< Ayyukan Manzanni 16 >
1 Bulus ya kuma isa Darbe da Listira, in da akwai wani almajiri mai suna Timoti a wurin, dan wata Bayahudiya wadda ta ba da gaskiya; ubansa kuwa Baheline ne.
He came then (both *no*) to Derbe and (to *no*) Lystra. And behold a disciple certain was there, named Timothy, [the] son of a woman (certain *k*) Jewish believing, father however a Greek;
2 Ana maganar kirki a kansa ta bakin 'yan'uwa da ke Listira da Ikoniyan.
who was well spoken of by the in Lystra and Iconium brothers.
3 Bulus ya yi wa Timoti kaciya, domin yana so su yi tafiya tare, domin kuma saboda Yahudawan da ke wurin, sun san cewa ubansa Baheline ne.
This one wanted Paul with him to go forth, and having taken he circumcised him on account of the Jews those being in the parts those; they knew for all that a Greek (the father *N(k)O*) of him was.
4 Suna shiga cikin biranen, suna yi wa iklisiyoyi gargadi da su yi biyayya da umurnan da Manzanni da dattawa suka rubuta a Urushalima.
While then they were passing through the cities, they were delivering to them to keep the decrees which [were] decided on by the apostles and (of the *k*) elders who [were] in Jerusalem.
5 Bangaskiyar iklisiyoyi kuwa ta karu, ana kuma samun karuwa na wadanda suke ba da gaskiya kowace rana.
The indeed therefore churches were strengthened in the faith and were increasing in number every day.
6 Bulus da abokan aikin sa sun shiga cikin lardin Firigiya da Galatiya, tun da Ruhu Mai Tsarki ya hana su wa'azin kalmar a cikin yankin Asiya.
(they passed through *N(k)O*) then Phrygia and (the *k*) Galatian region having been forbidden by the Holy Spirit to speak the word in Asia,
7 Sun zo kusa da Misiya, da nufin shiga cikin Bitiniya, Ruhun Yesu ya hana su.
having come (then *no*) down to Mysia they were attempting (into *N(k)O*) Bithynia (to go, *N(k)O*) and not did allow them the Spirit (of Jesus. *NO*)
8 Da suka ratse ta cikin Misiya, sai suka shiga birnin Taruwasa.
having passed by then Mysia they came down to Troas.
9 Bulus ya ga wahayi cikin dare, wani mutumin Makidoniya na kiransa, yana cewa. ''Ka zo Makidoniya ka taimake mu''.
And a vision during the night to Paul appeared: A man of Macedonia certain was already standing (and *no*) beseeching him and saying; Having passed over into Macedonia do help us.
10 Bulus, da ganin haka, ya kama hanya zuwa Makidoniya, da tunanin Allah ne ya ke so su kai wa mutanen Makidoniya bishara.
When now the vision he had seen, immediately we sought to go forth to (*k*) Macedonia concluding that he has called us (God *N(K)O*) to evangelise to them.
11 Da barin Taruwasa, Bulus da kungiyarsa sun shiga jirgin ruwa zuwa Samutaraki, da gari ya waye kuma sun tafi Niyafolis;
Having sailed (then *N(K)O*) from (*k*) Troas we made a straight course to Samothrace, (and *N(k)O*) the following day to Nea Polis,
12 Daga nan kuma suka tafi Filibi, birni na Makidoniya, mai muhimmanci ne a yankin Roma, in da mun yi zango kwanaki da dama.
(and from there and from there *N(k)O*) to Philippi, which is ([the] leading [city] *N(k)O*) (of the *ko*) district (*NK*) of Macedonia [the] city, [and Roman] colony. We were now in (this *NK(o)*) city staying days some.
13 Ranar Asabaci mun je kofar gari, gefen rafi, da tunanin samun wurin addu'a. Mun zauna mun kuma yi magana da matan da sun taru a wurin.
On the then day of the Sabbaths we went forth outside the (gate *N(K)O*) by a river where (we were accustomed *N(K)O*) (prayer *N(k)O*) to have, And having sat down we were speaking to those having gathered women.
14 Wata mace mai suna Lidiya, 'yar kasuwa ce a birnin Tiyatira, mai bautar Allah ce, ta saurare mu. Ubangiji ya bude zuciyarta, ta mai da hankali ga maganar da Bulus ke fadi.
And a certain woman named Lydia, a seller of purple of [the] city of Thyatira worshiping God, was listening of whom the Lord opened the heart to attend to the [things] being spoken by Paul.
15 Sa'anda da aka yi mata Baftisma tare da mutanen gidanta, ta ce da mu, “Idan kun dauke ni mai bautar Allah, ku zo gidana ku zauna.” Sai ta rinjaye mu.
When then she was baptized and the house of her, she begged saying; If you have judged me faithful to the Lord to be, having entered into the house of mine (do remain; *N(k)O*) And she persuaded us.
16 A daidai wannan lokaci, muna tafiya wurin addu'a, wata yarinya mai ruhun duba ta hadu da mu. Iyayen gijinta na arziki da ita sosai.
It happened now going of us to (the *no*) [place of] prayer, a girl certain having a spirit (Python meeting by *N(k)O*) us, who gain much was bringing the masters of her by fortune-telling.
17 Tana bin Bulus, tare da mu, tana fadi da murya mai karfi cewa, ''Wadannan mutanen, bayin Allah mafi daukaka ne, suna sanar maku hanyar ceto ne''.
She (having followed *N(k)O*) after Paul and us was crying out saying; These men servants of the God Most High are, who proclaim (to you *N(K)O*) [the] way of salvation.
18 Ta dauki kwanaki tana haka. Amma Bulus ya yi fushi da ita ainun, ya juya ya umarci ruhun, ya ce, ''Na umarce ka, ka rabu da ita a cikin sunan Yesu Almasihu''. Ruhun ya yi biyayya ya rabu da ita nan take.
This then she was continuing for many days. Having been distressed then (*k*) Paul and having turned to the spirit he said; I command you in (the *k*) name of Jesus Christ to come out from her. And it came out on [the] same hour.
19 Da iyayengijinta suka ga cewa hanyar shigar kudinsu ta toshe, sai suka kama Bulus da Sila, suka ja su cikin kasuwa suka kai su gaban mahunkunta.
Having seen now the masters of her that was gone the hope of the profit of them, having taken hold of Paul and Silas they dragged [them] into the marketplace before the rulers,
20 Da suka kai su Kotu, suka ce, ''Wadannan mutane Yahudawa ne, suna kawo tashin hankali a birninmu.
and having brought up them to the magistrates they said; These men exceedingly trouble of us the city Jews being;
21 Suna koyar da abubuwa da ba su karbuwa a gare mu, balle mu aikata, a matsayinmu na Romawa.”
and preach customs that not it is lawful for us to accept nor to practice Romans being.
22 Sai jama'a gaba daya sun tayar wa Bulus da Sila; alkalan kuma sun yage rigunansu, sun ba da umarni a duki Bulus da Sila da bulala.
And rose up together the crowd against them, and the magistrates having torn off of them the garments were commanding to beat with rods;
23 Bayan dukan, an jefa su Bulus a kurkuku, an ba mai tsaron kurkukun umurni ya kulle su da kyau, kada su gudu.
Many (then *NK(o)*) having laid on them blows they cast [them] into prison having charged the to jailer strictly to keep them;
24 Shi kuma ya yi hakanan, ya sa masu sarkoki a kafafun su, kamar yadda aka umurce shi.
who an order such (having received *N(k)O*) threw them into the inner prison and the feet fastened of them in the stocks.
25 Da tsakar dare, Bulus da Sila suna yin adu'a, su na raira wakoki ga Allah, sauran 'yan sarkar su na jin su.
Toward now midnight Paul and Silas praying they were singing praises to God; Were listening now to them the prisoners.
26 Nan da nan sai ga wata girgizar kasa, wadda ta sa ginshikan kurkukun sun kadu, nan da nan kofofin kurkukun sun bude, 'yan sarka kuma, sarkokin su sun karkatse.
Suddenly then earthquake there was a great so that shaking the foundations of the prison house; were opened (then *N(k)O*) immediately the doors all, and of all the chains were loosed.
27 Mai tsaron kurkukun ya tashi daga barci ya ga kofofin kurkukun a bude, ya zaro takobi, zai kashe kan sa, a tunanin sa, 'yan sarkar sun gudu.
Awoken then having been the jailer and was seeing having opened the doors of the prison, having drawn (*no*) [his] sword he was about himself to execute supposing to have escaped the prisoners.
28 Amma Bulus ya ta da murya da karfi, ya ce, ''kada kayi wa kanka barna, domin dukan mu muna nan''.
Called out however in a loud voice Paul saying; Not may do to yourself harm; all for we are here.
29 Mai tsaron kurkukun ya aika a kawo fitila, ya shiga ciki a gurguje da rawan jiki, ya fadi a gaban Bulus da Sila,
Having called for now lights he rushed in and terrified having become he fell down before Paul and Silas,
30 ya fitar da su waje ya ce, ''Shugabanni, me ya kamata in yi domin in tsira?''
And having brought them out he was saying; Sirs, what of me is necessary to do that I may be saved?
31 Sun ce masa, ''ka ba da gaskiya ga Yesu Ubangiji, da kai da gidan ka, za ku sami tsira''.
And they said; do believe on the Lord Jesus (Christ *K*) and will be saved you yourself and the household of you.
32 Bulus da Sila suka fada masa maganar Ubangiji, tare da iyalinsa.
And they spoke to him the word of the (Lord *NK(O)*) (along with *N(k)O*) all those in the house of him.
33 Shi mai tsaron kurkukun ya dauke su cikin daren, ya wanke raunukansu, an kuma yi masa Baftisma nan da nan tare da iyalinsa.
And having taken them in that [very] hour of the night he washed [them] from the wounds, and he was baptized he himself and the [household] of him (all *NK(o)*) immediately.
34 Ya kai Bulus da Sila gidansa, ya ba su abinci. Murna ta cika gidan mai tsaron kurkukun, domin iyalin sa duka sun ba da gaskiya ga Allah.
Having brought then them into the house (of him *ko*) he laid a table [for them] and (rejoiced *NK(o)*) with all [his] household having believed in God.
35 Da gari ya waye, alkalai sun ba da sako a saki Bulus da Sila.
When day then having come sent the magistrates the officers saying; do release the men those.
36 Mai tsaron kurkukun kuwa ya sanar wa Bulus wannan magana ta alkalan, saboda haka ya ce wa Bulus, ''Ku tafi cikin salama''.
Reported then the jailer words these to Paul that Have sent the captains that you may be let go; Now therefore having gone out do depart in peace.
37 Amma Bulus ya ce masu, “Sun yi mana duka a fili a gaban mutane mu da muke Romawa, ba a kashe mu ba, sun kuma sa mu a kurkuku; suna koran mu a asirce? Su zo da kansu su fitar da mu.
But Paul was saying to them; Having beaten us publicly uncondemned men Romans being, they cast [us] into prison, and now secretly us do they throw out? No indeed! Instead having come themselves us they should bring out.
38 Masu tsaron kurkuku sun mayar da maganar Bulus ga alkalan, wanda ya sa sun firgita, da jin cewa Bulus da Sila Romawa ne.
(Reported *N(k)O*) then to the magistrates the officers declarations these; (and *k*) They were afraid (then *no*) having heard that Romans they are,
39 Alkalai da kansu sun zo sun roki Bulus da Sila; da suka fitar da su daga kurkukun, sun ce wa Bulus da Sila su bar birnin.
And having come they appealed to them and having brought [them] out they were asking [them] (to go out *N(k)O*) (of *no*) the city.
40 Da hakanan ne Bulus da Sila suka fita daga kurkuku, sun je gidan Lidiya. Da Bulus da Sila sun ga 'yan'uwa, sun karfafa su, sa'annan suka bar birnin.
Having gone forth then (out of *N(k)O*) the prison they came (to *N(k)O*) Lydia; and having seen [them] they exhorted the brothers (them *k*) and departed.