< 2 Korintiyawa 1 >

1 Bulus, manzon Almasihu Yesu ta wurin nufin Allah, da kuma Timoti dan'uwan mu, zuwa ga Ikilisiyar Allah da ke a Korantus, da kuma dukan 'yan'uwa da ke yankin kasar Akaya.
To the Church of God which is in Corinth, and to all the saints throughout Greece. from Paul, by God’s will an apostle of Christ, and from brother Timothy.
2 Bari alheri ya kasance tare da ku da kuma salama ta Allah Ubanmu da kuma Ubangiji Yesu Almasihu.
Grace to you and peace from God our Father in the Lord Jesus Christ.
3 Bari yabo ya tabbata ga Allah da kuma Uba na Ubangijinmu Yesu Almasihu. Shine Uba na dukan jiyejiyenkai, da kuma Allah na dukan ta'aziya.
Thanks be to the God and Father of our Lord Jesus Christ, the Father of tender mercies and the God of all comfort,
4 Allah yana ta'azantar da mu a cikin dukan wahalarmu, domin mu iya ta'azantar da wadanda ke cikin kowace wahala. Muna ta'azantar da wasu da irin ta'aziyar da Allah ke ta'azantar da mu.
who ever comforts me in all my troubles, so that I may be continually able to comfort those who are in any trouble by the comfort with which God is ever comforting me.
5 Gama kamar yadda wahalhalun Almasihu suka karu domin mu, haka kuma ta'aziyarmu ta yawaita cikin Almasihu.
For just as I have more than my share in the sufferings of the Christ, so also through the Christ I have more than my share of comfort.
6 Amma fa idan muna shan wuya, domin ta'aziyarku ne da cetonku. Haka kuma in mun ta'azantu, domin ta'aziyarku ne. Ta'aziyarku tana aiki ne sosai yayinda kuka jure da irin shan wuyar da mu ma muke sha.
If I am afflicted, it is for your comfort and salvation; and if I am receiving comfort, it is for your comfort - a comfort produced within you by your patient fortitude, under the same sufferings which I also am enduring.
7 Kuma gabagadinmu game da ku tabbatacce ne. Mun kuwa sani kamar yadda kuke tarayya cikin shan wahalhalun, haka kuma za ku yi tarayya cikin ta'aziyyar.
My hope for you is firm; for I know that as you are comrades in my sufferings, so also are you comrades in my comfort.
8 Gama ba mu so ku rasa sani, 'yan'uwa, game da tsananin da ya same mu a Asiya. An murkushe mu gaba daya har fiye da karfin mu, har ma mun fidda zuciya za mu rayu.
Now, brothers, I want you to know about the troubles which befell me in Asia; how I was burdened altogether beyond my strength, so that I renounced all hope even of life itself.
9 Hakika, mun ji hukuncin mutuwa akan mu. Amma wannan ya faru ne domin kada mu dogara ga kanmu, sai dai ga Allah, wanda ke tada matattu.
Indeed, I had in myself, and still have, the sentence of death, in order that I might not rely on myself, but on God who raises the dead to life.
10 Ya kubutar da mu daga wannan mummunan hatsari na mutuwa, kuma zai sake kubutar da mu. Mun kafa begenmu gare shi cewa zai sake kubutar da mu.
He delivered me from such a death, and will deliver me. On him I have set my hopes that he will continue to deliver me,
11 Zai aikata wannan yayinda kuka taimake mu da addu'ar ku. Sa'an nan da dama za su bada godiya a madadin mu don tagomashin alheri da aka yi mana ta wurin addu'o'in mutane masu yawa.
while all of you also are helping me by your prayers; so that from many lips thanksgiving may rise on my behalf for the blessings vouchsafed to me through the intercessions of many.
12 Muna kuwa alfahari da haka: wato shaidar lamirinmu. Gama da kyakkyawan nufi da aminci da ke zuwa daga Allah muka tafiyar da rayuwarmu a Duniya. Mun yi wannan ne musamman tare da ku-ba kuwa cikin hikimar Duniya ba, amma ta wurin alherin Allah.
For this is my proud boast, the testimony of my conscience, that it was in holiness and with pure motives before God, not in worldly wisdom, but in the grace of God, that I have conducted myself in the world, and above all in my relations with you.
13 Bamu rubuta maku abinda ba za ku iya karantawa ko fahimta ba. Ina fata za ku fahimce mu baki daya,
For I am writing to you nothing different from what you read aloud and very well recognize, and I hope will continue to recognize to the very end,
14 kamar yadda kuka fahimce mu kadan yanzu. Daganan a ranar Ubangijinmu Yesu za mu zama dalilinku na alfahari, kamar yadda za ku zama namu.
as some indeed did recognize in part at last, that I am your cause of boasting, just as you will be mine on the Day of Jesus our Lord.
15 Saboda gabagadin da nake da shi game da haka, naso in zo gare ku da farko, domin ku amfana da ziyara sau biyu.
And in this confidence I intended to visit you, before going elsewhere, that you might have a pleasure twice over.
16 Ina da shirin ziyaratar ku a kan hanyata ta zuwa Makidoniya. Daga nan kuma ina da yi niyyar in sake ziyartar ku, a tafiya ta daga Makidoniya, domin ku aike ni a hanyata ta zuwa Yahudiya.
I intended to go by you into Macedonia, and to come again to you from Macedonia, and by you to be sent forward on my way to Judea.
17 Yayinda nake irin wannan tunani, ina shakka ne? Ina shirya abubuwa ne bisa ga magwajin mutum, ta yadda har zan ce “I, i” da “A, a, a, a” a lokaci guda?
In purposing this did I display "caprice"? Or what I purpose do I purpose in a worldly way, so that it may mean either "Yes, yes," or "No, no"?
18 Amma kamar yadda Allah yake amintacce, ba ma fadin ''I'' da ''A'a'' a lokaci guda.
As God is faithful, my message to you is not now "Yes," now "No."
19 Gama Dan Allah, Yesu Almasihu, wanda Silbanus da Sila, da Ni muka shaida maku, ba “I” da “A, a” ba ne. Maimakon haka, Shi “I” ne a kodayaushe.
For Jesus Christ, Son of God, who was proclaimed among you by us, that is, by Silvanus and Timothy and me, was not wavering between "Yes" and "No," but in him is the everlasting "Yes."
20 Gama dukan alkawaran Allah 'I' ne a cikin sa. Haka kuma ta wurin sa muna cewa ''Amin'' zuwa ga daukakar Allah.
For however many are the promises of God, in him they are "Yes." Therefore also through him let the Amen be said by our voices to the glory of God.
21 Yanzu dai Allah ne ya tabbatar da mu da ku a cikin Almasihu, ya kuma kebe mu.
And he who has established me with you in the Anointed One, and has anointed me, is God.
22 Ya sa hatiminsa a kan mu ya kuma ba mu Ruhu a zuciyar mu a matsayin tabbacin abinda zai bamu daga baya.
He has also set his seal upon me, and given me the pledge of his Spirit in my heart.
23 Maimakon haka, na yi kira ga Allah ya zama shaida domina, cewa dalilin dayasa banzo Korintis ba domin in kare ku ne.
But for my part I call God to witness, as my soul shall answer for it, that it was to spare you that I came not to Corinth
24 Ba muna kokarin mu sarrafa yadda bangaskiyar ku za ta zama ba ne. Maimakon haka, muna aiki tare da ku ne domin farincikinku, yayinda kuke tsaye cikin bangaskiyarku.
(not that I am attempting to lord it over your faith, but rather to work with you for your happiness); for your faith is stedfast.

< 2 Korintiyawa 1 >