< 2 Korintiyawa 13 >
1 Wannan ne karo na uku da nake zuwa gare ku, ''Ana tabbatar da kowanne zargi ta bakin shaidu biyu ko uku.''
Det er nu tredje Gang, jeg kommer til eder. På to og tre Vidners Mund skal enhver Sag stå fast.
2 Na riga na yi magana a baya da wadanda suka yi zunubi da kuma sauran a lokacin da ina tare da ku karo na biyu, kuma ina sake fadi: Idan na sake zuwa, ba zan raga masu ba.
Jeg har sagt det forud og siger det forud, ligesom da jeg anden Gang var nærværende, således også nu fraværende til dem, som forhen have syndet, og til alle de øvrige, at, om jeg kommer igen, vil jeg ikke skåne,
3 Ina fadi maku wannan ne domin kuna neman shaida ko Almasihu na magana ta bakina. Shi ba kasashshe bane zuwa gare ku. Maimakon haka, Shi mai iko ne a cikin ku.
efterdi I fordre Bevis på, at Kristus taler i mig, han, som ikke er magtesløs over for eder, men er stærk iblandt eder.
4 Domin an gicciye shi cikin kasawa, amma yana da rai ta ikon Allah. Don mu ma kasassu ne a cikin shi, amma za mu rayu tare da shi cikin ikon Allah dake cikinku.
Thi vel blev han korsfæstet i Magtesløshed, men han lever ved Guds Kraft; også vi ere svage i ham, men vi skulle leve med ham ved Guds Kraft over for eder.
5 Ku auna kanku ku gani ko kuna cikin bangaskiya. Ku yi wa kanku gwaji. Ba ku lura da cewa Yesu Almasihu yana cikin ku ba? Yana cikin ku, sai dai in ba a amince da ku ba.
Ransager eder selv, om I ere i Troen; prøver eder selv! Eller erkende I ikke om eder selv, at Jesus Kristus er i eder? ellers ere I udygtige.
6 Gama ina da gabagadin cewa za ku iske an amince da mu.
Men jeg håber, at I skulle kende, at vi ere ikke udygtige.
7 Ina addu'a ga Allah cewa ba za a same ku da laifi ba. Ba wai ina rokon mu bayyana kamar mun ci gwadawar ba. Maimakon haka, ina addu'a ku yi abinda ke dai dai, ko dayake mun yi kamar mun fadi gwadawar.
Men vi bede til Gud om, at I intet ondt må gøre; ikke for at vi må vise os dygtige, men for at I må gøre det gode, vi derimod stå som udygtige.
8 Domin bamu iya yin wani abu na tsayayya da gaskiya ba, sai dai mu yi domin gaskiya.
Thi vi formå ikke noget imod Sandheden, men for Sandheden.
9 Muna farin ciki idan mun kasa ku kuma kun yi karfi. Muna addu'a kuma domin ku kammalu.
Thi vi glæde os, når vi ere magtesløse, og I ere stærke; dette ønske vi også, at I må blive fuldkommengjorte.
10 Na rubuta wadannan abubuwa yayinda ba ni tare da ku, saboda yayin da zan kasance da ku ba zan zamar maku mai fada ba. Ba na so inyi amfani da ikon da Ubangiji ya bani in tsattsaga ku, sai dai in gina ku.
Derfor skriver jeg dette fraværende, for at jeg ikke nærværende skal bruge Strenghed, efter den Magt, som Herren har givet mig til Opbyggelse, og ikke til Nedbrydelse.
11 A karshe, 'yan'uwa, ku yi farinciki, ku yi aiki don sabuntuwa, ku karfafa, ku yarda da juna, ku zauna cikin salama. Kuma Allahn kauna da salama zai kasance tare da ku.
I øvrigt, Brødre! glæder eder, bliver fuldkommengjorte, lader eder formane, værer enige, værer fredsommelige; og Kærlighedens og Fredens Gud skal være med eder.
12 Ku gai da juna da tsattsarkar sumba.
Hilser hverandre med et helligt Kys!
13 Masu bi duka suna gaishe ku.
Alle de hellige hilse eder.
14 Bari alherin Ubangiji Yesu Almasihu, da kaunar Allah, da zumuntar Ruhu Mai Tsarki su kasance tare da ku duka.
Den Herres Jesu Kristi Nåde og Guds Kærlighed og den Helligånds Samfund være med eder alle!