< Ayyukan Manzanni 11 >
1 Yanzu Manzani da 'yan'uwa wadanda suke cikin Yahudiya suka ji cewa al'ummai ma sun karbi maganar Allah
Les apôtres et les frères de Judée apprirent que les païens aussi avaient accepté la Parole de Dieu,
2 Lokacin da Bitrus ya je Urushalima, wadanda suke na kaciya suka zarge shi;
et Pierre, à son retour à Jérusalem, fut blâmé par les fidèles circoncis:
3 suka ce, “Ka hada kai tare da mutane marasa kaciya kana ci tare da su!”
«Tu es entré chez des incirconcis, lui dirent-ils, et tu as mangé avec eux!»
4 Amma Bitrus ya fara bayyana masu dalla-dalla; ya ce,
Mais Pierre leur raconta, en suivant l'ordre des faits, tout ce qui s'était passé:
5 Ina addu'a a cikin birnin Yafa, sai na ga wahayi game da taska yana saukowa, kamar babban mayafi da aka saukar daga sama ta kusurwan nan hudu. Ya sauko gabana.
«J'étais, leur dit-il, dans la ville de Joppé, et pendant que je priais j'eus une extase et une vision m'apparut; c'était un objet descendant du ciel, ressemblant à une grande nappe nouée aux quatre coins et qui vint jusqu'à moi.
6 Na zura masa ido kuma na yi tunani a kansa, na ga dabbobi masu kafa hudu na duniya, miyagun dabbobi, da masu rarrafe, da tsuntsayen sama.
Ayant regardé à l'intérieur, l'ayant bien examinée, j'y vis les quadrupèdes de la terre, les animaux sauvages, les reptiles et les oiseaux du ciel,
7 Sai na ji murya tana ce da ni, “Tashi, Bitrus, yanka ka ci.”
et j'entendis une voix qui me disait: «Lève-toi, Pierre, tue et mange»;
8 Na ce, “Ba haka ba, Ubangiji: gama babu abu mara tsarki ko mai kazanta da ya taba shiga bakina.”
je répondis: «Nullement, Seigneur, parce que jamais rien de souillés ni d'impur n'est entré dans ma bouche».
9 Amma murya ta amsa kuma daga sama cewa, “Abin da Allah ya kira mai tsarki, kada ka kira shi mara tsarki.”
Une voix, venant du ciel, s'adressa à moi pour la seconde fois: «N'appelle pas souillés ce que Dieu a purifié.»
10 Wannan ya faru sau uku, sai dukan komai ya koma sama.
Cela se répéta par trois fois, puis tout remonta au ciel.»
11 Nan da nan sai ga mutane uku tsaye a gaban gidan da muke; an aike su daga Kaisariya zuwa gare ni.
«Et voilà qu'à ce moment même trois hommes se présentèrent à la porte de la maison où j'étais; ils m'étaient envoyés de Césarée.
12 Ruhun ya umurce ni in tafi tare da su, ba tare da nuna banbanci game da su ba. Yan'uwan nan shida sun tafi tare da ni, sai muka shiga gidan mutumin.
L'Esprit me dit d'aller avec eux sans aucun scrupule. Les six frères que voici m'accompagnèrent et nous entrâmes dans la maison de Cornélius.»
13 Ya fada mana yadda ya ga mala'ika tsaye a cikin gidansa yana cewa “Aiki mutane zuwa Yafa, su kirawo Saminu wanda ake kira Bitrus.
«Celui-ci nous raconta comment il avait vu dans sa maison l'ange se tenant devant lui et lui disant: «Envoie à Joppé et fais venir Simon, surnommé Pierre,
14 Zai gaya maku sakon da za ku sami ceto kai da dukan gidanka.”
il te dira des choses par lesquelles tu obtiendras le salut, toi et tous les tiens.»
15 Da na fara magana da su, Ruhu Mai Tsarki ya sauko akansu kamar yadda ya sauko mana tun da farko.
Lorsque je commençai à leur parler, l'Esprit saint descendit sur eux, comme sur nous à l'origine;
16 Sai na tuna da maganar Ubangiji, yadda ya ce,”Hakika Yahaya ya yi baptisma da ruwa, amma ku za a yi maku baptisma da Ruhu Mai Tsarki.”
et je me souvins de ce mot du Seigneur, quand il disait: «Jean baptisait d'eau, mais vous, vous serez baptisés d'Esprit saint.»
17 To, idan Allah ya yi masu baiwa kamar yadda ya yi mana yayin da muka bada gaskiya ga Ubangiji Yesu Almasihu, wane ni da zan yi jayayya da Allah?
Si donc Dieu leur a accordé le même don qu'à nous, pour avoir cru au Seigneur Jésus-Christ, qui étais-je moi pour oser m'opposer à Dieu?»
18 Da suka ji wadannan abubuwa, suka rasa ta cewa, amma suka daukaka Allah suka ce “Ga al'ummai ma Allah ya basu tuba zuwa rai.”
A l'ouïe de ces paroles, ils se calmèrent, et ils rendirent gloire à Dieu: «Ainsi, disaient-ils, Dieu a aussi accordé aux païens la repentance pour qu'ils aient la vie.»
19 Sai wadanda suka warwatsu saboda tsananin da ya bi bayan mutuwan Istifanas, suka yadu har zuwa Finikiya, Kuburus da Antakiya, amma suka yi wa'azin Yesu ga Yahudawa kadai.
Ceux qui avaient été dispersés par la persécution, à la suite de la mort d'Étienne, allèrent jusqu'en Phénicie et atteignirent Chypre et Antioche, n'annonçant la parole à personne qu'aux Juifs.
20 Amma wadan sunsu, mutane daga Kuburus da Kurane, suka zo Antakiya suka yi magana da hellenawa, suna yi masu wa'azin Ubangiji Yesu.
Mais quelques-uns d'eux qui étaient Chypriotes et Cyrénéens, arrivés à Antioche, parlèrent aussi aux Hellénistes et leur annoncèrent l'Évangile du Seigneur Jésus.
21 Kuma ikon Ubangiji yana tare da su, har mutane da yawa suka gaskata kuma suka juyo wurin Ubangiji.
La main du Seigneur fut avec eux et grand fut le nombre de ceux qui crurent et se convertirent au Seigneur.
22 Labari game da su ya iso kunnen ikilisiya da ke Urushalima: sai suka aika da Barnaba zuwa can Antakiya.
Le bruit en parvint aux oreilles des membres de l'Église de Jérusalem et ils envoyèrent Barnabas jusqu'à Antioche.
23 Da ya iso kuma ya ga kyautar Allah, sai ya yi farinciki; ya karfafa su dukka su kafu cikin Ubangiji da dukan zuciyar su.
Lorsque, à son arrivée, il vit la grâce de Dieu, il s'en réjouit et il les exhorta tous à rester, d'un coeur convaincu, fidèles au Seigneur,
24 Domin shi mutumin kirki ne, cike kuma da Ruhu Mai Tsarki da bangaskiya, sai mutane da yawa suka karu ga Ubangiji.
parce qu'il était homme de bien, plein d'Esprit saint et de foi; et un grand nombre de personnes s'unirent au Seigneur.
25 Sai Barnaba ya tafi Tarsus domin ya nemi Shawulu.
Barnabas se rendit ensuite à Tarse, y chercha Saul, le trouva et l'amena à Antioche.
26 Da ya same shi, ya kawo shi Antakiya. Ya kasance, shekara guda suna taruwa tare da ikilisiya suka koyar da mutane da yawa. A Antakiya ne aka fara kiran almajiran Krista.
Durant une année entière ils restèrent ensemble dans l'Église et instruisirent un grand nombre de personnes. Ce fut à Antioche qu'on donna pour la première fois aux disciples le nom de chrétiens.
27 A cikin kwanakin nan wadansu annabawa daga Urushalima suka zo Antakiya.
En ce temps-là, des prophètes se rendirent de Jérusalem à Antioche.
28 Daya daga cikinsu, mai suna Agabas ya mike tsaye yayi magana da ikon Ruhu cewa za a yi tsanani fari ko'ina a duniya. Wannan ya faru ne a zamanin Kalaudiya.
L'un d'eux, nommé Agabus, se leva et annonça par l'Esprit qu'une grande famine régnerait sur toute la terre; elle arriva, en effet, sous Claude.
29 Sai, almajiran, suka dau niyya kowa gwargwadon karfinsa, su aika wa 'yan'uwa da ke Yahudiya da taimako.
Les disciples décidèrent d'envoyer, chacun selon son pouvoir, un secours aux frères demeurant en Judée;
30 Suka yi haka; sun aika wa dattawa da kudi ta hanun Barnaba da Shawulu.
ce qu'ils firent en le remettant aux Anciens par l'entremise de Barnabas et de Saul.