< 2 Timoti 4 >
1 Ina bada wannan umarni a gaban Allah da Yesu Almasihu, wanda zai yi wa rayayyu da matattu shari'a, kuma saboda bayyanuwarsa da mulkinsa:
I CHARGE thee therefore before God, and the Lord Jesus Christ, who shall judge the quick and the dead at his appearing and his kingdom;
2 Ka yi wa'azin Kalma. Ka himmantu a kai ko da zarafi ko ba zarafi. Ka tsautar, ka kwabar, ka gargadar, da dukan hakuri da koyarwa.
Preach the word; be instant in season, out of season; reprove, rebuke, exhort with all longsuffering and doctrine.
3 Gama lokaci na zuwa wanda mutane ba za su jure wa koyarwar kirki ba. Maimakon haka, zasu tattara wa kansu malamai bisa ga sha'awowin zuciyarsu. Za su rika fada masu abin da kunnuwansu ke so.
For the time will come when they will not endure sound doctrine; but after their own lusts shall they heap to themselves teachers, having itching ears;
4 Za su juya kunnuwansu daga koyarwar gaskiya, za su koma wa tatsunniyoyi na banza.
And they shall turn away their ears from the truth, and shall be turned unto fables.
5 Amma kai, sai ka natsu a cikin dukan abubuwa. Ka jure wa wahala; ka yi aikin mai bishara, ka cika hidimarka.
But watch thou in all things, endure afflictions, do the work of an evangelist, make full proof of thy ministry.
6 Gama ana-tsiyaye ni. Lokacin yin kaurata yayi.
For I am now ready to be offered, and the time of my departure is at hand.
7 Na yi tsere na gaskiya; na kuma kammala tseren; na rike bangaskiya.
I have fought a good fight, I have finished my course, I have kept the faith:
8 An adana mani rawani na adalci, wanda Ubangiji, alkali mai adalci, zai ba ni a ranan nan. Ba ni kadai ba, amma kuma ga dukkan wadanda suke kaunar zuwansa.
Henceforth there is laid up for me a crown of righteousness, which the Lord, the righteous judge, shall give me at that day: and not to me only, but unto all them also that love his appearing.
9 Ka yi iyakacin kokarinka ka zo wurina da sauri.
Do thy diligence to come shortly unto me:
10 Domin Dimas ya yashe ni. Ya kaunaci wannan duniyar, ya tafi Tassalonika, Kariskis ya tafi Galatiya, Titus kuma ya tafi Dalmatiya. (aiōn )
For Demas hath forsaken me, having loved this present world, and is departed unto Thessalonica; Crescens to Galatia, Titus unto Dalmatia. (aiōn )
11 Luka ne kadai yake tare da ni. Ka nemo Markus ka zo tare da shi domin yana da amfani a gareni a cikin aikin.
Only Luke is with me. Take Mark, and bring him with thee: for he is profitable to me for the ministry.
12 Na aiki Tikikus zuwa Afisus.
And Tychicus have I sent to Ephesus.
13 Ka kawo mani mayafin da na bari a Taruwasa wurin Karbus, idan za ka zo ka taho da shi, duk da littatafan nan, musanman takardun nan.
The cloke that I left at Troas with Carpus, when thou comest, bring with thee, and the books, but especially the parchments.
14 Iskandari makerin dalma ya kulla mani makirci ba kadan ba. Ubangiji zai biya shi gwargwadon ayyukansa.
Alexander the coppersmith did me much evil: the Lord reward him according to his works:
15 Kai ma ka yi hankali da shi, domin yana tsayyaya da maganganunmu sosai.
Of whom be thou ware also; for he hath greatly withstood our words.
16 Da farkon kariyar kaina, babu wanda ya goyi bayana. Maimakon haka kowa ya guje ni. Bana so dai a lissafta wannan a kansu.
At my first answer no man stood with me, but all men forsook me: I pray God that it may not be laid to their charge.
17 Amma Ubangiji ya kasance tare da ni, ya kuma karfafa ni, yadda ta wurina, shelar ta sami cika da kyau, domin dukan al'ummai su ji. An kwato ni daga bakin zaki.
Notwithstanding the Lord stood with me, and strengthened me; that by me the preaching might be fully known, and that all the Gentiles might hear: and I was delivered out of the mouth of the lion.
18 Allah zai kubutar ni daga dukan ayyukan mugunta, ya kuma cece ni domin mulkinsa na sama. Daukaka ta tabatta a gareshi har abada abadin. Amin. (aiōn )
And the Lord shall deliver me from every evil work, and will preserve me unto his heavenly kingdom: to whom be glory for ever and ever. Amen. (aiōn )
19 Ka gayar da Briskilla, da Akila, da gidan Onisifurus.
Salute Prisca and Aquila, and the household of Onesiphorus.
20 Arastus ya nan zaune a Korinti, amma na bar Turufimus ya na zazzabi a Militus.
Erastus abode at Corinth: but Trophimus have I left at Miletum sick.
21 Ka yi iyakar kokarinka, ka zo kamin hunturu. Yubulus yana gayar da kai, haka ma Budis da Linus da Kalafidiya da dukan 'yan'uwa.
Do thy diligence to come before winter. Eubulus greeteth thee, and Pudens, and Linus, and Claudia, and all the brethren.
22 Bari Ubangiji ya kasance tare da ruhunka. Bari Alheri ya kasance da kai.
The Lord Jesus Christ be with thy spirit. Grace be with you. Amen. The second epistle unto Timotheus, ordained the first bishop of the church of the Ephesians, was written from Rome, when Paul was brought before Nero the second time.