< Ayyukan Manzanni 17 >

1 Bayan sun wuce biranen Amfibolis da Aboloniya, sun iso birnin Tasalunika, in da akwai wata majami'ar Yahudawa a wurin.
And having passed through Amphipolis, and Apollonia, they came to Thessalonica, where the synagogue of the Jews was,
2 Bulus, kamar yadda ya saba, ya nufi wurinsu, yana tattaunawa da su har Asabaci uku, daga cikin littattafai.
and according to the custom of Paul, he went in to them, and for three Sabbaths he was reasoning with them from the Writings,
3 Bulus ya bude littattafai yana bayyana masu cewa, dole ne Almasihu ya sha wahala, ya kuma tashi daga matattu. Ya ce, ''Wannan Yesu kuwa da nake sanar maku, shine Almasihu''.
opening and alleging that it was necessary [for] the Christ to suffer, and to rise again out of the dead, and that “this is the Christ—Jesus whom I proclaim to you.”
4 Wasu Yahudawa sun yarda, sun bi Bulus da Sila, da wadansu Helenawa, da Shugabannin Mata da jama'a da yawa.
And certain of them believed, and attached themselves to Paul and to Silas, also a great multitude of the worshiping Greeks, also not a few of the principal women.
5 Yahudawan da basu ba da gaskiya ba suka cika da kishi, suka dauki wadansu 'yan ta'adda daga cikin kasuwa, suka tada tarzoma cikin birnin, mutane da yawa na bin su. Sun kai hari a gidan Yason, da niyyar fitar da Bulus da Sila a gaban jama'a.
And the Jews, having been moved with envy, and having taken to themselves certain evil men of the agitators, and having made a crowd, were setting the city in an uproar; having also assailed the house of Jason, they were seeking them to bring [them] to the populace,
6 Amma da ba su ga Bulus da Sila ba, suka ja Yason da wasu 'yan'uwa masu bi zuwa gaban mahukuntar birnin, suna cewa, ''Wadannan ne fa masu ta da zaune tsaye, gashi sun zo mana.
and having not found them, they drew Jason and certain brothers to the city rulers, calling aloud, “These, having put the world in commotion, are also present here,
7 Wadannan mutane da Yason ya marabta, sun saba wa dokokin Kaisar; Suna cewa akwai wani sarki mai suna - Yesu.''
whom Jason has received; and all these do contrary to the decrees of Caesar, saying another to be king—Jesus.”
8 Da taron jama'a, da mahukuntan birnin suka ji haka, sun damu.
And they troubled the multitude and the city rulers, hearing these things,
9 Bayan da sun amshi kudi daga wurin Yason da sauran 'yan'uwan, sai suka sake su.
and having taken security from Jason and the rest, they let them go.
10 A wannan daren, 'yan'uwa masu bi suka fitar da Bulus da Sila, suka aike su garin Biriya. Da isar su can, su ka nufa majami'ar Yahudawa.
And the brothers immediately, through the night, sent forth both Paul and Silas to Berea, who having come, went into the synagogue of the Jews;
11 Mutanen Biriya daban suke da na Tasalunika, sun yarda da sakon Bulus da zuciya daya, suna kuma binciken littattafai kowace rana domin su tabbatar da sakon Bulus, ko gaskiya ne.
and these were more noble than those in Thessalonica; they received the word with all readiness of mind, examining the Writings every day [to see] whether those things were so;
12 Saboda haka mutane da yawa cikin su sun ba da gaskiya, tare da wadansu sannanun mata Helenawa da maza da yawa.
therefore, many of them, indeed, believed, and not a few of the honorable Greek women and men.
13 Amma da Yahudawan Tasalunika suka ji cewa Bulus yana wa'azin kalmar Allah a Biriya, sun haura can, sun tada hankulan jama'a.
And when the Jews from Thessalonica knew that also in Berea was the word of God declared by Paul, they came there also, agitating the multitudes;
14 Nan da nan, masu bi na Biriya sun dauki Bulus sun aika shi zuwa teku, an bar Sila da Timoti a Biriya tukuna.
and then immediately the brothers sent forth Paul, to go on as it were to the sea, but both Silas and Timotheus were remaining there.
15 Wadanda sun fitar da Bulus, sun kai shi har zuwa birnin Atina. Bulus ya ba su sako, su fada wa Sila da Timoti suyi hanzari su same shi.
And those conducting Paul, brought him to Athens, and having received a command to Silas and Timotheus that with all speed they may come to him, they departed;
16 Sa'anda Bulus yana jiran zuwan Sila da Timoti a Atina, ya yi fushi a ransa, da ya ga birnin cike da gumakai.
and Paul waiting for them in Athens, his spirit was stirred in him, beholding the city wholly given to idolatry,
17 Ya tattauna da Yahudawa a cikin majami'a tare da masu yin sujada ga Allah, da kuma wadanda yake samu a kowace rana, a kasuwa.
therefore, indeed, he was reasoning in the synagogue with the Jews, and with the worshiping persons, and in the marketplace every day with those who met with him.
18 Amma wadan su Abikuriyawa da masana sun yi karo da shi. Wadansun su na cewa, ''Menene wannan sakaren ke cewa?'' Wadansu kuma sun ce, ''Da alama mai wa'azi ne na wasu alloli dabam,'' domin yana wa'azin Yesu da tashin sa daga matattu.
And certain of the Epicurean and of the Stoic philosophers, were meeting together to see him, and some were saying, “What would this seed picker wish to say?” And others, “He seems to be an announcer of strange demons”; because he proclaimed to them Jesus and the resurrection as good news,
19 Suka dauki Bulus zuwa Tudun Arasa, suna cewa, ''Ko za ka sanar mana da wannan sabuwar koyaswar taka?
having also taken him, they brought [him] to the Areopagus, saying, “Are we able to know what this new teaching [is] that is spoken by you,
20 Abubbuwan da kake fadi, baki ne a gare mu. Muna so mu san ma'anar su.''
for you bring certain strange things to our ears? We resolve, then, to know what these things would wish to be”;
21 (Atiniyawa da bakin da ke cikinsu, suna ba da lokacin su ga fadin sabobbin abubuwa da sauraron su).
and all Athenians, and the strangers sojourning, for nothing else were at leisure but to say something, and to hear some newer thing.
22 Bulus ya tsaya a tsakiyar Tudun Arasa ya ce, ''Ku mutanen Atiniya na lura masu kwazon addini ne ku.
And Paul, having stood in the midst of the Areopagus, said, “Men, Athenians, in all things I perceive you as over-religious;
23 Na lura da abubuwan sujadar ku yayin da nake zagawa, amma na ga wani bagadi da rubutu a kansa mai cewa, ''Ga Allah wanda ba a sani ba.” Abin da kuke bauta wa cikin rashin sani, shi nake sanar maku.
for passing through and contemplating your objects of worship, I also found an altar on which had been inscribed: To God—unknown; whom, therefore—not knowing—you worship, this One I announce to you.
24 Allahn da ya yi duniya da kome da ke cikinta, tun da ya ke shine Ubangijin sama da kasa, ba ya zama a haikalin da mutane suka gina da hannu.
God, who made the world, and all things in it, this One, being Lord of Heaven and of earth, does not dwell in temples made with hands,
25 Ba ya neman taimakon kowa, babu kuma wanda ya isa ya ba shi. Shine ke ba da rai, da numfashi da kowanne abu.
neither is He served by the hands of men—needing anything, He giving life to all, and breath, and all things;
26 Daga mutum daya ya hallici dukan al'umman duniya, ya rarraba, ya kuma sanya kowa a inda ya shirya masa.
He also made every nation of man of one blood, to dwell on all the face of the earth—having ordained times before appointed, and the bounds of their dwellings—
27 Domin su nemi Allah ko za su iya kaiwa zuwa gareshi su same shi, ga shi kuwa ba ya nesa da kowannenmu.
to seek the LORD, if perhaps they felt after Him and found, though, indeed, He is not far from each one of us,
28 A cikinsa muke rayuwa, muna walwala, kamar yadda wani daga cikin masananku yace, 'Mu 'ya'yansa ne'.
for in Him we live, and move, and are; as certain of your poets have also said: For we are also His offspring.
29 Idan mu 'ya'yan Allah ne, bai kamata mu danganta Allah da zinariya ko azurfa, ko kuma duwatsu da itatuwa da an sassaka ba.
Being, therefore, offspring of God, we ought not to think the Godhead to be like to gold, or silver, or stone, [an] engraving of art and imagination of man;
30 Saboda haka ne, Allah ya kawar da kwanakin jahilci, amma ya ba da umarni kowa a ko'ina ya tuba.
therefore indeed God, having overlooked the times of ignorance, now commands all men everywhere to convert,
31 Akwai ranar da ya shirya zai yi wa duniya shari'a cikin adalci, ta wurin mutumin da ya zaba. Allah ya nuna wannan mutumin, ta wurin ta da shi daga matattu''.
because He set a day in which He is about to judge the world in righteousness, by a Man whom He ordained, having given assurance to all, having raised Him out of the dead.”
32 Da mutanen Atina sun ji batun tashi daga matattu, wadansu suka yi wa Bulus ba'a; amma wadansu kuma sun ce, ''Za mu saurare ka kuma, a kan wannan maganar.''
And having heard of a resurrection of the dead, some, indeed, were mocking, but others said, “We will hear you again concerning this”;
33 Bayan haka, Bulus ya bar su.
and so Paul went forth from the midst of them,
34 Amma wasu maza a cikinsu sun yarda da bisharar, sun ba da gaskiya, hade da Diyonisiyus dan Majalisar Tudun Arasa da wata mace mai suna Damaris, da wadansu tare da su.
and certain men having cleaved to him, believed, among whom [is] also Dionysius the Areopagite, and a woman, by name Damaris, and others with them.

< Ayyukan Manzanni 17 >