< 2 Korintiyawa 9 >
1 Game da hidima domin tsarkaka, ya dace in rubuta maku.
There is no need for me to write to you about this ministry of giving to the saints in Jerusalem.
2 Na san marmarinku, wanda na yi fahariya da shi a gaban mutanen Makidoniya. Na gaya masu Akaya sun riga sun shirya tun bara. Kwazon ku ya sa yawancin su sun shiga aiki.
For I know how eager you are to help, and I keep boasting about you to the Macedonians, saying that Achaia has been prepared to give since last year; and your zeal has stirred up most of them.
3 To na aiko maku da 'yan'uwa saboda kada fahariyarmu akanku ta zama a banza, domin kuma ku zauna a shirye, kamar yadda na ce za ku yi.
But I have sent the brothers so that our boasting about you in this matter may not prove to be empty, but that you may be prepared, just as I said you would be.
4 Idan kuwa ba haka ba, idan wani cikin makidoniyawa ya biyoni kuma ya tarar da baku shirya ba, za mu ji kunya-ba ni cewa komai game da ku-domin ina da gabagadi a kan ku.
Otherwise, if any of the Macedonians were to come with me and find you unprepared, we (not to mention you) would be ashamed of this confident boasting.
5 Sai na ga ya dace in turo 'yan'uwa su zo wurin ku kafin lokaci yayi suyi shirye shirye game da gudummuwar da kuka yi alkawari. Wannan ya zama haka ne domin a shirya shi a matsayin bayarwar albarka, ba wani abin kwace ba.
So I thought it necessary to urge the brothers to go on ahead to you and arrange in advance your previously announced blessing, so that this gift of yours may be ready as a blessing and not as something you feel forced to do.
6 Batun shine: wanda ya shuka kadan zai girbi kadan, wanda kuma ya shuka da manufar albarka zai girbi albarka
My point is this: Whoever sows sparingly will also reap sparingly, and whoever sows bountifully will also reap bountifully.
7 Bari kowa ya bayar bisa ga yadda ya yi niyya a zuciyarsa. Kada ya bayar da bacin rai ko kamar dole. Gama Allah yana kaunar mai bayarwa da dadin rai.
Each person should give as he decides in his heart, not with sadness or under compulsion, for God loves a cheerful giver.
8 Allah na da ikon ya sa kowace albarka ta ribanbanya domin ku, domin, a koyaushe, a cikin dukan abubuwa, ku sami duk abinda kuke bukata. Hakan zai kasance domin ku ribabbanya kowanne kyakkyawan aiki.
And God is able to provide you with every blessing in abundance so that you will always have everything you need to abound in every good work.
9 Kamar yadda aka rubuta, ''Ya rarraba arzikinsa, ya bada shi ga matalauta. Adalcinsa ya dawwama har abada.'' (aiōn )
As it is written, “He has distributed freely, he has given to the poor; his righteousness endures forever.” (aiōn )
10 Shi wanda ke bayar da iri ga mai shuka da gurasa domin abinci, zai bayar ya kuma ribabbanya maku iri domin shuka. Zai sa girbin adalcinku ya karu.
Now may he who provides seed to the sower, and bread for food, also multiply your seed for sowing and increase the harvest of your righteousness!
11 Za ku wadata ta kowace hanya domin ku zama masu bayarwa, wannan kuwa zai sa a yi wa Allah godiya ta wurin mu.
May you be enriched in every way to be generous on every occasion, and through us may your generosity produce thanksgiving to God!
12 Aiwatar da wannan hidima ba biyan bukatun tsarkaka kawai take yi ba. Tana kuma ribanbanya zuwa ayyuka masu yawa na bada godiya ga Allah.
For this ministry of giving is not only providing for the needs of the saints in Jerusalem but is also abounding through many thanksgivings to God.
13 Domin an gwada ku an tabbatar da ku akan wannan hidima, za ku kuma daukaka Allah ta wurin biyayyar ku ga shaidar bisharar Almasihu. Za ku kuma daukaka Allah ta wurin yalwar bayarwarku gare su da kowa duka.
By their approval of this ministry, the saints in Jerusalem will glorify God because of your submission to the gospel of Christ that you confess, and also because of your generous contribution to them and to all.
14 Suna marmarin ganin ku, suna kuma yi maku addu'a. Suna yin haka saboda alherin Allah mai girma da ke bisan ku.
They will pray for you with deep affection because of the surpassing grace of God that is upon you.
15 Godiya ga Allah domin kyautarsa wadda ta fi gaban bayyanawa.
Thanks be to God for his indescribable gift!