< Ayyukan Manzanni 14 >

1 A lokacin da Bulus da Barnaba sun shiga garin Ikoniya suka shiga majami'an Yahudawa suka yi wa'azi yadda har mutane da yawa daga cikin Yahudawa da Hellinawa suka ba da gaskiya.
And it came to pass in Iconium, that they went together into the synagogue of the Jews, and so spoke that a great multitude of the Jews and Greeks believed.
2 Amma Yahudawa da basu yi biyayya ba, suka zuga al'umman har suka yi fushi da 'yan'uwan.
But the unbelieving Jews excited and embittered the minds of the Gentiles against the brethren.
3 Suka zauna a wurin na tsawon lokaci, suna yni maganarsu gabagadi da ikon Ubangiji, yana kuma shaidar sakon alherinsa. Ya yi wannan ta wurin alamu da al'ajibai ta hannun Bulus da Barnaba.
Therefore, they continued a long time, and spoke boldly in the Lord, who gave testimony to the word of his grace, by granting signs and wonders to be done by their hands.
4 Saboda haka mutanen garin sun rabu: wadansun su suka bi ra'ayin Yahudawa, wasu kuwa sun bi manzannin.
But the multitude of the city were divided; and some were with the Jews, and some with the apostles.
5 Al'umman garin da Yahudawa sun nemi jan hankali shugabanninsu, don su wulakanta Bulus da Barnaba, su jajjefe su,
But when there was a violent purpose on the part of the Gentiles and of the Jews, with their rulers, to outrage and to stone them,
6 da suka gane haka suka gudu zuwa biranen Likoniya, Listira da Darbe, da garuruwa wadanda ke kewaye da su,
being aware of it, they fled to the cities of Lycaonia, Lystra, and Derbe, and to the region round about,
7 a can suka yi wa'azin bishara.
and there they preached the gospel.
8 A Listira akwai wani wanda ke zaune bai taba tashi da kafafunsa ba, don shi gurgu ne tun daga haihuwa.
And there was a certain man in Lystra, without strength in his feet, who sat, for he was a cripple from his mother’s womb, and had never walked.
9 Wannan mutumin ya ji Bulus yana magana. Bulus ya kafa masa ido, ya gane mutumin na da bangaskiya da za a warkar da shi. Sai ya ce masa da murya mai karfi, “Tashi ka tsaya akan kafafunka”
This man heard Paul speak, who, looking earnestly on him, and seeing that he had faith to be saved,
10 Sai mutumin ya yi tsalle ya fara tafiya da kafafunsa, yana yawo.
said, with a loud voice: Stand erect upon your feet. And he leaped and walked.
11 Da jama'an garin sun ga abin da Bulus ya yi, suka tada muryarsu suna cewa da Likoniyanci, “Ai alloli sun ziyarce mu daga sama, da kamanin mutane.”
When the multitude saw what Paul had done, they lifted up their voice, and said, in the Lycaonian language: The Gods have come down to us in the likeness of men.
12 Suna kiran Barnaba da sunan “Zafsa,” Bulus kuwa suka kira shi da sunan “Hamisa” domin shine yafi yin magana.
And they called Barnabas, Jupiter, and Paul, Mercury, for he was the chief speaker.
13 Sai firist din zafsa wanda dakin yin masa sujada na kofar birni; ya kawo bijimai biyu da furannin da aka saka su kamar gammo; shi da jama'arsa suna so su yi masa hadaya.
Then the priest of Jupiter, whose temple was before the city, having brought bulls and garlands to the entrance, intended to offer sacrifice, with the multitudes.
14 Amma da manzannin, wato Barnaba da Bulus, su ka ji labarin, suka yage rigunansu, suka hanzarta zuwa gun taron mutanen.
But when the apostles, Barnabas and Paul, heard of it, they rent their clothes, and ran in among the multitude, crying out,
15 Suna ta cewa, “Kuji! Ku mutane don me kuke wannan abin? Mu fa mutane ne kamarku. Mun kawo maku labari mai dadi ne, da cewa, ku rabu da abubuwa marar amfani, ku koma ga Allah mai rai, wanda ya hallici sama da kasa da teku da dukan abubuwa da ke cikinsu.
and saying: Men, why are you doing these things? We also are human beings, with passions like your own, and we preach the gospel to you, that you may turn from these vanities to the living God, who made the heaven, and the earth, and the sea, and all things that are in them;
16 A da dai ya bar mutane su yi abinda suka ga dama.
who, in past generations, permitted all the nations to walk in their own ways;
17 Duk da haka, bai bar kansa ba tare da shaida ba, don yana bada abubuwa masu kyau, yana ba ku ruwan sama, lokatai masu albarka, ya cika ranku da abinci da farin ciki.”
and yet he did not leave himself without testimony, doing good, and giving you rain from heaven, and fruitful seasons, filling your hearts with food and gladness.
18 Duk da wadannan kalmomin da kyar, Bulus da Barnaba suka iya tsayar da su daga yi masu hadaya.
And with these words they hardly restrained the multitudes from offering sacrifice to them.
19 Amma wasu Yahudawa daga Antakiya da wasunsu daga Ikoniya suka rinjayi tarun jama'ar. Suka jajjefi Bulus suka ja shi zuwa wajen garin, suna ganin kamar ya mutu.
Then came thither, from Antioch and Iconium, Jews, who persuaded the multitudes; and having stoned Paul, they dragged him out of the city, supposing that he was dead.
20 Duk da haka da almajirai suka kewaye shi a tsaitsaye, sai ya tashi ya koma cikin garin. Washegari, ya tafi Darba tare Barnaba.
But while the disciples were standing around him, he arose, and went into the city. And on the next day, he departed with Barnabas to Derbe;
21 Bayan sun yi wa'azin bishara a wannan birnin suka kuma sami almajirai da yawa, suka dawo Listira, da Ikoniya da Antikiya.
and when they had preached the gospel to that city, and had made many disciples, they returned to Lystra, and to Iconium, and to Antioch,
22 Suna karfafa zuciyar almajiran su rike bangaskiyarsu, su ci gaba da ita, suna ce masu, “Ta wurin jimrewa mai yawa zamu shiga mulkin Allah, don haka dole ne mu sha wahala.”
strengthening the souls of the disciples, exhorting them to continue in the faith, and saying, that through many afflictions we mast enter the kingdom of God.
23 Da suka zabar masu dattawa a kowace iklisiya, sai suka yi addu'oi da azumi, suka mika su ga Ubangiji, ga wanda suka gaskanta a gareshi.
And when they had appointed elders for them in every church, with prayer and fasting, they commended them to the Lord, on whom they believed.
24 Sa'annan sun bi ta Bisidiya suka kai Bamfiliya.
And having passed through Pisidia, they came into Pamphylia;
25 Da suka yi maganarsu a Biriya, sun wuce zuwa har Italiya.
and when they had preached the word in Perga, they went down to Attalia:
26 Ta jirgin ruwa zuwa Antakiya, a nan ne aka mika su ga alherin Allah don aikin da suka gama a yanzu.
thence they sailed to Antioch, from which place they had been commended to the grace of God, for the work which they had accomplished.
27 Da isowarsu Antakiya sun tara 'yan iklisiya a wuri daya, sun ba da labarin dukan abin da Allah ya yi ta wurinsu. Da yadda Ya bude kofa a wurin al'ummai ta bangaskiya.
And having come and called together the church, they reported all that God had done with them, and that he had opened the door of faith to the Gentiles.
28 Sun zauna tare da almajiran na tsawon lokaci.
And they continued a long time with the disciples.

< Ayyukan Manzanni 14 >