< Ayyukan Manzanni 13 >
1 A cikin iklisiyar da take Antakiya, akwai annabawa da malamai. Sune su Barnabas, Saminu (wadda ake kira Baki) da Lukiya Bakurame da Manayin (wanda aka yi renon su tare da sarki Hiridus mai mulki) da Shawulu.
Now in the congregation that was in Antioch there were certain prophets and teachers: Barnabas, Simeon (the one called Niger), Lucius the Cyrenian, Manaen (who had been brought up with Herod the tetrarch), and Saul.
2 Sa'adda suke bauta wa Allah tare da azumi, sai Ruhu Mai Tsarki ya ce, “Ku kebe mani Barnaba da Shawulu domin aikin da na kiraye su”.
As they were ministering to the Lord and fasting, the Holy Spirit said, “Set apart to me Barnabas and Saul for the work to which I have called them!”
3 Bayan taron sun yi addu'a da azumi, sai suka sa masu hannu, su suka sallame su.
Then, having fasted and prayed and laid their hands on them, they sent them off.
4 Sai Shawulu da Barnabas suka yi biyayya da Ruhu Mai Tsarki suka tafi Sulukiya; daga nan suka ketare zuwa tsibirin Kuburus.
So, having been sent out by the Holy Spirit, they went down to Seleucia; and from there they sailed to Cyprus.
5 Sa'adda suke garin Salami, suka koyar da maganar Ubangiji a majami'un Yahudawa, suna kuma tare da Yahaya Markus mai taimakonsu.
And upon arriving in Salamis, they started proclaiming the Word of God in the synagogues of the Jews (also they had John as assistant).
6 Bayan sun zaga tsibirin duka har Bafusa, nan suka iske wani Bayahude mai suna Bar-yeshua mai tsafi kuma annabin karya.
Now when they had gone through the island to Paphos, they found a certain sorcerer, a false prophet, a Jew named Bar-Jesus,
7 Wannan mai tsafin wanda ke tare da Makaddas, shi Sarjus Bulus mutum mai basira ne. Wannan kuwa ya kira Shawulu da Barnaba domin yana so ya ji maganar Allah.
who was with the proconsul, Sergius Paulus, an intelligent man. This man summoned Barnabas and Saul, really wanting to hear the Word of God.
8 Amma Elimas “mai tsafi” (fasarar sunansa kenan) ya yi adawa da su; yana so ya baudar da Makaddashin daga bangaskiya.
But the sorcerer Elymas (for so his name is translated) opposed them, seeking to turn the proconsul away from the faith.
9 Amma Shawulu wanda ake ce da shi Bulus yana cike da Ruhu Mai Tsarki ya kafa masa ido.
Then Saul, also called Paul, filled with Holy Spirit and looking intently at him,
10 Sai ya ce, “Kai dan iblis, kana cike da kowace irin yaudara da mugunta. Kai abokin gabar kowanne irin adalci ne. Ba za ka daina karkata mikakkakun hanyoyin Ubangiji ba?
said: “O full of all deceit and all trickery, son of a devil, enemy of all righteousness! Will you not stop perverting the straight ways of the Lord?
11 Yanzu ga hannun Ubangiji bisa kanka, zaka zama makaho. Ba za ka ga rana ba nan da dan lokaci.” Nan take kuwa sai wani hazo da duhu suka rufe shi ya fara yawo yana neman mutane su yi masa jagora.
Well now, the Lord's hand is against you and you will be blind, not seeing the sun until next season!” Immediately mist and darkness engulfed him, and he started going around looking for someone to lead him by the hand.
12 Bayan da Makaddashin ya ga abin da ya faru ya ba da gaskiya saboda ya yi mamakin koyarwa game da Ubangiji.
Then the proconsul believed, when he saw what had happened, being astonished at the teaching of the Lord.
13 Bulus da abokansa suka shirya suka ketare a jirgin ruwa daga Bafusa zuwa Firjiya a Bamfiliya. Amma Yahaya ya bar su ya koma Urushalima.
Then Paul and his party set sail from Paphos and came to Perga in Pamphilia (here John left them and returned to Jerusalem).
14 Bulus da abokansa suka tafi daga Firjiya zuwa Antakiya na kasar Bisidiya. Nan suka shiga majami'a ran Asabaci suka zauna.
Going on from Perga they arrived in Antioch of Pisidia; and entering the synagogue on the Sabbath day, they sat down.
15 Bayan karatun dokoki da annabawa, shugabanin iklisiyar suka tura sako cewa, “'Yan'uwa, idan kuna da wani sakon karfafawa ga jama'a ku fadi.”
After the reading of the Law and the Prophets, the synagogue leaders sent to them, saying, “Men, brothers, if you have a word of encouragement for the people, do speak.”
16 Bulus kuwa ya tashi ya yi alama da hannunsa ya ce, “Mutanen Isra'ila da ku wadanda kuke girmama Allah, ku ji.
So standing up and motioning with his hand, Paul said: “Men of Israel and you who fear God, listen.
17 Allahn Isar'ila ya zabi kakkaninmu ya kuma ribabbanya su sa'adda suke kasar Masar da kuma madaukakin iko ya fito da su daga cikinta.
The God of this people chose our fathers, and prospered the people during their sojourn in the land of Egypt, and brought them out of it with an uplifted arm.
18 Ya yi hakuri da su a jeji har na tsawon shekara arba'in.
For a period of about forty years He put up with them in the wilderness.
19 Bayan ya hallaka kasashe bakwai a kasar Kan'ana, ya ba kakkaninmu kasar nan gado.
And when He had destroyed seven nations in the land of Canaan, He gave them possession of their land.
20 Duk wadanan abubuwan sun faru shekaru dari hudu da hamsin da suka wuce. Bayan wadannan, Allah ya ba su alkalai har sai da annabi Sama'ila ya zo.
After these things, He gave judges for about four hundred and fifty years, until Samuel the prophet.
21 Sai jama'a suka roka a ba su sarki, Allah kuwa ya ba su Saul dan Kish, mutumin kabilar Binyamin ya zama sarki har na tsawon shekara arba'in.
And then they asked for a king, and God gave them Saul, a son of Kish, a man of the tribe of Benjamin, for forty years.
22 Allah kuwa ya cire shi daga kan kujerar sarauta, ya daga Dauda ya zama sarkinsu. A kan Dauda ne Allah ya ce, 'Na sami Dauda dan Yessi, mutumin da zuciyata ke so; zai yi duk abin da nake so'.
And removing him He raised up for them David as king, about whom He gave witness and said, ‘I have found David son of Jesse a man after my heart, who will do all my will.’
23 Daga zuriyar mutumin nan Allah ya fito da mai ceto, Yesu, kamar yadda aka alkawarta zai yi.
God, from this man's seed, according to promise, has brought Salvation to Israel,
24 Wannan ya faru kafin Yesu ya zo, Yahaya ya yi shelar baftimar tuba ga jamma'ar Isra'ila.
John having heralded beforehand, in advance of His coming, a baptism of repentance to Israel.
25 Sa'adda Yahaya ya gama aikin sa, sai ya ce, 'Wanene ni a tsamanin ku? Ba nine shi ba. Amma ku saurara, akwai wani mai zuwa bayana wanda maballin takalminsa ban isa in kwance ba.'
Well, as John was fulfilling his course, he said: ‘Whom do you suppose me to be? No I am not—but indeed He comes after me, the sandals of whose feet I am not worthy to untie.’
26 Yan'uwa 'ya'ya daga zuriyar Ibrahim, da wadanda ke bautar Allah a cikinku, saboda mune aka turo sakon ceto.
“Men, brothers, sons of the stock of Abraham, and those among you who fear God: to you the word of this salvation has been sent.
27 Saboda wadanda ke zaune cikin Urushalima, da masu mulkinsu, ba su gane shi ba, kuma sun cika fadin annabawa da a ke karantawa kowace ranar Asabaci ta wurin kashe shi.
The Jerusalem dwellers and their rulers, understanding neither Him nor the voices of the prophets that are read every Sabbath, fulfilled them by condemning Him.
28 Duk da cewa ba su sami dalilin mutuwa a kansa ba, suka roki Bilatus ya kashe shi.
Though they found no cause for death, they asked Pilate to have Him executed.
29 Bayan sun gama duk abin da aka rubuta game da shi, sai suka sauke shi daga giciye suka sa shi a cikin kabari.
When they had fulfilled all things that were written about Him, they took Him down from the cross and placed Him in a tomb.
30 Amma Allah ya tashe shi daga matattu.
But God raised Him from the dead;
31 Mutanen da suka zo tare da shi daga Galili da Urushalima kuwa suka yi ta ganinsa har kwanaki da yawa. Wadanan mutane kuma sune shaidunsa ga jama'a a yanzu.
and for many days He was seen by those who came up with Him from Galilee to Jerusalem, who are His witnesses to the people.
32 Mun kawo maku labari mai dadi game da alkawaran da aka yi wa kakkaninmu.
“Yes we proclaim to you the good news: the promise that was made to the fathers,
33 Ubangiji ya bar mana alkawaran. Don haka ya ta da Yesu daga matattu. Kamar yadda ya ke a littafin zabura ta biyu: ''Kai da na ne yau na zama mahaifinka.''
God has fulfilled the same to us, their children, when He raised up Jesus; as also it stands written in the second Psalm: ‘You are my Son, today I have begotten you.’
34 Kuma dalilin tayar da shi daga matattu shine saboda kada jikinsa ya rube, ya yi magana kamar haka: ''Zan baku albarkun Dauda masu tsarki tabatattu.''
And that He raised Him from the dead, no longer to return to corruption, He has spoken thus, ‘I will give you the holy things guaranteed to David.’
35 Wannan shine dalilin da ya yi magana kuma a wata Zabura, 'Ba za ka bar Mai Tsarkinka ya rube ba.'
Further, it is stated elsewhere, ‘You will not allow your Holy One to see decay.’
36 Bayan Dawuda ya yi wa Allah bauta a cikin zuciyarsa da kuma abin da Allah yake so, ya mutu, aka binne shi tare da kakkaninsa, ya kuma ruba,
Now David, after he had served his own generation by the will of God, fell asleep, was buried with his fathers, and saw decay;
37 amma wanda Allah ya tayar bai ga ruba ba.
but the One whom God raised up did not see decay.
38 'Yan'uwa, ku sani cewa ta wurin mutumin nan aka yi maku wa'azin gafarar zunubai.
Therefore, let it be known to you, men, brothers, that through this One forgiveness of sins is proclaimed to you;
39 Ta wurinsa ne duk wanda ya ba da gaskiya zai kubuta daga dukan abin da dokar Musa bata 'yantar da ku a kai ba.
and by Him everyone who believes is justified from everything you could not be justified from by the Law of Moses.
40 Saboda haka ku yi hankali da abubuwan da annabawa suka fada kada su faru a kanku:
So take care, lest there come upon you that which has been spoken in the prophets:
41 'Ku masu reni, za ku rude don mamaki, ku kuma shude; saboda ina aiki a cikin kwananakinku, aikin da ba za ku yarda ba ko da wani ya gaya maku.”
‘Look you despisers, marvel and perish! For I am working a work in your days to which you will not give credence, even if someone were to explain it in detail to you.’”
42 Da Bulus da Barnaba suna fita kenan, sai jama'a suka rokesu, su sake yin irin wannan magana ranar Assabaci mai zuwa.
Now as the Jews were going out of the synagogue, the Gentiles implored repeatedly that these words might be spoken to them the next Sabbath.
43 Bayan da sujadar ta kare, Yahudawa da yawa da kuma wadanda suka shiga addinin Yahudanci suka bi Bulus da Barnaba, sai suka gargade su da su cigaba da aikin alherin Allah.
The synagogue service having been dismissed, many of the Jews and the devout proselytes followed Paul and Barnabas, who started addressing them, urging them to continue in the grace of God.
44 Da Asabaci ta kewayo, kusan dukan garin suka taru domin su ji maganar Ubangiji.
Well the next Sabbath almost the whole city was gathered to hear the Word of God.
45 Sa'adda Yahudawa suka ga taron jama'a, sai suka cika da kishi suna karyata abubuwan da Bulus ya fada suka kuma aibata shi.
But when the Jews saw the crowds, they were filled with envy and started speaking against the things said by Paul, contradicting and blaspheming.
46 Amma Bulus da Barnaba sun yi magana gabagadi suka ce, “Dole ne a fara fada maku maganar Allah. Amma da yake kun ture ta, kun nuna baku cancanci rai madawwami ba soboda haka zamu juya ga al'ummai. (aiōnios )
But Paul and Barnabas speaking boldly said: “It was necessary that God's Word should be spoken to you first. But since you reject it, and judge yourselves unworthy of eternal life, now we are being turned to the Gentiles. (aiōnios )
47 Don haka Ubangiji ya umarce mu, cewa, 'Na sa ku haske ga al'ummai, saboda ku kawo ceto ga iyakar duniya.'”
Because that is just how the Lord has commanded us: ‘I have set you to be a light for ethnic nations, that you should be for salvation up to the last place on earth.’”
48 Da al'ummai suka ji haka, sai suka yi murna suka kuma yabi kalmar Ubangiji. Dukan wadanda aka kaddarawa samin rai madawwami suka tuba. (aiōnios )
Now upon hearing this, the Gentiles rejoiced and glorified the Word of the Lord; and as many as had been appointed to eternal live believed. (aiōnios )
49 Kalmar Ubangiji kuwa ta bazu a kowanne bangaren yankin.
Well the Word of the Lord was being spread throughout all the region.
50 Amma Yahudawan suka zuga wadansu mata masu sujada, masu daraja da kuma shugabannin mazan garin. Wannan ya tayar da tsanani ga Bulus da Barnaba har suka fitar da su daga iyakar garinsu.
But the Jews stirred up the devout and prominent women and the chief men of the city, and raised up a persecution against Paul and Barnabas, and expelled them from their borders.
51 Amma Bulus da Barnaba suka kade masu kurar kafarsu. Suka tafi garin Ikoniya.
So they shook off the dust from their feet against them, and went to Iconium.
52 Amma almajiran suka cika da farin ciki da kuma Ruhu Mai Tsarki.
But the disciples were filled with joy and with Holy Spirit.