< Ayyukan Manzanni 10 >

1 An yi wani Mutum a birnin Kaisariya, mai suna Karniliyas, shugaban sojoji ne na kungiyar da ake kira Italiya.
And there was a certain man in Caesarea, named Cornelius, a centurion of that which is called the Italian band;
2 Mutum ne mai ibada, wanda ya mika kansa da iyalinsa ga bautar Allah; ya kan bada taimakon kudi mai yawa ga Yahudawa, kuma yana addu'a ko yaushe ga Allah.
A religious man, and fearing God with all his house, giving much alms to the people, and always praying to God.
3 Wajen sa'a ta tara ga yini, an bayyana masa cikin wahayi mala'kan Ubangiji na zuwa gare shi sai mala'ikan ya ce masa, ''Karniliyas!''
This man saw in a vision manifestly, about the ninth hour of the day, an angel of God coming in unto him, and saying to him: Cornelius.
4 Karniliyas ya zuba wa mala'ikan ido a tsorace ya ce ''Menene, mai gida?'' mala'ikan ya ce masa, ''Addu'ar ka da taimakon ka ga talakawa ya kai sama matsayin sadaka abin tunawa a gaban Allah,
And he, beholding him, being seized with fear, said: What is it, Lord? And he said to him: Thy prayers and thy alms are ascended for a memorial in the sight of God.
5 ''Yanzu ka aika mutane zuwa birnin Yafa su kawo mutum mai suna Saminu wanda ake kira Bitrus.
And now send men to Joppe, and call hither one Simon, who is surnamed Peter:
6 Yana zama tare da Saminu majemi, wanda gidansa ke bakin teku.
He lodgeth with one Simon a tanner, whose house is by the sea side. He will tell thee what thou must do.
7 Da mala'ikan da ya yi magana da shi ya tafi, Karniliyas ya kira biyu daga barorin gidansa, da kuma soja guda mai bautar Allah daga cikin sojojin da suke masa hidima.
And when the angel who spoke to him was departed, he called two of his household servants, and a soldier who feared the Lord, of them that were under him.
8 Karniliyas ya fada masu dukan abin ya faru sai ya aike su Yafa.
To whom when he had related all, he sent them to Joppe.
9 Washe gari wajen sa'a ta shida (tsakar rana) suna cikin tafiya da suka yi kusa da birni, Bitrus ya hau kan bene don ya yi addu'a.
And on the next day, whilst they were going on their journey, and drawing nigh to the city, Peter went up to the higher parts of the house to pray, about the sixth hour.
10 Sai ya ji yunwa kuma yana bukatar wani abinda da zai ci, amma a yayin da mutanen na dafa abinci, sai ya ga wahayi.
And being hungry, he was desirous to taste somewhat. And as they were preparing, there came upon him an ecstasy of mind.
11 Sai ya ga sararin sama ya bude kuma wani tasa na saukowa, wani abu kamar babban mayafi yana saukowa zuwa duniya, ana zuro shi ta kusuryoyinsa hudu.
And he saw the heaven opened, and a certain vessel descending, as it were a great linen sheet let down by the four corners from heaven to the earth:
12 A cikinsu kuwa akwai dukan halitun dabbobi masu kafa hudu da kuma masu rarrafe a duniya da tsunstayen sama.
Wherein were all manner of fourfooted beasts, and creeping things of the earth, and fowls of the air.
13 Sai murya ta yi magana da shi; “Tashi, Bitrus, yanka ka ci ''
And there came a voice to him: Arise, Peter; kill and eat.
14 Amma Bitrus ya ce ''Ba haka ba, Ubangiji, gama ban taba cin abu mara tsarki ko mai kazanta ba.”
But Peter said: Far be it from me; for I never did eat any thing that is common and unclean.
15 Amma muryar ta sake zuwa masa karo na biyu kuma; “Abinda Allah ya tsarkake, kada ka kira shi kazantacce.”
And the voice spoke to him again the second time: That which God hath cleansed, do not thou call common.
16 Wannan ya faru sau uku; nan da nan sai aka dauki tasar zuwa sama.
And this was done thrice; and presently the vessel was taken up into heaven.
17 A yayin da Bitrus na cikin rudani game da ma'anar wahayin da ya gani, sai ga mutanen da Karniliyas ya aika suna tsaye a bakin kofar gidan, bayan sun tambayi hanyar zuwa gidan,
Now, whilst Peter was doubting within himself, what the vision that he had seen should mean, behold the men who were sent from Cornelius, inquiring for Simon’s house, stood at the gate.
18 Kuma suka yi sallama suna tambaya ko Saminu wanda ake kira Bitrus ya sauka a nan.
And when they had called, they asked, if Simon, who is surnamed Peter, were lodged there.
19 A yayin da Bitrus yana kan tunani akan wahayin, Ruhu ya ce masa, “Duba, mutane uku na neman ka.”
And as Peter was thinking of the vision, the Spirit said to him: Behold three men seek thee.
20 Tashi ka sauka ka tafi tare da su. Kada ka yi jinkirin tafiya tare da su, domin Nine na aike su.”
Arise, therefore, get thee down and go with them, doubting nothing: for I have sent them.
21 Bitrus kuwa ya sauko wurin mutanen ya ce, “Ni ne wanda kuke nema. Me ya sa kuka zo?”
Then Peter, going down to the men, said: Behold, I am he whom you seek; what is the cause for which you are come?
22 Suka ce, “Shugaban soja mai suna Karniliyas, adalin mutum kuma mai bautar Allah, yana da kyakkyawar shaida a dukan al'umman Yahudawa, shi ne wanda mala'ika mai tsarki na Allah ya aika domin ka zo gidansa, ya ji sako daga wurinka.”
Who said: Cornelius, a centurion, a just man, and one that feareth God, and having good testimony from all the nation of the Jews, received an answer of an holy angel, to send for thee into his house, and to hear words of thee.
23 Sai Bitrus ya gayyace su su zo ciki kuma su zauna tare da shi. Washegari sai ya tafi tare da su, kuma wadansu 'yan'uwa daga Yafa suka raka shi.
Then bringing them in, he lodged them. And the day following he arose, and went with them: and some of the brethren from Joppe accompanied him.
24 Kashegari suka shiga Kaisariya, Karniliyas kuwa yana jiran su; har ma ya gayyaci 'yan'uwansa da kuma abokansa na kusa.
And the morrow after, he entered into Caesarea. And Cornelius waited for them, having called together his kinsmen and special friends.
25 Ya kasance sa'adda Bitrus ya shiga, Karniliyas ya sadu da shi kuma ya durkusa ya yi masa sujada.
And it came to pass, that when Peter was come in, Cornelius came to meet him, Cornelius came to meet him, and falling at his feet adored.
26 Amma Bitrus ya tashe shi yana cewa, “Tashi tsaye! Ni ma mutum ne.”
But Peter lifted him up, saying: Arise, I myself also am a man.
27 A lokacin da Bitrus yake magana da shi, ya shiga ciki sai ya tarar da mutane da yawa sun taru a wuri daya.
And talking with him, he went in, and found many that were come together.
28 Ya ce masu, “Ku da kanku kun sani bai dace Bayahuden mutum ya yi ma'amulla ko ya ziyarci wani ko wata kabila ba. Amma Allah ya ce da ni kada in ce da kowa mara tsarki ko kazantacce.
And he said to them: You know how abominable it is for a man that is a Jew, to keep company or to come unto one of another nation: but God hath shewed to me, to call no man common or unclean.
29 Wannan shine yasa na zo ba tare da musu ba, a lokacin da kuka kira ni. Don haka na tambaye ku me ya sa kuka aika in zo.”
For which cause, making no doubt, I came when I was sent for. I ask, therefore, for what cause you have sent for me?
30 Karniliyas ya ce “Kwanaki hudu da sun wuce a daidai wannan lokaci, ina addu'a da cikin sa'a na tara (karfe uku) a gidana, sai na ga mutum tsaye a gabana da tufafi mai haske.
And Cornelius said: Four days ago, unto this hour, I was praying in my house, at the ninth hour, and behold a man stood before me in white apparel, and said:
31 Ya ce, “Karniliyas, Allah ya ji addu'ar ka, kuma taimakon ka ga talakawa ya tuna ma Allah da kai.
Cornelius, thy prayer is heard, and thy alms are had in remembrance in the sight of God.
32 Saboda haka ka aika da wani Yafa, ya kira maka mutum mai suna Saminu wanda ake kira Bitrus. Yana zama a gidan Saminu majemi, da ke bakin teku.
Send therefore to Joppe, and call hither Simon, who is surnamed Peter: he lodgeth in the house of Simon a tanner, by the sea side.
33 [Idan ya zo, zai yi magana da kai.]
Immediately therefore I sent to thee: and thou hast done well in coming. Now therefore all we are present in thy sight, to hear all things whatsoever are commanded thee by the Lord.
34 Sai Bitrus ya bude bakinsa ya ce, “Gaskiya, na fahimci Allah baya nuna bambanci.
And Peter opening his mouth, said: In very deed I perceive, that God is not a respecter of persons.
35 Maimakon haka, cikin kowace al'umma duk mai ibada kuma mai aikata adalci karbabbe ne a gare shi.
But in every nation, he that feareth him, and worketh justice, is acceptable to him.
36 Ku kun san sakon da ya aika wa mutanen Isra'ila, a lokacin da ya sanar da labarin mai kyau na salama ta wurin Yesu Kristi, wanda shine Ubangiji na duka.
God sent the word to the children of Israel, preaching peace by Jesus Christ: (he is Lord of all.)
37 Ku da kanku kun san al'amuran da suka kasance, wanda ya faru cikin Yahudiya, farawa daga Galili, bayan sanarwar baftismar da Yahaya ya yi.
You know the word which hath been published through all Judea: for it began from Galilee, after the baptism which John preached,
38 Al'amura game da Yesu Banazare, yadda Allah ya kebe shi da Ruhu Mai Tsarki da iko kuma. Ya kuma ci gaba da aikin alheri da warkarwa ga dukan wadanda shaidan ya daure, domin Allah yana tare da shi.
Jesus of Nazareth: how God anointed him with the Holy Ghost, and with power, who went about doing good, and healing all that were oppressed by the devil, for God was with him.
39 Mu shaidu ne ga dukan abubuwan da ya yi a kasar Yahudawa da cikn Urushalima, wannan Yesu wanda suka kashe, ta wurin giciye shi a akan itace.
And we are witnesses of all things that he did in the land of the Jews and in Jerusalem, whom they killed, hanging him upon a tree.
40 Wannan mutumin, Allah ya ta da shi rana ta uku ya kuma maishe shi sananne,
Him God raised up the third day, and gave him to be made manifest,
41 ba ga dukan mutane ba, amma ga shaidun da Allah ya zaba tun da farko - mu kanmu, wadanda muka ci muka sha tare da shi bayan tashin sa daga matattu,
Not to all the people, but to witnesses preordained by God, even to us, who did eat and drink with him after he arose again from the dead;
42 Ya umarce mu mu yi wa mutane wa'azi mu kuma tabbatar cewa shine wanda Allah ya zaba ya yi shariya bisa masu rai da matattu.
And he commanded us to preach to the people, and to testify that it is he who was appointed by God, to be judge of the living and of the dead.
43 Gareshi ne dukan annabawa suka yi shaida, domin dukan wanda ya bada gaskiya gareshi ya sami gafarar zunubai ta wurin sunansa.`
To him all the prophets give testimony, that by his name all receive remission of sins, who believe in him.
44 Sa'adda Bitrus yana kan magana game da wadannan abubuwa, Ruhu Mai Tsarki ya sauko a kan dukan wadanda suke sauraron wa'azin sa.
While Peter was yet speaking these words, the Holy Ghost fell on all them that heard the word.
45 Mutanen da ke kungiyar masu bi da suka yarda da kaciya, dukan wadanda suka zo tare da Bitrus suka yi mamaki, domin baiwar Ruhu Mai Tsarki ya sauko a kan al'ummai.
And the faithful of the circumcision, who came with Peter, were astonished, for that the grace of the Holy Ghost was poured out upon the Gentiles also.
46 Domin sun ji al'umman nan suna magana da wasu harsuna suna yabon Allah. Sai Bitrus ya amsa,
For they heard them speaking with tongues, and magnifying God.
47 “Ko akwai wanda zai hana wa wadannan baftisma ta ruwa, da shike suma sun karbi Ruhu Mai Tsarki kamar mu?”
Then Peter answered: Can any man forbid water, that these should not be baptized, who have received the Holy Ghost, as well as we?
48 Sai ya ba da umarni a yi masu baftisma cikin sunan Yesu Kristi. Sai suka roke shi ya kasance da su na wasu kwanaki.
And he commanded them to be baptized in the name of the Lord Jesus Christ. Then they desired him to tarry with them some days.

< Ayyukan Manzanni 10 >