know that our prosperity depends on this business of ours;
26 Kun gani kun kuma ji cewa, ba a Afisa kadai ba, amma har da fadin kasar Asiya wannan Bulus ya rinjayi mutane da yawa. Yana cewa babu alloli da ake kerawa da hannu.
and you see and hear that, not in Ephesus only but throughout almost the whole province of Asia, this fellow Paul has led away a vast number of people by inducing them to believe that they are not gods at all that are made by men's hands.
27 Ba sana'ar mu kadai ke cikin hatsari ba, amma har da haikalin allahnmu Dayana babba zai zama mara amfani. Ta haka za ta rasa girmanta, ita da dukan kasar Asiya da duniya ke wa sujada.”
There is danger, therefore, not only that this our trade will become of no account, but also that the temple of the great goddess Diana will fall into utter disrepute, and that before long she will be actually deposed from her majestic rank--she who is now worshipped by the whole province of Asia; nay, by the whole world."
28 Da suka ji haka sai suka fusata kwarai, suka yi kira mai karfi suna cewa “Mai girma ce Dayana ta Afisa.”
After listening to this harangue, they became furiously angry and kept calling out, "Great is the Ephesian Diana!"
29 Gari gaba daya ya rude, jama'a kuma sun hanzarta zuwa wurin taron. Kafin wannan lokaci, sun riga sun kama abokan tafiyar Bulus, wato Gayus da Aristakas wadanda suka zo daga Makidoniya.
The riot and uproar spread through the whole city, till at last with one accord they rushed into the Theatre, dragging with them Gaius and Aristarchus, two Macedonians who were fellow travellers with Paul.
30 Bulus ya yi niyya ya shiga cikin taron jama'ar, amma almajiran suka hana shi.
Then Paul would have liked to go in and address the people, but the disciples would not let him do so.
31 Haka nan ma wadansu abokan Bulus da ke shugabanin yankin al'umma Asiya sun aika masa da roko mai karfi kada ya shiga dandalin.
A few of the public officials, too, who were friendly to him, sent repeated messages entreating him not to venture into the Theatre.
32 Wadansu mutane na kirarin wani abu, wadansu kuma na kirarin wani abu dabam, domin jama'a sun rude. Da yawa daga cikinsu ma ba su san dalilin taruwarsu ba.
The people, meanwhile, kept shouting, some one thing and some another; for the assembly was all uproar and confusion, and the greater part had no idea why they had come together.
33 Yahudawa suka kawo Iskandari ya tsaya a gaban taruwan jama'a. Iskandari ya mika hannunsa sama domin ya yi bayani ga jama'a.
Then some of the people crowded round Alexander, whom the Jews had pushed forward; and Alexander, motioning with his hand to get silence, was prepared to make a defence to the people.
34 Amma da suka gane shi Bayahude ne, sai dukansu suka kwala ihu wajen sa'a biyu, “Mai girma ce Dayana ta Afisa.”
No sooner, however, did they see that he was a Jew, than there arose from them all one roar of shouting, lasting about two hours. "Great is the Ephesian Diana," they said.
35 Da magatakardar garin ya sha kan jama'a, sai ya ce, “Ya ku mutanen Afisa, wanene bai san cewa birnin Afisa cibiya ce na allahn nan Dayana mai girma da na sifar da ta fado daga sama ba?
At length the Recorder quieted them down. "Men of Ephesus," he said, "who is there of all mankind that needs to be told that the city of Ephesus is the guardian of the temple of the great Diana and of the image which fell down from Zeus?
36 Tun da ba a karyata wadannan abubuwa ba, ya kamata ku yi shuru don kada ku yi wani abu a gaggauce.
These facts, then, being unquestioned, it becomes you to maintain your self-control and not act recklessly.
37 Gama kun kawo wadannan mutane a wannan dakin sharia ba a kan su mafasa ne na haikali ba ko kuma masu sabo ga allahnmu ba.
For you have brought these men here, who are neither robbers of temples nor blasphemers of our goddess.
38 Saboda haka idan Damatrayas da makeran da ke tare da su na da wata tuhuma a kan wani, kotuna suna nan a bude masu shari'a kuma suna nan. Ba ri su kai karar junansu.
If, however, Demetrius and the mechanics who support his contention have a grievance against any one, there are Assize-days and there are Proconsuls: let the persons interested accuse one another.
39 Amma idan akwai maganganu na dubawa, za a daidaita su a taronmu na lokaci lokaci.
But if you desire anything further, it will have to be settled in the regular assembly.
40 Domin hakika muna cikin hatsarin zargi game da hargitsin yau. Babu dalilin wanan yamutsi domin ba mu da bayani a kansa.”
For in connexion with to-day's proceedings there is danger of our being charged with attempted insurrection, there having been no real reason for this riot; nor shall we be able to justify the behaviour of this disorderly mob."
41 Da ya fadi haka, sai ya sallami taron.
With these words he dismissed the assembly.

< Ayyukan Manzanni 19 >