< Ayyukan Manzanni 10 >
1 An yi wani Mutum a birnin Kaisariya, mai suna Karniliyas, shugaban sojoji ne na kungiyar da ake kira Italiya.
Or il y avait à Césarée un homme, nommé Corneille, Centenier d'une cohorte [de la Légion] appelée Italique;
2 Mutum ne mai ibada, wanda ya mika kansa da iyalinsa ga bautar Allah; ya kan bada taimakon kudi mai yawa ga Yahudawa, kuma yana addu'a ko yaushe ga Allah.
[Homme] dévot et craignant Dieu, avec toute sa famille, faisant aussi beaucoup d'aumônes au peuple, et priant Dieu continuellement;
3 Wajen sa'a ta tara ga yini, an bayyana masa cikin wahayi mala'kan Ubangiji na zuwa gare shi sai mala'ikan ya ce masa, ''Karniliyas!''
Lequel vit clairement en vision environ sur les neuf heures du jour, un Ange de Dieu qui vint à lui, et qui lui dit: Corneille!
4 Karniliyas ya zuba wa mala'ikan ido a tsorace ya ce ''Menene, mai gida?'' mala'ikan ya ce masa, ''Addu'ar ka da taimakon ka ga talakawa ya kai sama matsayin sadaka abin tunawa a gaban Allah,
Et Corneille ayant les yeux arrêtés sur lui, et étant tout effrayé, lui dit: qu'y a-t-il, Seigneur? Et il lui dit: tes prières et tes aumônes sont montées en mémoire devant Dieu.
5 ''Yanzu ka aika mutane zuwa birnin Yafa su kawo mutum mai suna Saminu wanda ake kira Bitrus.
Maintenant donc envoie des gens à Joppe, et fais venir Simon, qui est surnommé Pierre.
6 Yana zama tare da Saminu majemi, wanda gidansa ke bakin teku.
Il est logé chez un certain Simon corroyeur, qui a sa maison près de la mer; c'est lui qui te dira ce qu'il faut que tu fasses.
7 Da mala'ikan da ya yi magana da shi ya tafi, Karniliyas ya kira biyu daga barorin gidansa, da kuma soja guda mai bautar Allah daga cikin sojojin da suke masa hidima.
Et quand l'Ange qui parlait à Corneille s'en fut allé, il appela deux de ses serviteurs, et un soldat craignant Dieu, d'entre ceux qui se tenaient autour de lui.
8 Karniliyas ya fada masu dukan abin ya faru sai ya aike su Yafa.
Auxquels ayant tout raconté, il les envoya à Joppe.
9 Washe gari wajen sa'a ta shida (tsakar rana) suna cikin tafiya da suka yi kusa da birni, Bitrus ya hau kan bene don ya yi addu'a.
Or le lendemain comme ils marchaient, et qu'ils approchaient de la ville, Pierre monta sur la maison pour prier, environ vers les six heures.
10 Sai ya ji yunwa kuma yana bukatar wani abinda da zai ci, amma a yayin da mutanen na dafa abinci, sai ya ga wahayi.
Et il arriva qu'ayant faim, il voulut prendre son repas; et comme ceux de la maison lui apprêtaient à manger, il lui survint un ravissement d'esprit;
11 Sai ya ga sararin sama ya bude kuma wani tasa na saukowa, wani abu kamar babban mayafi yana saukowa zuwa duniya, ana zuro shi ta kusuryoyinsa hudu.
Et il vit le ciel ouvert, et un vaisseau descendant sur lui comme un grand linceul, lié par les quatre bouts, et descendant en terre;
12 A cikinsu kuwa akwai dukan halitun dabbobi masu kafa hudu da kuma masu rarrafe a duniya da tsunstayen sama.
Dans lequel il y avait de toutes sortes d'animaux terrestres à quatre pieds, des bêtes sauvages, des reptiles, et des oiseaux du ciel.
13 Sai murya ta yi magana da shi; “Tashi, Bitrus, yanka ka ci ''
Et une voix lui fut adressée, disant: Pierre, lève-toi, tue, et mange.
14 Amma Bitrus ya ce ''Ba haka ba, Ubangiji, gama ban taba cin abu mara tsarki ko mai kazanta ba.”
Mais Pierre répondit: je n'ai garde, Seigneur! car jamais je n'ai mangé aucune chose immonde ou souillée.
15 Amma muryar ta sake zuwa masa karo na biyu kuma; “Abinda Allah ya tsarkake, kada ka kira shi kazantacce.”
Et la voix lui dit encore pour la seconde fois: les choses que Dieu a purifiées, ne les tiens point pour souillées.
16 Wannan ya faru sau uku; nan da nan sai aka dauki tasar zuwa sama.
Et cela arriva jusques à trois fois, et puis le vaisseau se retira au ciel.
17 A yayin da Bitrus na cikin rudani game da ma'anar wahayin da ya gani, sai ga mutanen da Karniliyas ya aika suna tsaye a bakin kofar gidan, bayan sun tambayi hanyar zuwa gidan,
Or comme Pierre était en peine en lui-même, pour savoir quel était le sens de cette vision qu'il avait vue, alors voici, les hommes envoyés par Corneille s'enquérant de la maison de Simon, arrivèrent à la porte.
18 Kuma suka yi sallama suna tambaya ko Saminu wanda ake kira Bitrus ya sauka a nan.
Et ayant appelé quelqu'un, ils demandèrent si Simon, qui était surnommé Pierre, était logé là.
19 A yayin da Bitrus yana kan tunani akan wahayin, Ruhu ya ce masa, “Duba, mutane uku na neman ka.”
Et comme Pierre pensait à la vision, l'Esprit lui dit: voilà trois hommes qui te demandent.
20 Tashi ka sauka ka tafi tare da su. Kada ka yi jinkirin tafiya tare da su, domin Nine na aike su.”
Lève-toi donc, et descends, et t'en va avec eux, sans en faire difficulté: car c'est moi qui les ai envoyés.
21 Bitrus kuwa ya sauko wurin mutanen ya ce, “Ni ne wanda kuke nema. Me ya sa kuka zo?”
Pierre donc, étant descendu vers les gens qui lui avaient été envoyés par Corneille leur dit: voici, je suis celui que vous cherchez; quelle est la cause pour laquelle vous êtes venus?
22 Suka ce, “Shugaban soja mai suna Karniliyas, adalin mutum kuma mai bautar Allah, yana da kyakkyawar shaida a dukan al'umman Yahudawa, shi ne wanda mala'ika mai tsarki na Allah ya aika domin ka zo gidansa, ya ji sako daga wurinka.”
Et ils dirent: Corneille Centenier, homme juste et craignant Dieu, et ayant un bon témoignage de toute la nation des Juifs, a été averti de Dieu par un saint Ange de t'envoyer quérir pour venir en sa maison, et t'ouïr parler.
23 Sai Bitrus ya gayyace su su zo ciki kuma su zauna tare da shi. Washegari sai ya tafi tare da su, kuma wadansu 'yan'uwa daga Yafa suka raka shi.
Alors Pierre les ayant fait entrer, les logea; et le lendemain il s'en alla avec eux, et quelques-uns des frères de Joppe lui tinrent compagnie.
24 Kashegari suka shiga Kaisariya, Karniliyas kuwa yana jiran su; har ma ya gayyaci 'yan'uwansa da kuma abokansa na kusa.
Et le lendemain ils entrèrent à Césarée. Or Corneille les attendait, ayant appelé ses parents et ses familiers amis.
25 Ya kasance sa'adda Bitrus ya shiga, Karniliyas ya sadu da shi kuma ya durkusa ya yi masa sujada.
Et il arriva que comme Pierre entrait, Corneille venant au-devant de lui, et se jetant à ses pieds, l'adora.
26 Amma Bitrus ya tashe shi yana cewa, “Tashi tsaye! Ni ma mutum ne.”
Mais Pierre le releva, en lui disant: lève-toi, je suis aussi un homme.
27 A lokacin da Bitrus yake magana da shi, ya shiga ciki sai ya tarar da mutane da yawa sun taru a wuri daya.
Puis en parlant avec lui, il entra, et trouva plusieurs personnes qui étaient là assemblées.
28 Ya ce masu, “Ku da kanku kun sani bai dace Bayahuden mutum ya yi ma'amulla ko ya ziyarci wani ko wata kabila ba. Amma Allah ya ce da ni kada in ce da kowa mara tsarki ko kazantacce.
Et il leur dit: vous savez comme il n'est pas permis à un homme Juif de se lier avec un étranger, ou d'aller chez lui, mais Dieu m'a montré que je ne devais estimer aucun homme être impur ou souillé.
29 Wannan shine yasa na zo ba tare da musu ba, a lokacin da kuka kira ni. Don haka na tambaye ku me ya sa kuka aika in zo.”
C'est pourquoi dès que vous m'avez envoyé quérir, je suis venu sans en faire difficulté. Je vous demande donc pour quel sujet vous m'avez envoyé quérir.
30 Karniliyas ya ce “Kwanaki hudu da sun wuce a daidai wannan lokaci, ina addu'a da cikin sa'a na tara (karfe uku) a gidana, sai na ga mutum tsaye a gabana da tufafi mai haske.
Et Corneille lui dit: il y a quatre jours à cette heure-ci, que j'étais en jeûne, et que je faisais la prière à neuf heures dans ma maison; et voici, un homme se présenta devant moi en un vêtement éclatant.
31 Ya ce, “Karniliyas, Allah ya ji addu'ar ka, kuma taimakon ka ga talakawa ya tuna ma Allah da kai.
Et il me dit: Corneille, ta prière est exaucée, et Dieu s'est souvenu de tes aumônes.
32 Saboda haka ka aika da wani Yafa, ya kira maka mutum mai suna Saminu wanda ake kira Bitrus. Yana zama a gidan Saminu majemi, da ke bakin teku.
Envoie donc à Joppe, et fais venir de là Simon, surnommé Pierre, qui est logé dans la maison de Simon corroyeur, près de la mer, lequel étant venu, te parlera.
33 [Idan ya zo, zai yi magana da kai.]
C'est pourquoi j'ai d'abord envoyé vers toi, et tu as bien fait de venir. Or maintenant nous sommes tous présents devant Dieu pour entendre tout ce que Dieu t'a commandé de nous dire.
34 Sai Bitrus ya bude bakinsa ya ce, “Gaskiya, na fahimci Allah baya nuna bambanci.
Alors Pierre prenant la parole, dit: en vérité je reconnais que DIeu n'a point d'égard à l'apparence des personnes;
35 Maimakon haka, cikin kowace al'umma duk mai ibada kuma mai aikata adalci karbabbe ne a gare shi.
Mais qu'en toute nation celui qui le craint, et qui s'adonne à la justice, lui est agréable.
36 Ku kun san sakon da ya aika wa mutanen Isra'ila, a lokacin da ya sanar da labarin mai kyau na salama ta wurin Yesu Kristi, wanda shine Ubangiji na duka.
c'est ce qu'il a envoyé signifier aux enfants d'Israël, en annonçant la paix par Jésus-Christ, qui est le Seigneur de tous.
37 Ku da kanku kun san al'amuran da suka kasance, wanda ya faru cikin Yahudiya, farawa daga Galili, bayan sanarwar baftismar da Yahaya ya yi.
Vous savez ce qui est arrivé dans toute la Judée en commençant par la Galilée, après le Baptême que Jean a prêché;
38 Al'amura game da Yesu Banazare, yadda Allah ya kebe shi da Ruhu Mai Tsarki da iko kuma. Ya kuma ci gaba da aikin alheri da warkarwa ga dukan wadanda shaidan ya daure, domin Allah yana tare da shi.
[Savoir], comment Dieu a oint du Saint-Esprit et de force Jésus le Nazarien, qui a passé de lieu en lieu, en faisant du bien, et guérissant tous ceux qui étaient sous le pouvoir du démon: car Dieu était avec Jésus.
39 Mu shaidu ne ga dukan abubuwan da ya yi a kasar Yahudawa da cikn Urushalima, wannan Yesu wanda suka kashe, ta wurin giciye shi a akan itace.
Et nous sommes témoins de toutes les choses qu'il a faites, tant au pays des Juifs, qu'à Jérusalem; et comment ils l'ont fait mourir le pendant au bois.
40 Wannan mutumin, Allah ya ta da shi rana ta uku ya kuma maishe shi sananne,
[Mais] Dieu l'a ressuscité le troisième jour, et l'a donné pour être manifesté;
41 ba ga dukan mutane ba, amma ga shaidun da Allah ya zaba tun da farko - mu kanmu, wadanda muka ci muka sha tare da shi bayan tashin sa daga matattu,
Non à tout le peuple, mais aux témoins auparavant ordonnés de Dieu, à nous, [dis-je], qui avons mangé et bu avec lui après qu'il a été ressuscité des morts.
42 Ya umarce mu mu yi wa mutane wa'azi mu kuma tabbatar cewa shine wanda Allah ya zaba ya yi shariya bisa masu rai da matattu.
Et il nous a commandé de prêcher au peuple, et de témoigner que c'est lui qui est destiné de Dieu pour être le Juge des vivants et des morts.
43 Gareshi ne dukan annabawa suka yi shaida, domin dukan wanda ya bada gaskiya gareshi ya sami gafarar zunubai ta wurin sunansa.`
Tous les Prophètes lui rendent témoignage, que quiconque croira en lui, recevra la rémission de ses péchés par son Nom.
44 Sa'adda Bitrus yana kan magana game da wadannan abubuwa, Ruhu Mai Tsarki ya sauko a kan dukan wadanda suke sauraron wa'azin sa.
Comme Pierre tenait encore ce discours, le Saint-Esprit descendit sur tous ceux qui écoutaient la parole.
45 Mutanen da ke kungiyar masu bi da suka yarda da kaciya, dukan wadanda suka zo tare da Bitrus suka yi mamaki, domin baiwar Ruhu Mai Tsarki ya sauko a kan al'ummai.
Mais les Fidèles de la Circoncision qui étaient venus avec Pierre, s'étonnèrent de ce que le don du Saint-Esprit était aussi répandu sur les Gentils.
46 Domin sun ji al'umman nan suna magana da wasu harsuna suna yabon Allah. Sai Bitrus ya amsa,
Car ils les entendaient parler [diverses] Langues, et glorifier Dieu.
47 “Ko akwai wanda zai hana wa wadannan baftisma ta ruwa, da shike suma sun karbi Ruhu Mai Tsarki kamar mu?”
Alors Pierre prenant la parole, dit: qu'est-ce qui pourrait s'opposer à ce que ceux-ci, qui ont reçu comme nous le Saint-Esprit, ne soient baptisés d'eau.
48 Sai ya ba da umarni a yi masu baftisma cikin sunan Yesu Kristi. Sai suka roke shi ya kasance da su na wasu kwanaki.
Il commanda donc qu'ils fussent baptisés au Nom du Seigneur. Alors ils le prièrent de demeurer là quelques jours.