< 2 Timoti 2 >

1 Domin wannan kai, dana, ka karfafa cikin alherin da ke cikin Almasihu Yesu.
Thou therefore, my child, be strengthened in the grace that is in Christ Jesus.
2 Abubuwan da ka ji daga gare ni a bainar jama'a masu yawa, ka danka su ga mutane masu aminci da za su iya koya wa wadansu kuma.
And the things which thou hast heard from me among many witnesses, the same commit thou to faithful men, who shall be able to teach others also.
3 Ka daure shan tsanani tare da ni, kamar amintaccen sojan Almasihu Yesu.
Suffer hardship with [me], as a good soldier of Christ Jesus.
4 Ba bu sojan da zai yi bauta yayin da ya nannade kansa da al'amuran wannan rayuwar, domin ya gamshi shugabansa.
No soldier on service entangleth himself in the affairs of [this] life; that he may please him who enrolled him as a soldier.
5 Hakanan, idan wani yana gasa a matsayin dan wasa, ba zai sami rawani ba tukuna har sai in ya karasa tseren bisa ga ka'idodin gasar.
And if also a man contend in the games, he is not crowned, except he have contended lawfully.
6 Wajibi ne manomi mai kwazon aiki ya fara karbar amfanin gonarsa.
The husbandman that laboureth must be the first to partake of the fruits.
7 Ka yi tunani game da abin da na ke gaya maka, gama Ubangiji zai ba ka ganewa a cikin komai.
Consider what I say; for the Lord shall give thee understanding in all things.
8 Ka tuna da Yesu Almasihu, daga zuriyar Dauda, wanda a ka tayar daga matattu. Bisa ga wa'azin bisharata,
Remember Jesus Christ, risen from the dead, of the seed of David, according to my gospel:
9 wanda na ke shan wahala har ya kai ga dauri kamar mai laifi. Amma maganar Allah ba a daure ta ba.
wherein I suffer hardship unto bonds, as a malefactor; but the word of God is not bound.
10 Saboda haka na jure wa dukkan abubuwa domin wadanda aka zaba, saboda su ma su sami ceton da ke cikin Almasihu Yesu, da daukaka madawwamiya. (aiōnios g166)
Therefore I endure all things for the elect’s sake, that they also may obtain the salvation which is in Christ Jesus with eternal glory. (aiōnios g166)
11 Wannan magana tabbatacciya ce: “Idan mun mutu tare da shi, za mu kuma rayu tare da shi.
Faithful is the saying: For if we died with him, we shall also live with him:
12 Idan mun jure, zamu kuma yi mulki tare da shi. Idan mun yi musun sa, shi ma zai yi musun mu.
if we endure, we shall also reign with him: if we shall deny him, he also will deny us:
13 Idan mun zama marasa aminci, shi mai aminci ne koyaushe, domin shi ba zai yiwu ya musunta kansa ba.”
if we are faithless, he abideth faithful; for he cannot deny himself.
14 Ka yi ta tuna masu da wadannan abubuwan. Ka yi masu kashedi a gaban Allah kada su yi ta dauki ba dadi game da kalmomi. Saboda wannan bai da wani amfani. Domin wannan zai halakar da ma su sauraro.
Of these things put them in remembrance, charging [them] in the sight of the Lord, that they strive not about words, to no profit, to the subverting of them that hear.
15 Ka yi iyakacin kokarika domin ka mika kanka ma'aikacin Allah wanda aka tabbatar, wanda babu dalilin kunya a gareshi. Wanda ya ke koyar da kalmar gaskiya daidai.
Give diligence to present thyself approved unto God, a workman that needeth not to be ashamed, handling aright the word of truth.
16 Ka guje wa masu maganar sabo, wanda ya kan kara kaiwa ga rashin bin Allah.
But shun profane babblings: for they will proceed further in ungodliness,
17 Maganarsu za ta yadu kamar ciwon daji. Daga cikinsu akwai Himinayus da Filitus.
and their word will eat as doth a gangrene: of whom is Hymenaeus and Philetus;
18 Wadannan mutanen sun kauce wa gaskiya. Sun fadi cewa an rigaya an yi tashin matattu. Suka birkitar da bangaskiyar wadansu.
men who concerning the truth have erred, saying that the resurrection is past already, and overthrow the faith of some.
19 Duk da haka, ginshikin Allah ya tabbata. Ya na da wannan hatimi: “Ubangiji ya san wadanda ke nasa,” Kuma “Duk mai kira bisa ga sunan Ubangiji dole ya rabu da rashin adalci.”
Howbeit the firm foundation of God standeth, having this seal, The Lord knoweth them that are his: and, Let every one that nameth the name of the Lord depart from unrighteousness.
20 A gida mai wadata, ba kayayyaki na zinariya da azurfa ba ne kawai. Haka kuma akwai kayayyaki na itace da yunbu. Wadansu domin aikin mai daraja, wadansu kuma ga aiki mara daraja.
Now in a great house there are not only vessels of gold and of silver, but also of wood and of earth; and some unto honour, and some unto dishonour.
21 Idan wani ya tsarkake kansa daga rashin daraja, shi kayan aiki ne mai daraja. An kebe shi, abin aiki domin mai gidan, kuma a shirye domin kowanne aiki mai kyau.
If a man therefore purge himself from these, he shall be a vessel unto honour, sanctified, meet for the master’s use, prepared unto every good work.
22 Ka guje wa sha'awoyi na kuruciya, ka nemi adalci, bangaskiya, kauna da salama da wadanda suke kira ga sunan Ubangiji daga zuciya mai tsabta.
But flee youthful lusts, and follow after righteousness, faith, love, peace, with them that call on the Lord out of a pure heart.
23 Amma ka ki tambayoyi na wauta da jahilci. Ka sani sukan haifar da gardandami.
But foolish and ignorant questionings refuse, knowing that they gender strifes.
24 Tilas bawan Ubangiji ya guje wa jayayya. A maimakon haka dole ya zama mai tawali'u ga kowa, mai iya koyarwa, kuma mai hakuri.
And the Lord’s servant must not strive, but be gentle towards all, apt to teach, forbearing,
25 Dole ne ya koyarwa mutane da su ke jayayya da shi a cikin tawali'u. Watakila Allah ya ba su ikon tuba domin sanin gaskiyar.
in meekness correcting them that oppose themselves; if peradventure God may give them repentance unto the knowledge of the truth,
26 Suna iya sake dawowa cikin hankalinsu kuma su bar tarkon Ibilis, bayan da ya cafke su domin nufinsa.
and they may recover themselves out of the snare of the devil, having been taken captive by the Lord’s servant unto the will of God.

< 2 Timoti 2 >