< Ayyukan Manzanni 17 >
1 Bayan sun wuce biranen Amfibolis da Aboloniya, sun iso birnin Tasalunika, in da akwai wata majami'ar Yahudawa a wurin.
Men de rejste igennem Amfipolis og Apollonia og kom til Thessalonika, hvor Jøderne havde en Synagoge.
2 Bulus, kamar yadda ya saba, ya nufi wurinsu, yana tattaunawa da su har Asabaci uku, daga cikin littattafai.
Og efter sin Sædvane gik Paulus ind til dem, og på tre Sabbater samtalede han med dem ud fra Skrifterne,
3 Bulus ya bude littattafai yana bayyana masu cewa, dole ne Almasihu ya sha wahala, ya kuma tashi daga matattu. Ya ce, ''Wannan Yesu kuwa da nake sanar maku, shine Almasihu''.
idet han udlagde og forklarede, at Kristus måtte lide og opstå fra de døde, og han sagde: "Denne Jesus, som jeg forkynder eder, han er Kristus."
4 Wasu Yahudawa sun yarda, sun bi Bulus da Sila, da wadansu Helenawa, da Shugabannin Mata da jama'a da yawa.
Og nogle af dem bleve overbeviste og sluttede sig til Paulus og Silas, og tillige en stor Mængde at de gudfrygtige Grækere og ikke få af de fornemste Kvinder.
5 Yahudawan da basu ba da gaskiya ba suka cika da kishi, suka dauki wadansu 'yan ta'adda daga cikin kasuwa, suka tada tarzoma cikin birnin, mutane da yawa na bin su. Sun kai hari a gidan Yason, da niyyar fitar da Bulus da Sila a gaban jama'a.
Men Jøderne bleve nidkære og toge med sig nogle slette Mennesker af Lediggængerne på Torvet, rejste et Opløb og oprørte Byen; og de stormede Jasons Hus og søgte efter dem for at føre dem ud til Folket.
6 Amma da ba su ga Bulus da Sila ba, suka ja Yason da wasu 'yan'uwa masu bi zuwa gaban mahukuntar birnin, suna cewa, ''Wadannan ne fa masu ta da zaune tsaye, gashi sun zo mana.
Men da de ikke fandt dem, trak de Jason og nogle Brødre for Byens Øvrighed og råbte: "Disse, som have bragt hele Verden i Oprør, ere også komne hid;
7 Wadannan mutane da Yason ya marabta, sun saba wa dokokin Kaisar; Suna cewa akwai wani sarki mai suna - Yesu.''
dem har Jason taget ind til sig; og alle disse handle imod Kejserens Befalinger og sige, at en anden er Konge, nemlig Jesus."
8 Da taron jama'a, da mahukuntan birnin suka ji haka, sun damu.
Og de satte Skræk i Mængden og Byens Øvrighed, som hørte det.
9 Bayan da sun amshi kudi daga wurin Yason da sauran 'yan'uwan, sai suka sake su.
Og denne lod Jason og de andre stille Borgen og løslod dem.
10 A wannan daren, 'yan'uwa masu bi suka fitar da Bulus da Sila, suka aike su garin Biriya. Da isar su can, su ka nufa majami'ar Yahudawa.
Men Brødrene sendte straks om Natten både Paulus og Silas bort til Berøa; og da de vare komne dertil, gik de ind i Jødernes Synagoge.
11 Mutanen Biriya daban suke da na Tasalunika, sun yarda da sakon Bulus da zuciya daya, suna kuma binciken littattafai kowace rana domin su tabbatar da sakon Bulus, ko gaskiya ne.
Men disse vare mere velsindede end de i Thessalonika, de modtoge Ordet med al Redebonhed og ransagede daglig Skrifterne, om disse Ting forholdt sig således.
12 Saboda haka mutane da yawa cikin su sun ba da gaskiya, tare da wadansu sannanun mata Helenawa da maza da yawa.
Så troede da mange af dem og ikke få af de fornemme græske Kvinder og Mænd.
13 Amma da Yahudawan Tasalunika suka ji cewa Bulus yana wa'azin kalmar Allah a Biriya, sun haura can, sun tada hankulan jama'a.
Men da Jøderne i Thessalonika fik at vide, at Guds Ord blev forkyndt af Paulus også i Berøa, kom de og vakte også der Røre og Bevægelse iblandt Skarerne.
14 Nan da nan, masu bi na Biriya sun dauki Bulus sun aika shi zuwa teku, an bar Sila da Timoti a Biriya tukuna.
Men da sendte Brødrene straks Paulus bort, for at han skulde drage til Havet; men både Silas og Timotheus bleve der tilbage.
15 Wadanda sun fitar da Bulus, sun kai shi har zuwa birnin Atina. Bulus ya ba su sako, su fada wa Sila da Timoti suyi hanzari su same shi.
Og de, som ledsagede Paulus, førte ham lige til Athen; og efter at have fået det Bud med til Silas og Timotheus, at de snarest muligt skulde komme til ham, droge de bort.
16 Sa'anda Bulus yana jiran zuwan Sila da Timoti a Atina, ya yi fushi a ransa, da ya ga birnin cike da gumakai.
Medens nu Paulus ventede på dem i Athen, harmedes hans Ånd i ham, da han så, at Byen var fuld af Afgudsbilleder.
17 Ya tattauna da Yahudawa a cikin majami'a tare da masu yin sujada ga Allah, da kuma wadanda yake samu a kowace rana, a kasuwa.
Derfor talte han i Synagogen med Jøderne og de gudfrygtige og på Torvet hver Dag til dem, som han traf på.
18 Amma wadan su Abikuriyawa da masana sun yi karo da shi. Wadansun su na cewa, ''Menene wannan sakaren ke cewa?'' Wadansu kuma sun ce, ''Da alama mai wa'azi ne na wasu alloli dabam,'' domin yana wa'azin Yesu da tashin sa daga matattu.
Men også nogle af de epikuræiske og stoiske Filosoffer indlode sig i Ordstrid med ham; og nogle sagde: ""Hvad vil denne Ordgyder sige?"" men andre: ""Han synes at være en Forkynder af fremmede Guddomme;"" fordi han forkyndte Evangeliet om Jesus og Opstandelsen.
19 Suka dauki Bulus zuwa Tudun Arasa, suna cewa, ''Ko za ka sanar mana da wannan sabuwar koyaswar taka?
Og de toge ham og førte ham op på Areopagus og sagde: ""Kunne vi få at vide, hvad dette er for en ny Lære, som du taler om?
20 Abubbuwan da kake fadi, baki ne a gare mu. Muna so mu san ma'anar su.''
Thi du bringer os nogle fremmede Ting for Øren; derfor ville vi vide, hvad dette skal betyde.""
21 (Atiniyawa da bakin da ke cikinsu, suna ba da lokacin su ga fadin sabobbin abubuwa da sauraron su).
Men alle Atheniensere og de fremmede, som opholdt sig der, gave sig ikke Stunder til andet end at fortælle eller høre nyt.
22 Bulus ya tsaya a tsakiyar Tudun Arasa ya ce, ''Ku mutanen Atiniya na lura masu kwazon addini ne ku.
Men Paulus stod frem midt på Areopagus og sagde: ""I athemiensiske Mænd! jeg ser, at I i alle Måder ere omhyggelige for eders Gudsdyrkelse.
23 Na lura da abubuwan sujadar ku yayin da nake zagawa, amma na ga wani bagadi da rubutu a kansa mai cewa, ''Ga Allah wanda ba a sani ba.” Abin da kuke bauta wa cikin rashin sani, shi nake sanar maku.
Thi da jeg gik omkring og betragtede eders Helligdommen, fandt jeg også et Alter, på hvilket der var skrevet: ""For en ukendt Gud."" Det, som I således dyrke uden at kende det, det forkynder jeg eder.
24 Allahn da ya yi duniya da kome da ke cikinta, tun da ya ke shine Ubangijin sama da kasa, ba ya zama a haikalin da mutane suka gina da hannu.
Gud, som har gjort Verden og alle Ting, som ere i den, han, som er Himmelens og Jordens Herre, bor ikke i Templer, gjorte med Hænder,
25 Ba ya neman taimakon kowa, babu kuma wanda ya isa ya ba shi. Shine ke ba da rai, da numfashi da kowanne abu.
han tjenes ikke heller af Menneskers Hænder som en, der trænger til noget, efterdi han selv giver alle Liv og Ånde og alle Ting.
26 Daga mutum daya ya hallici dukan al'umman duniya, ya rarraba, ya kuma sanya kowa a inda ya shirya masa.
Og han har gjort, at hvert Folk iblandt Mennesker bor ud af eet Blod på hele Jordens Flade, idet han fastsatte bestemte Tider og Grænserne for deres Bolig,
27 Domin su nemi Allah ko za su iya kaiwa zuwa gareshi su same shi, ga shi kuwa ba ya nesa da kowannenmu.
for at de skulde søge Gud, om de dog kunde føle sig frem og finde ham, skønt han er ikke langt fra hver enkelt af os;
28 A cikinsa muke rayuwa, muna walwala, kamar yadda wani daga cikin masananku yace, 'Mu 'ya'yansa ne'.
thi i ham leve og røres og ere vi, som også nogle af eders Digtere have sagt: Vi ere jo også hans Slægt.
29 Idan mu 'ya'yan Allah ne, bai kamata mu danganta Allah da zinariya ko azurfa, ko kuma duwatsu da itatuwa da an sassaka ba.
Efterdi vi da ere Guds Slægt, bør vi ikke mene, at Guddommen er lig Guld eller Sølv eller Sten, formet ved Menneskers Kunst og Opfindsomhed.
30 Saboda haka ne, Allah ya kawar da kwanakin jahilci, amma ya ba da umarni kowa a ko'ina ya tuba.
Efter at Gud altså har båret over med disse Vankundighedens Tider, byder han nu Menneskene at de alle og alle Vegne skulle omvende sig.
31 Akwai ranar da ya shirya zai yi wa duniya shari'a cikin adalci, ta wurin mutumin da ya zaba. Allah ya nuna wannan mutumin, ta wurin ta da shi daga matattu''.
Thi han har fastsat en Dag, på hvilken han vil dømme Jorderige med Retfærdighed ved en Mand, som han har beskikket dertil, og dette har han bevist for alle ved at oprejse ham fra de døde."
32 Da mutanen Atina sun ji batun tashi daga matattu, wadansu suka yi wa Bulus ba'a; amma wadansu kuma sun ce, ''Za mu saurare ka kuma, a kan wannan maganar.''
Men da de hørte om de dødes Opstandelse, spottede nogle; men andre sagde: "Ville atter høre dig om dette."
33 Bayan haka, Bulus ya bar su.
Således gik Paulus ud fra dem.
34 Amma wasu maza a cikinsu sun yarda da bisharar, sun ba da gaskiya, hade da Diyonisiyus dan Majalisar Tudun Arasa da wata mace mai suna Damaris, da wadansu tare da su.
Men nogle Mænd holdt sig til ham og troede; iblandt hvilke også var Areopagiten Dionysius og en Kvinde ved Navn Damaris og andre med dem.