< 2 Tessalonikawa 1 >

1 Bulus da Silbanus da Timoti, zuwa ga ikilisiyar Tasolonika cikin Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Almasihu.
Paul, Silvanus, and Timothy, to the church of the Thessalonians in God our Father and the Lord Jesus Christ:
2 Bari alheri ya kasance tare da ku da salama daga Allah Ubanmu da Ubangijinmu Yesu Almasihu.
Grace to you and peace from God our Father and the Lord Jesus Christ.
3 Lallai ne mu godewa Allah kulluyaumin domin ku, yan'uwa. Domin hakan dai dai ne, saboda bangaskiyarku ta karu sosai, kuma kaunar junanku tana karuwa.
We ought always to give thanks to God for you, brothers, as is only fitting, because your faith is greatly increasing and the love that each of you has for one another is abounding.
4 Mu da kanmu muna fahariya da ku a ikilisiyoyin Allah. Muna maganar hakurinku da bangaskiyarku a cikin dukkan tsananin da kuke fuskanta. Muna maganar kuncin da kuke jimrewa.
As a result we ourselves boast about you in the churches of God for your perseverance and faithfulness in all the persecutions and tribulations that you are enduring.
5 Wannan itace alamar shari'ar Allah ta adalci. Sakamakon haka shine za a dauke ku cancantattu na mulkin Allah wanda kuke wahala dominsa.
This is evidence of the righteous judgment of God, and it is happening so that you may be considered worthy of the kingdom of God, for which you are suffering.
6 Adalci ne ga Allah ya mayar da kunci ga wadanda suke kuntata maku,
It is indeed right for God to repay with affliction those who afflict you,
7 ya kuma baku hutu ku dake shan wuya tare da mu. Zai yi haka ne a bayyanar Ubangiji Yesu daga sama da Mala'ikun ikonsa.
and to give to you who are being afflicted relief along with us at the revelation of the Lord Jesus from heaven with his mighty angels.
8 A cikin wuta mai huruwa zai dau fansa bisa wadanda basu san Allah ba da wadanda basu karbi bisharar Ubangijinmu Yesu almasihu ba.
With flaming fire he will inflict vengeance on those who do not know God and who do not obey the gospel of our Lord Jesus.
9 Za su sha azaba ta hallaka har abada daga fuskar Ubangiji da kuma daukakar ikonsa. (aiōnios g166)
They will suffer the punishment of eternal destruction, separated from the presence of the Lord and from the glory of his might, (aiōnios g166)
10 Zai yi wannan lokacin da yazo a wannan rana don jama'arsa su daukaka shi, kuma ya zama abin mamaki ga dukkan wadanda suka bada gaskiya. Domin kun gaskata shaidarmu a gare ku.
on that day when he comes to be glorified by his saints and to be marveled at by all who have believed, including you, because you have believed our testimony.
11 Saboda wannan muke addu'a kullum domin ku. Muna addu'a domin Allahnmu ya sa ku cancanci kiran ku. Muna addu'a ya biya ku muradin ku na yin nagarta da dukkan wani aikin bangaskiya da kuma iko.
With this in mind, we always pray for you that our God will make you worthy of his calling and by his power bring to fulfillment every good intention and work of faith,
12 Muna addu'a haka domin sunan Ubangijinmu Yesu ya sami daukaka daga gare ku. Addu'armu itace ya daukaka ku, saboda alherin Allahnmu da Ubangijinmu Yesu Almasihu.
so that the name of our Lord Jesus will be glorified in you, and you in him, according to the grace of our God and Lord, Jesus Christ.

< 2 Tessalonikawa 1 >