< 2 Korintiyawa 3 >
1 Muna fara sake yabon kanmu ne? Ba mu bukatar wasikun shaida daga gare ku ko zuwa gare ku, kamar wadansu mutane, ko ba haka ba?
Recommençons-nous à nous recommander nous-même. Aurions-nous par hasard besoin, comme certaines gens, de lettres de recommandation pour vous, ou de votre part?
2 Ku da kanku kune wasikar shaidarmu, wadda aka rubuta a zukatanmu, wadda Kuma dukan mutane suka sani suke kuma karantawa.
Vous êtes, vous-mêmes, notre lettre de recommandation, une lettre écrite dans notre coeur, connue et lue de tout le monde.
3 Kuma kun nuna ku wasika ne daga Almasihu, wadda muka isar. Ba da tawada aka rubuta ta ba amma da Ruhun Allah mai rai. Ba bisa allunan duwatsu aka rubuta ta ba, amma bisa allunan zukatan mutane.
Il est manifeste que vous êtes une lettre de Christ, tracée par nous, ses ministres, écrite, non avec de l'encre, mais avec l'Esprit du Dieu vivant; non sur des tables de pierre, mais sur des tables de chair, sur vos coeurs.
4 Gama wannan ne gabagadin da muke da shi cikin Allah ta wurin Almasihu.
Cette haute assurance, nous l'avons par Christ en Dieu;
5 Ba mu da wata gwanintar kanmu da za mu yi takamar wani abu ya zo daga gare mu. Maimakon haka, gwanintar mu daga Allah take.
non que nous soyons capables de rien concevoir par nous-même, comme si nous le tirions de notre propre fonds, mais c'est de Dieu que nous vient notre capacité.
6 Allah ne ya maishe mu kwararrun bayi na sabon alkawari. Wannan alkawari ne ba na rubutu ba amma na Ruhu. Gama rubutu kisa yake yi, amma Ruhu rai yake bayarwa.
C'est lui également qui nous a rendu capables d'être ministres d'une nouvelle alliance, non d'une lettre, mais de l'esprit; car la lettre tue, mais l'esprit vivifie.
7 To hidimar da ta haifar da mutuwa- wadda aka rubuta bisa duwatsu- ta zo cikin irin wannan daukaka da har Israila ba su iya kallon fuskar Musa kai tsaye ba. Wannan kuwa saboda daukakar da ke fuskarsa ne, daukaka mai shudewa.
Si le ministère de mort, gravé en lettres sur des tables de pierre, a été entouré d'assez de gloire pour que les fils d'Israël ne pussent fixer leurs regards sur la face de Moïse, à cause de l’éclat passager de son visage,
8 Ina misalin girman daukakar hidimar da Ruhu ke yi?
comment le ministère de l'esprit ne sera-t-il pas revêtu d'une gloire supérieure?
9 Gama idan hidimar kayarwa tana da daukaka, ina misalin yalwatar daukaka da hidimar adalchi za ta yi!
Si le ministère de la condamnation est glorieux, le ministère de la justification le surpasse de beaucoup en gloire:
10 Babu shakka, abin da aka maishe shi mai daukaka a da, ba ya da sauran daukaka a wannan fanni, saboda irin daukakar da ta zarce shi.
sous ce rapport, la gloire dont le premier a été entouré est totalement éclipsée par la gloire infinie du second;
11 To idan har mai shudewar nan ya na da daukaka, ina misalin daukakar da abu na dindindin zai samu!
car, si ce qui se passe n'a pas été sans éclat, ce qui demeure est bien autrement glorieux.
12 Dashike muna da wannan tabbaci, muna da gabagadi sosai.
Ayant donc une telle espérance, nous parlons et nous agissons avec une grande liberté:
13 Ba kamar Musa muke ba wanda ya sa mayafi ya rufe fuskarsa, ta yadda mutanen Isra'ila basu iya kallon karshen daukaka mai shudewa ba kai tsaye.
nous ne faisons pas comme Moïse qui se mettait un voile sur le visage, pour que les fils d'Israël ne vissent pas la fin de ce qui était passager.
14 Amma tunaninsu ya zama a rufe. Har yau kuwa mayafin na nan sa'adda ake karanta tsohon alkawari. Ba a bude shi ba, saboda a cikin Almasihu ne kadai ake kawar da shi.
Malheureusement leur intelligence s'est aveuglée; car, jusqu’à ce jour, ce même voile demeure, lorsqu'ils lisent l'Ancien Testament. Il ne leur est point dévoilé que l'alliance a pris fin en la personne de Christ;
15 Amma har yau, duk lokacin da ake karanta littafin Musa, akwai mayafi shimfide a zukatansu.
mais aujourd'hui encore, un voile est étendu sur leurs coeurs:
16 Amma sa'adda mutum ya juyo wurin Ubangiji, an kawar da mayafin.
quand leurs coeurs se tourneront vers le Seigneur, le voile tombera.
17 To Ubangiji shine Ruhun. Inda Ruhun Ubangiji yake, akwai 'yanci.
Or le Seigneur est l'esprit; et là où est l'esprit du Seigneur, là est la liberté.
18 Dukan mu yanzu, da fuskoki marasa mayafi, muna ganin daukakar Ubangiji. Muna samun sakewa zuwa cikin irin wannan daukaka, daga wannan mataki na daukaka zuwa wani matakin, kamar dai daga wurin Ubangiji, wanda shine Ruhun.
Quant à nous tous, qui, le visage découvert, contemplons en un miroir la gloire du Seigneur, nous sommes transformés en son image, avançant de gloire en gloire, comme on doit l’attendre de l'esprit du Seigneur.