< Ayyukan Manzanni 12 >
1 A lokacin nan Sarki Hiridus ya sa wa wasu masu bi hannu domin ya musguna masu.
Now at the same time, king Herod extended his hand, in order to afflict some from the Church.
2 Ya kashe Yakubu dan'uwan Yahaya da takobi.
Then he killed James, the brother of John, with the sword.
3 Bayan da ya ga hakan ya gamshi Yahudawa, sai ya kama Bitrus ma.
And seeing that it pleased the Jews, he set out next to apprehend Peter also. Now it was the days of Unleavened Bread.
4 Bayan ya kama shi, sai ya tsare shi a kurkuku ya kuwa sa sojoji hudu su dinga tsaron sa; yana niyyar kawo shi gaban mutanen a bayan Idin katarewa.
So when he had apprehended him, he sent him into prison, handing him over into the custody of four groups of four soldiers, intending to produce him to the people after the Passover.
5 To, Bitrus na tsare a kurkuku, amma 'yan'uwa na iklisiya suna yin addu'a ga Allah sosai domin sa.
And so Peter was detained in prison. But prayers were being made without ceasing, by the Church, to God on his behalf.
6 Ana kamar gobe Hiridus zai fitar da shi, a wannan daren, Bitrus yana barci a tsakanin sojoji biyu, daure da sarkoki biyu; sojoji kuma na gadi a bakin kurkukun.
And when Herod was ready to produce him, in that same night, Peter was sleeping between two soldiers, and was bound with two chains. And there were guards in front of the door, guarding the prison.
7 Ba zato, sai ga mala'ikan Ubangiji ya bayyana a gareshi, haske ya haskaka dakin. Ya taba Bitrus a gefe ya tashe shi kuma ya ce, “Tashi da sauri.” Sai ga sarkokin suka zube daga hannunsa.
And behold, an Angel of the Lord stood near, and a light shined forth in the cell. And tapping Peter on the side, he awakened him, saying, “Rise up, quickly.” And the chains fell from his hands.
8 Mala'ikan ya ce masa, “Yi damara ka sa takalmanka.” Bitrus kuwa yayi haka. Mala'ikan ce ma sa, “Yafa mayafinka, ka biyo ni.”
Then the Angel said to him: “Dress yourself, and put on your boots.” And he did so. And he said to him, “Wrap your garment around yourself and follow me.”
9 Bitrus kuwa ya bi mala'ikan suka fita waje. Bai gane abin da mala'ikan ke yi zahiri ne ba. Yana zaton ko yana ganin wahayi ne.
And going out, he followed him. And he did not know this truth: that this was being done by an Angel. For he thought that he was seeing a vision.
10 Bayan da suka wuce masu tsaron fari da na biyu, sun kai kofar da aka yi da karfe wadda ta mike zuwa cikin gari; ta bude masu da kanta. Suka fita sun bi titin, kuma nan take kuma sai mala'ikan ya bar shi.
And passing by the first and second guards, they came to the iron gate which leads into the city; and it opened for them by itself. And departing, they continued on along a certain side street. And suddenly the Angel withdrew from him.
11 Da Bitrus ya komo hayyacin sa, ya ce, “Hakika yanzu na gane Ubangiji ya aiko da mala'ikansa don ya kubutar da ni daga hannun Hiridus da abin da Yahudawa suke zato.”
And Peter, returning to himself, said: “Now I know, truly, that the Lord sent his Angel, and that he rescued me from the hand of Herod and from all that the people of the Jews were anticipating.”
12 Da ya gane haka, ya zo gidan Maryamu mahaifiyar Yahaya wanda sunan mahaifinsa Markus; masu bi da yawa sun taru a can suna addu'a.
And as he was considering this, he arrived at the house of Mary, the mother of John, who was surnamed Mark, where many were gathered and were praying.
13 Da ya kwankwasa kofar gidan, sai baiwar gidan mai suna Roda ta zo don ta bude kofar.
Then, as he knocked at the door of the gate, a girl went out to answer, whose name was Rhoda.
14 Da ta gane muryar Bitrus, don farin ciki ta kasa bude kofar; maimakon haka, ta koma daki a guje, don ta basu labari Bitrus na tsaye a bakin kofa.
And when she recognized the voice of Peter, out of joy, she did not open the gate, but instead, running in, she reported that Peter stood before the gate.
15 Suka ce mata, “Kin haukace.” Amma ta nace da cewa haka ne. Suka ce, “Mala'ikansa ne.”
But they said to her, “You are crazy.” But she reaffirmed that this was so. Then they were saying, “It is his angel.”
16 Amma Bitrus ya ci gaba da kwankwasawa, da suka bude kofar, sai suka ga ai shine, suka sha mamaki kwarai.
But Peter was persevering in knocking. And when they had opened, they saw him and were astonished.
17 Bitrus kuwa ya yi masu hannu yana, masu alama su yi shuru. Sai ya gaya masu labarin yadda Ubangiji ya kubutar da shi daga kurkukun. Ya ce, “Ku gaya wa Yakubu da dukan 'yan'uwa abin da ya faru.” Sai ya bar su, ya tafi wani wuri.
But motioning to them with his hand to be silent, he explained how the Lord had led him away from prison. And he said, “Inform James and those brothers.” And going out, he went away to another place.
18 Sa'anda gari ya waye ba karamar hargowa ce ta tashi a cikin sojojin ba, game da abin da ya faru da Bitrus.
Then, when daylight came, there was no small commotion among the soldiers, as to what had happened concerning Peter.
19 Bayan da Hiridus ya neme shi kuma bai same shi ba, sai ya tambayi masu tsaron kuma ya bada umarni a kashe su. Sai ya gangara daga Yahudiya zuwa Kaisariya ya yi zamansa a can.
And when Herod had requested him and did not obtain him, having had the guards interrogated, he ordered them led away. And descending from Judea into Caesarea, he lodged there.
20 Yanzu kuwa Hiridus ya yi fushi sosai da mutanen Taya da Sidon. Suka tafi wurinsa tare. Suka roki Bilastasa, mataimakin sarkin, ya taimake su. Sai suka nemi sasantawa don suna samun abinci daga kasarsa ne.
Now he was angry with those of Tyre and Sidon. But they came to him with one accord, and, having persuaded Blastus, who was over the bedchamber of the king, they petitioned for peace, because their regions were supplied with food by him.
21 A ranan da aka kayyade, Hirudus ya sha damara da kayan saurata kuma ya zauna akan kursiyi; ya yi masu jawabi.
Then, on the appointed day, Herod was clothed in kingly apparel, and he sat in the judgment seat, and he gave a speech to them.
22 Mutanen suka yi ihu, “Wannan muryar allahce, ba ta mutum ba!”
Then the people were crying out, “The voice of a god, and not of a man!”
23 Nan take mala'ika Ubangiji ya buge shi don bai ba Allah daukaka ba, nan take tsutsotsi suka cinye shi har ya mutu.
And immediately, an Angel of the Lord struck him down, because he had not given honor to God. And having been consumed by worms, he expired.
24 Maganar Allah ta yadu tana ta ribabbanya.
But the word of the Lord was increasing and multiplying.
25 Bayan Barnaba da Shawulu sun gama aikin su a Urushalima. Suna dawowa, suka zo tare da Yahaya wanda sunan mahaifinsa Markus ne. [Barnaba da Shawulu suka koma Urushalima.]
Then Barnabas and Saul, having completed the ministry, returned from Jerusalem, bringing with them John, who was surnamed Mark.