< 2 Timoti 1 >
1 Bulus, manzon Almasihu Yesu ta wurin nufin Allah, bisa ga alkawarin rai da ke cikin Almasihu Yesu,
Paulus; Kristi Jesu Apostel ved Guds Villie, for at bringe Forjættelse om Livet i Kristus Jesus
2 zuwa ga Timoti, kaunataccen da: Alheri, jinkai, da salama daga Allah Uba da Almasihu Yesu Ubangijinmu.
- til Timotheus, sit elskede Barn: Nåde, Barmhjertighed og Fred fra Gud Fader og Kristus Jesus, vor Herre!
3 Na gode wa Allah, wanda na ke bautawa tun daga kakannina, da lamiri mai tsabta, sa'adda na ke tuna wa da kai cikin addu'o'ina koyaushe (dare da rana).
Jeg takker Gud, hvem jeg fra mine Forfædre af har tjent i en ren Samvittighed, ligesom jeg uafladelig har dig i Erindring i mine Bønner Nat og Dag,
4 Sa'adda na tuna da hawayenka, na yi marmarin ganinka, saboda in cika da farin ciki.
da jeg i Mindet om dine Tårer længes efter at se dig, for at jeg må fyldes med Glæde,
5 An tunashshe ni game da sahihiyar bangaskiyarka, wadda ta samo asali daga kakarka Loyis da mahaifiyarka Afiniki. Na kuma tabbata ta na zaune a cikinka.
idet jeg er bleven mindet om den uskrømtede Tro, som er i dig, den, som boede først i din Mormoder Lois og din Moder Eunike, og jeg er vis på, at den også bor i dig.
6 Wannan shine dalilin da ni ke tunashshe ka cewa ka sake rura baiwar Allah da ke cikinka wadda ka samu sa'adda na dibiya maka hannuwana.
Derfor påminder jeg dig, at du opflammer den Guds Nådegave, som er i dig ved mine Hænders Pålæggelse.
7 Domin Allah bai ba mu ruhun tsoro ba, amma na iko da kauna da kamun kai.
Thi Gud har ikke givet os Fejgheds Ånd, men Krafts og Kærligheds og Sindigheds Ånd.
8 Saboda haka kada ka ji kunyar shaida ga me da Ubangijinmu, ko ni, Bulus, daurarrensa. Maimakon haka, ka zama a shirye ka sha wahala domin bishara bisa ga ikon Allah.
Derfor, skam dig ikke ved Vidnesbyrdet om vor Herre eller ved mig, hans Fange, men lid ondt med Evangeliet ved Guds Kraft,
9 Allah ne ya cecemu kuma ya kira mu da kira mai tsarki. Ya yi wannan, ba ta wurin ayyukanmu ba, amma ta wurin shirinsa da alherinsa. Ya ba mu wadannan abubuwan a cikin Almasihu Yesu kafin farkon zamanai. (aiōnios )
han, som frelste os og kaldte os med en hellig Kaldelse, ikke efter vore Gerninger, men efter sit eget Forsæt og Nåden, som blev given os i Kristus Jesus fra evige Tider, (aiōnios )
10 Amma yanzu an bayyana ceton Allah ta wurin bayyanuwar mai cetonmu Almasihu Yesu. Almasihu ne ya kawo karshen mutuwa ya kuma kawo rai marar karshe da ya bayyana ta wurin bishara.
men nu er kommen for Dagen ved vor Frelsers Jesu Kristi Åbenbarelse, han, som tilintetgjorde Døden, men bragte Liv og Uforkrænkelighed for Lyset ved Evangeliet,
11 Domin wannan, an zabe ni mai wa'azi, manzo da mallami zuwa ga al'ummai.
for hvilket jeg er bleven sat til Prædiker og Apostel og Hedningers Lærer,
12 Domin wannan dalili na ke shan wahalar wadannan abubuwa. Amma ban ji kunya ba, domin na san shi, wanda na gaskanta. Na sakankance zai iya adana abinda na mika masa har zuwa ranan nan.
hvorfor jeg også lider dette, men jeg skammer mig ikke derved; thi jeg ved, til hvem jeg har sat min Tro, og jeg er vis på, at han er mægtig til at vogte på den mig betroede Skat til hin Dag.
13 Ka adana misalin amintattun sakwanni da ka ji daga gare ni, ta wurin bangaskiya da kauna da ke cikin Almasihu Yesu.
Hav et Forbillede i de sunde Ord, som du har hørt af mig, i Tro og Kærlighed i Kristus Jesus.
14 Abu mai kyau da Allah ya danka maka, ka tsare shi ta wurin Ruhu Mai Tsarki, da ke zaune a cikinmu.
Vogt på den skønne betroede Skat ved den Helligånd, som bor i os.
15 Ka dai sani, dukkan wadanda su ke zama a Asiya sun juya mani baya. A cikin kungiyar akwai Fijalas da Harmajanas.
Du ved dette, at alle de i Asien have vendt sig fra mig, iblandt hvilke ere Fygelus og Hermogenes.
16 Bari Ubangiji ya yi wa iyalin Onisifaras jinkai, domin ya na yawan yi mani hidima, kuma ba ya jin kunyar sarkata.
Herren vise Onesiforus's Hus Barmhjertighed; thi han har ofte vederkvæget mig og skammede sig ikke ved min Lænke,
17 Maimakon haka, sa'adda ya ke a Roma, ya neme ni da kokarin gaske, ya kuma same ni.
men da han kom til Rom, søgte han ivrigt efter mig og fandt mig.
18 Bari Ubangiji ya sa, ya sami jinkai daga gare shi a wannan rana. Dukkan hanyoyin da ya taimake ni a kasar Afisa, kun sani sarai.
Herren give ham at finde Barmhjertighed fra Herren på hin Dag! Og hvor megen Tjeneste han har gjort i Efesus, ved du bedst.