< Ayyukan Manzanni 17 >
1 Bayan sun wuce biranen Amfibolis da Aboloniya, sun iso birnin Tasalunika, in da akwai wata majami'ar Yahudawa a wurin.
After Paul and Silas had passed through Amphipolis and Apollonia they arrived at Thessalonica, where there was a Jewish synagogue.
2 Bulus, kamar yadda ya saba, ya nufi wurinsu, yana tattaunawa da su har Asabaci uku, daga cikin littattafai.
As usual, Paul went into the synagogue and over the course of three Sabbaths he debated with them using the Scriptures.
3 Bulus ya bude littattafai yana bayyana masu cewa, dole ne Almasihu ya sha wahala, ya kuma tashi daga matattu. Ya ce, ''Wannan Yesu kuwa da nake sanar maku, shine Almasihu''.
He explained what the Scriptures meant, proving that the Messiah had to die and rise from the dead. “This Jesus I'm telling you about—he is the Messiah,” he told them.
4 Wasu Yahudawa sun yarda, sun bi Bulus da Sila, da wadansu Helenawa, da Shugabannin Mata da jama'a da yawa.
Some of them were convinced and joined Paul and Silas, along with many Greek-speaking worshipers and some leading women of the town.
5 Yahudawan da basu ba da gaskiya ba suka cika da kishi, suka dauki wadansu 'yan ta'adda daga cikin kasuwa, suka tada tarzoma cikin birnin, mutane da yawa na bin su. Sun kai hari a gidan Yason, da niyyar fitar da Bulus da Sila a gaban jama'a.
But the Jews became jealous and with some rabble-rousers they gathered from the marketplace they formed a mob. They rioted in the town, and attacked Jason's house. They tried to find Paul and Silas so they could bring them before the people.
6 Amma da ba su ga Bulus da Sila ba, suka ja Yason da wasu 'yan'uwa masu bi zuwa gaban mahukuntar birnin, suna cewa, ''Wadannan ne fa masu ta da zaune tsaye, gashi sun zo mana.
When they couldn't find them they dragged Jason and some of the other believers before the town leaders, shouting, “These people are famous for causing trouble, turning the world upside down. Now they've come here,
7 Wadannan mutane da Yason ya marabta, sun saba wa dokokin Kaisar; Suna cewa akwai wani sarki mai suna - Yesu.''
and Jason has made them welcome in his house. They all defy Caesar's decrees, committing treason by saying there is another king called Jesus.”
8 Da taron jama'a, da mahukuntan birnin suka ji haka, sun damu.
The people and the leaders of the town were very disturbed when they heard this.
9 Bayan da sun amshi kudi daga wurin Yason da sauran 'yan'uwan, sai suka sake su.
So they made Jason and the others post bail before they let them go.
10 A wannan daren, 'yan'uwa masu bi suka fitar da Bulus da Sila, suka aike su garin Biriya. Da isar su can, su ka nufa majami'ar Yahudawa.
The believers had Paul and Silas leave for Berea that very night. When they arrived in Berea they went to the Jewish synagogue.
11 Mutanen Biriya daban suke da na Tasalunika, sun yarda da sakon Bulus da zuciya daya, suna kuma binciken littattafai kowace rana domin su tabbatar da sakon Bulus, ko gaskiya ne.
The people there had a better attitude than those in Thessalonica in that they were very quick to accept the word, and every day they examined the Scriptures to make sure what they were told was right.
12 Saboda haka mutane da yawa cikin su sun ba da gaskiya, tare da wadansu sannanun mata Helenawa da maza da yawa.
As a result many of them became believers, along with some highly-placed Greek women and men.
13 Amma da Yahudawan Tasalunika suka ji cewa Bulus yana wa'azin kalmar Allah a Biriya, sun haura can, sun tada hankulan jama'a.
But when the Jews in Thessalonica heard that Paul was also spreading the word of God in Berea, they went there and caused the same kind of trouble, stirring up the crowds.
14 Nan da nan, masu bi na Biriya sun dauki Bulus sun aika shi zuwa teku, an bar Sila da Timoti a Biriya tukuna.
Immediately the believers sent Paul to the coast, while Silas and Timothy remained behind.
15 Wadanda sun fitar da Bulus, sun kai shi har zuwa birnin Atina. Bulus ya ba su sako, su fada wa Sila da Timoti suyi hanzari su same shi.
Those escorting Paul took him as far as Athens, and then returned with instructions from Paul to Silas and Timothy that they should join him there as soon as possible.
16 Sa'anda Bulus yana jiran zuwan Sila da Timoti a Atina, ya yi fushi a ransa, da ya ga birnin cike da gumakai.
While Paul was waiting for them in Athens he was very troubled to see all the idolatry in the city.
17 Ya tattauna da Yahudawa a cikin majami'a tare da masu yin sujada ga Allah, da kuma wadanda yake samu a kowace rana, a kasuwa.
He debated in the synagogue with the Jews and those who worshiped God, as well as in the marketplace with those he happened to meet from day to day.
18 Amma wadan su Abikuriyawa da masana sun yi karo da shi. Wadansun su na cewa, ''Menene wannan sakaren ke cewa?'' Wadansu kuma sun ce, ''Da alama mai wa'azi ne na wasu alloli dabam,'' domin yana wa'azin Yesu da tashin sa daga matattu.
Some Epicurean and Stoic philosophers also argued with him. “What is he going on about?” they wondered. Others concluded, “He seems to be teaching about some foreign gods,” because he was speaking about Jesus and the resurrection.
19 Suka dauki Bulus zuwa Tudun Arasa, suna cewa, ''Ko za ka sanar mana da wannan sabuwar koyaswar taka?
So they took him to the Areopagus, and asked him, “Please tell us about this new teaching that you're promoting.
20 Abubbuwan da kake fadi, baki ne a gare mu. Muna so mu san ma'anar su.''
We're hearing from you things that sound odd to us, so we'd like to know what they mean.”
21 (Atiniyawa da bakin da ke cikinsu, suna ba da lokacin su ga fadin sabobbin abubuwa da sauraron su).
(All the Athenians, including foreigners who lived there, spent their whole time doing nothing except explaining or listening to something new.)
22 Bulus ya tsaya a tsakiyar Tudun Arasa ya ce, ''Ku mutanen Atiniya na lura masu kwazon addini ne ku.
Paul stood up right in the middle of the Areopagus and said, “People of Athens, I notice you are very religious about everything.
23 Na lura da abubuwan sujadar ku yayin da nake zagawa, amma na ga wani bagadi da rubutu a kansa mai cewa, ''Ga Allah wanda ba a sani ba.” Abin da kuke bauta wa cikin rashin sani, shi nake sanar maku.
As I was walking along, looking at your shrines, I found an altar that had the inscription, ‘To an Unknown God.’ This unknown God whom you worship is the one I'm describing to you.
24 Allahn da ya yi duniya da kome da ke cikinta, tun da ya ke shine Ubangijin sama da kasa, ba ya zama a haikalin da mutane suka gina da hannu.
The God who created the world and everything in it, the Lord of heaven and earth, doesn't live in temples we make.
25 Ba ya neman taimakon kowa, babu kuma wanda ya isa ya ba shi. Shine ke ba da rai, da numfashi da kowanne abu.
He doesn't need to be served by us as if he needed anything, since he is the source of all life for every living being.
26 Daga mutum daya ya hallici dukan al'umman duniya, ya rarraba, ya kuma sanya kowa a inda ya shirya masa.
From one man he made all the peoples who live on the earth, and decided beforehand when and where they should live.
27 Domin su nemi Allah ko za su iya kaiwa zuwa gareshi su same shi, ga shi kuwa ba ya nesa da kowannenmu.
God's purpose was that they should seek him, hoping they would reach out for him and find him—though he isn't far from any one of us.
28 A cikinsa muke rayuwa, muna walwala, kamar yadda wani daga cikin masananku yace, 'Mu 'ya'yansa ne'.
In him we live, move, and exist. Just as one of your own poets wrote, ‘We are his family.’
29 Idan mu 'ya'yan Allah ne, bai kamata mu danganta Allah da zinariya ko azurfa, ko kuma duwatsu da itatuwa da an sassaka ba.
Since we are his family we shouldn't think that God is like gold, or silver, or stone, shaped by human artistry and thinking.
30 Saboda haka ne, Allah ya kawar da kwanakin jahilci, amma ya ba da umarni kowa a ko'ina ya tuba.
God disregarded people's ignorance in the past, but now he commands everyone everywhere to repent.
31 Akwai ranar da ya shirya zai yi wa duniya shari'a cikin adalci, ta wurin mutumin da ya zaba. Allah ya nuna wannan mutumin, ta wurin ta da shi daga matattu''.
For he has set a time when he will rightly judge the world by the man he has appointed, and he proved to everyone that he is the one by raising him from the dead.”
32 Da mutanen Atina sun ji batun tashi daga matattu, wadansu suka yi wa Bulus ba'a; amma wadansu kuma sun ce, ''Za mu saurare ka kuma, a kan wannan maganar.''
Some of them laughed when they heard about the resurrection of the dead, while others said, “Please come back so we can hear more about this later.”
33 Bayan haka, Bulus ya bar su.
So Paul left them.
34 Amma wasu maza a cikinsu sun yarda da bisharar, sun ba da gaskiya, hade da Diyonisiyus dan Majalisar Tudun Arasa da wata mace mai suna Damaris, da wadansu tare da su.
A few men joined him and trusted in God, including Dionysius, a member of the Areopagus, as well as a woman called Damaris, and some others.