< 2 Korintiyawa 6 >
1 haka, tundashike muna aiki tare, na roke ku kar ku yi watsi da alherin Allah.
As God's fellow workers, we urge you not to receive the grace of God in vain.
2 Domin ya ce, “A lokacin alheri na saurare ku, kuma a ranar ceto na agaje ku.” Yanzu ne fa, lokacin alheri. Duba, yanzu ne ranar ceto.
For he says, “At a favorable time I listened to yoʋ, and in a day of salvation I helped yoʋ.” Behold, now is the favorable time; now is the day of salvation.
3 Ba mu sa sanadin faduwa a gaban kowannen ku, domin ba mu so hidimarmu ta zama marar amfani.
We are putting no obstacle in anyone's way, so that our ministry may not be discredited.
4 Maimakon haka, mun tabbatar da kan mu ta wurin dukan ayyukanmu, cewa mu bayin Allah ne. Mu bayinsa ne ta wurin yawan jimiri, azaba, kunci, wahala,
Rather, as servants of God we commend ourselves in every way: in great endurance, in afflictions, in hardships, in distresses,
5 duka, kurkuku, tarzoma, cikin aiki tukuru, cikin rashin barci yawancin dare, cikin yunwa,
in beatings, in imprisonments, in riots, in labors, in sleepless nights, in hunger,
6 cikin tsarki, ilimi, hakuri, kirki, cikin Ruhu Mai tsarki, da sahihiyar kauna.
in purity, in knowledge, in patience, in kindness, in the Holy Spirit, in genuine love,
7 Mu bayinsa ne cikin kalmar gaskiya, cikin ikon Allah. Muna kuma da makamai na adalci, a hanun dama da hagu.
in the word of truth, in the power of God; with weapons of righteousness for the right hand and the left,
8 Muna aiki cikin daraja da rashin daraja, kushe da yabo. Ana zargin mu a kan mu mayaudara ne, duk da haka mu masu gaskiya ne.
through glory and dishonor, through bad report and good report; regarded as deceivers, and yet true;
9 Muna aiki kamar ba a san mu ba, gashi kuwa mu sanannu ne. Muna aiki kamar masu mutuwa-duba! -har yanzu muna raye. Muna aiki kamar wadanda aka hukunta, amma ba hukuncin kisa ba.
as unknown, and yet well known; as dying, and behold, we live; as punished, and yet not put to death;
10 Muna aiki kamar muna bakinciki, amma a koyaushe muna farinciki. Muna aiki kamar matalauta, amma muna azurta mutane dayawa. Muna aiki kamar ba mu da komai, amma mun mallaki komai.
as sorrowful, yet always rejoicing; as poor, yet making many rich; as having nothing, yet possessing everything.
11 Mun fada maku dukan gaskiyar, Korantiyawa, kuma zuciyar mu a bude ta ke.
O Corinthians, we have spoken freely to you; our hearts have been opened wide.
12 Ba mu kange zukatan ku ba, ku ne kuka kange zukatanku a gare mu.
You are not restricted by us, but by your own affections.
13 Yanzu a sabanin haka-Ina magana da ku kamar yara-ku bude mana zukatanku.
Now in return—I am speaking as I would to my own children—open your hearts to us.
14 Kada ku yi cudanya da marasa bangaskiya. Wace tarayya ke tsakanin adalci da take shari'a? Ko kuma wace zumunta ce ke tsakanin haske da duhu?
Do not be unequally yoked with unbelievers. For what partnership is there between righteousness and lawlessness? What fellowship does light have with darkness?
15 Wace yarjejeniya ke tsakanin Almasihu da Ibilis? ko kuma me ya hada masu bangaskiya da marasa bangaskiya?
What harmony does Christ have with Belial? What portion does a believer have with an unbeliever?
16 ko wace yarjejeniya ce a tsakanin haikalin Allah da gumaka? Domin kuwa mu haikali ne na Allah mai rai, kamar yadda Allah ya ce: ''Zan zauna a cikin su, in kuma yi tafiya a tsakanin su. Zan zama Allahnsu, su kuma za su zama mutanena.”
And what agreement does the temple of God have with idols? For you are the temple of the living God, just as God said, “I will dwell in them and walk among them. I will be their God, and they will be my people.
17 Sabili da haka, ''Ku fito daga cikin su, kuma ku zama kebabbu,'' in ji Ubangiji. ''Kada ku taba kazamin abu, zan kuma karbe ku.
Therefore, come out from among them and be separate, says the Lord. Touch no unclean thing, and I will receive you.
18 Zan zama Uba a gare ku, ku kuma za ku zama 'ya'ya maza da mata a gare ni,'' in ji Ubangiji Mai iko duka.
I will be a father to you, and you will be sons and daughters to me, says the Lord Almighty.”