< Ayyukan Manzanni 17 >

1 Bayan sun wuce biranen Amfibolis da Aboloniya, sun iso birnin Tasalunika, in da akwai wata majami'ar Yahudawa a wurin.
paulasIlau AmphipalyApallOniyAnagarAbhyAM gatvA yatra yihUdIyAnAM bhajanabhavanamEkam AstE tatra thiSalanIkInagara upasthitau|
2 Bulus, kamar yadda ya saba, ya nufi wurinsu, yana tattaunawa da su har Asabaci uku, daga cikin littattafai.
tadA paulaH svAcArAnusArENa tESAM samIpaM gatvA vizrAmavAratrayE taiH sArddhaM dharmmapustakIyakathAyA vicAraM kRtavAn|
3 Bulus ya bude littattafai yana bayyana masu cewa, dole ne Almasihu ya sha wahala, ya kuma tashi daga matattu. Ya ce, ''Wannan Yesu kuwa da nake sanar maku, shine Almasihu''.
phalataH khrISTEna duHkhabhOgaH karttavyaH zmazAnadutthAnanjca karttavyaM yuSmAkaM sannidhau yasya yIzOH prastAvaM karOmi sa IzvarENAbhiSiktaH sa EtAH kathAH prakAzya pramANaM datvA sthirIkRtavAn|
4 Wasu Yahudawa sun yarda, sun bi Bulus da Sila, da wadansu Helenawa, da Shugabannin Mata da jama'a da yawa.
tasmAt tESAM katipayajanA anyadEzIyA bahavO bhaktalOkA bahyaH pradhAnanAryyazca vizvasya paulasIlayOH pazcAdgAminO jAtAH|
5 Yahudawan da basu ba da gaskiya ba suka cika da kishi, suka dauki wadansu 'yan ta'adda daga cikin kasuwa, suka tada tarzoma cikin birnin, mutane da yawa na bin su. Sun kai hari a gidan Yason, da niyyar fitar da Bulus da Sila a gaban jama'a.
kintu vizvAsahInA yihUdIyalOkA IrSyayA paripUrNAH santO haTaTsya katinayalampaTalOkAn sagginaH kRtvA janatayA nagaramadhyE mahAkalahaM kRtvA yAsOnO gRham Akramya prEritAn dhRtvA lOkanivahasya samIpam AnEtuM cESTitavantaH|
6 Amma da ba su ga Bulus da Sila ba, suka ja Yason da wasu 'yan'uwa masu bi zuwa gaban mahukuntar birnin, suna cewa, ''Wadannan ne fa masu ta da zaune tsaye, gashi sun zo mana.
tESAmuddEzam aprApya ca yAsOnaM katipayAn bhrAtRMzca dhRtvA nagarAdhipatInAM nikaTamAnIya prOccaiH kathitavantO yE manuSyA jagadudvATitavantastE 'trApyupasthitAH santi,
7 Wadannan mutane da Yason ya marabta, sun saba wa dokokin Kaisar; Suna cewa akwai wani sarki mai suna - Yesu.''
ESa yAsOn AtithyaM kRtvA tAn gRhItavAn| yIzunAmaka EkO rAjastIti kathayantastE kaisarasyAjnjAviruddhaM karmma kurvvati|
8 Da taron jama'a, da mahukuntan birnin suka ji haka, sun damu.
tESAM kathAmimAM zrutvA lOkanivahO nagarAdhipatayazca samudvignA abhavan|
9 Bayan da sun amshi kudi daga wurin Yason da sauran 'yan'uwan, sai suka sake su.
tadA yAsOnastadanyESAnjca dhanadaNPaM gRhItvA tAn parityaktavantaH|
10 A wannan daren, 'yan'uwa masu bi suka fitar da Bulus da Sila, suka aike su garin Biriya. Da isar su can, su ka nufa majami'ar Yahudawa.
tataH paraM bhrAtRgaNO rajanyAM paulasIlau zIghraM birayAnagaraM prESitavAn tau tatrOpasthAya yihUdIyAnAM bhajanabhavanaM gatavantau|
11 Mutanen Biriya daban suke da na Tasalunika, sun yarda da sakon Bulus da zuciya daya, suna kuma binciken littattafai kowace rana domin su tabbatar da sakon Bulus, ko gaskiya ne.
tatrasthA lOkAH thiSalanIkIsthalOkEbhyO mahAtmAna Asan yata itthaM bhavati na vEti jnjAtuM dinE dinE dharmmagranthasyAlOcanAM kRtvA svairaM kathAm agRhlan|
12 Saboda haka mutane da yawa cikin su sun ba da gaskiya, tare da wadansu sannanun mata Helenawa da maza da yawa.
tasmAd anEkE yihUdIyA anyadEzIyAnAM mAnyA striyaH puruSAzcAnEkE vyazvasan|
13 Amma da Yahudawan Tasalunika suka ji cewa Bulus yana wa'azin kalmar Allah a Biriya, sun haura can, sun tada hankulan jama'a.
kintu birayAnagarE paulEnEzvarIyA kathA pracAryyata iti thiSalanIkIsthA yihUdIyA jnjAtvA tatsthAnamapyAgatya lOkAnAM kupravRttim ajanayan|
14 Nan da nan, masu bi na Biriya sun dauki Bulus sun aika shi zuwa teku, an bar Sila da Timoti a Biriya tukuna.
ataEva tasmAt sthAnAt samudrENa yAntIti darzayitvA bhrAtaraH kSipraM paulaM prAhiNvan kintu sIlatImathiyau tatra sthitavantau|
15 Wadanda sun fitar da Bulus, sun kai shi har zuwa birnin Atina. Bulus ya ba su sako, su fada wa Sila da Timoti suyi hanzari su same shi.
tataH paraM paulasya mArgadarzakAstam AthInInagara upasthApayan pazcAd yuvAM tUrNam Etat sthAnaM AgamiSyathaH sIlatImathiyau pratImAm AjnjAM prApya tE pratyAgatAH|
16 Sa'anda Bulus yana jiran zuwan Sila da Timoti a Atina, ya yi fushi a ransa, da ya ga birnin cike da gumakai.
paula AthInInagarE tAvapEkSya tiSThan tannagaraM pratimAbhiH paripUrNaM dRSTvA santaptahRdayO 'bhavat|
17 Ya tattauna da Yahudawa a cikin majami'a tare da masu yin sujada ga Allah, da kuma wadanda yake samu a kowace rana, a kasuwa.
tataH sa bhajanabhavanE yAn yihUdIyAn bhaktalOkAMzca haTTE ca yAn apazyat taiH saha pratidinaM vicAritavAn|
18 Amma wadan su Abikuriyawa da masana sun yi karo da shi. Wadansun su na cewa, ''Menene wannan sakaren ke cewa?'' Wadansu kuma sun ce, ''Da alama mai wa'azi ne na wasu alloli dabam,'' domin yana wa'azin Yesu da tashin sa daga matattu.
kintvipikUrIyamatagrahiNaH stOyikIyamatagrAhiNazca kiyantO janAstEna sArddhaM vyavadanta| tatra kEcid akathayan ESa vAcAlaH kiM vaktum icchati? aparE kEcid ESa janaH kESAnjcid vidEzIyadEvAnAM pracAraka ityanumIyatE yataH sa yIzum utthitinjca pracArayat|
19 Suka dauki Bulus zuwa Tudun Arasa, suna cewa, ''Ko za ka sanar mana da wannan sabuwar koyaswar taka?
tE tam arEyapAganAma vicArasthAnam AnIya prAvOcan idaM yannavInaM mataM tvaM prAcIkaza idaM kIdRzaM Etad asmAn zrAvaya;
20 Abubbuwan da kake fadi, baki ne a gare mu. Muna so mu san ma'anar su.''
yAmimAm asambhavakathAm asmAkaM karNagOcarIkRtavAn asyA bhAvArthaH ka iti vayaM jnjAtum icchAmaH|
21 (Atiniyawa da bakin da ke cikinsu, suna ba da lokacin su ga fadin sabobbin abubuwa da sauraron su).
tadAthInInivAsinastannagarapravAsinazca kEvalaM kasyAzcana navInakathAyAH zravaNEna pracAraNEna ca kAlam ayApayan|
22 Bulus ya tsaya a tsakiyar Tudun Arasa ya ce, ''Ku mutanen Atiniya na lura masu kwazon addini ne ku.
paulO'rEyapAgasya madhyE tiSThan EtAM kathAM pracAritavAn, hE AthInIyalOkA yUyaM sarvvathA dEvapUjAyAm AsaktA ityaha pratyakSaM pazyAmi|
23 Na lura da abubuwan sujadar ku yayin da nake zagawa, amma na ga wani bagadi da rubutu a kansa mai cewa, ''Ga Allah wanda ba a sani ba.” Abin da kuke bauta wa cikin rashin sani, shi nake sanar maku.
yataH paryyaTanakAlE yuSmAkaM pUjanIyAni pazyan ‘avijnjAtEzvarAya` EtallipiyuktAM yajnjavEdImEkAM dRSTavAn; atO na viditvA yaM pUjayadhvE tasyaiva tatvaM yuSmAn prati pracArayAmi|
24 Allahn da ya yi duniya da kome da ke cikinta, tun da ya ke shine Ubangijin sama da kasa, ba ya zama a haikalin da mutane suka gina da hannu.
jagatO jagatsthAnAM sarvvavastUnAnjca sraSTA ya IzvaraH sa svargapRthivyOrEkAdhipatiH san karanirmmitamandirESu na nivasati;
25 Ba ya neman taimakon kowa, babu kuma wanda ya isa ya ba shi. Shine ke ba da rai, da numfashi da kowanne abu.
sa Eva sarvvEbhyO jIvanaM prANAn sarvvasAmagrIzca pradadAti; ataEva sa kasyAzcit sAmagyrA abhAvahEtO rmanuSyANAM hastaiH sEvitO bhavatIti na|
26 Daga mutum daya ya hallici dukan al'umman duniya, ya rarraba, ya kuma sanya kowa a inda ya shirya masa.
sa bhUmaNPalE nivAsArtham EkasmAt zONitAt sarvvAn manuSyAn sRSTvA tESAM pUrvvanirUpitasamayaM vasatisImAnjca niracinOt;
27 Domin su nemi Allah ko za su iya kaiwa zuwa gareshi su same shi, ga shi kuwa ba ya nesa da kowannenmu.
tasmAt lOkaiH kEnApi prakArENa mRgayitvA paramEzvarasya tatvaM prAptuM tasya gavESaNaM karaNIyam|
28 A cikinsa muke rayuwa, muna walwala, kamar yadda wani daga cikin masananku yace, 'Mu 'ya'yansa ne'.
kintu sO'smAkaM kasmAccidapi dUrE tiSThatIti nahi, vayaM tEna nizvasanaprazvasanagamanAgamanaprANadhAraNAni kurmmaH, punazca yuSmAkamEva katipayAH kavayaH kathayanti ‘tasya vaMzA vayaM smO hi` iti|
29 Idan mu 'ya'yan Allah ne, bai kamata mu danganta Allah da zinariya ko azurfa, ko kuma duwatsu da itatuwa da an sassaka ba.
ataEva yadi vayam Izvarasya vaMzA bhavAmastarhi manuSyai rvidyayA kauzalEna ca takSitaM svarNaM rUpyaM dRSad vaitESAmIzvaratvam asmAbhi rna jnjAtavyaM|
30 Saboda haka ne, Allah ya kawar da kwanakin jahilci, amma ya ba da umarni kowa a ko'ina ya tuba.
tESAM pUrvvIyalOkAnAm ajnjAnatAM pratIzvarO yadyapi nAvAdhatta tathApIdAnIM sarvvatra sarvvAn manaH parivarttayitum AjnjApayati,
31 Akwai ranar da ya shirya zai yi wa duniya shari'a cikin adalci, ta wurin mutumin da ya zaba. Allah ya nuna wannan mutumin, ta wurin ta da shi daga matattu''.
yataH svaniyuktEna puruSENa yadA sa pRthivIsthAnAM sarvvalOkAnAM vicAraM kariSyati taddinaM nyarUpayat; tasya zmazAnOtthApanEna tasmin sarvvEbhyaH pramANaM prAdAt|
32 Da mutanen Atina sun ji batun tashi daga matattu, wadansu suka yi wa Bulus ba'a; amma wadansu kuma sun ce, ''Za mu saurare ka kuma, a kan wannan maganar.''
tadA zmazAnAd utthAnasya kathAM zrutvA kEcid upAhaman, kEcidavadan EnAM kathAM punarapi tvattaH zrOSyAmaH|
33 Bayan haka, Bulus ya bar su.
tataH paulastESAM samIpAt prasthitavAn|
34 Amma wasu maza a cikinsu sun yarda da bisharar, sun ba da gaskiya, hade da Diyonisiyus dan Majalisar Tudun Arasa da wata mace mai suna Damaris, da wadansu tare da su.
tathApi kEcillOkAstEna sArddhaM militvA vyazvasan tESAM madhyE 'rEyapAgIyadiyanusiyO dAmArInAmA kAcinnArI kiyantO narAzcAsan|

< Ayyukan Manzanni 17 >