< 2 Korintiyawa 1 >

1 Bulus, manzon Almasihu Yesu ta wurin nufin Allah, da kuma Timoti dan'uwan mu, zuwa ga Ikilisiyar Allah da ke a Korantus, da kuma dukan 'yan'uwa da ke yankin kasar Akaya.
Paul, an Apostle of Jesus Christ by the will of God, and Timothy, a brother, to the church of God which is at Corinth, with all the saints who are in all of Achaia:
2 Bari alheri ya kasance tare da ku da kuma salama ta Allah Ubanmu da kuma Ubangiji Yesu Almasihu.
Grace and peace to you from God our Father and from the Lord Jesus Christ.
3 Bari yabo ya tabbata ga Allah da kuma Uba na Ubangijinmu Yesu Almasihu. Shine Uba na dukan jiyejiyenkai, da kuma Allah na dukan ta'aziya.
Blessed be the God and Father of our Lord Jesus Christ, the Father of mercies and the God of all consolation.
4 Allah yana ta'azantar da mu a cikin dukan wahalarmu, domin mu iya ta'azantar da wadanda ke cikin kowace wahala. Muna ta'azantar da wasu da irin ta'aziyar da Allah ke ta'azantar da mu.
He consoles us in all our tribulation, so that we too may be able to console those who are in any kind of distress, through the exhortation by which we also are being exhorted by God.
5 Gama kamar yadda wahalhalun Almasihu suka karu domin mu, haka kuma ta'aziyarmu ta yawaita cikin Almasihu.
For just as the Passion of Christ abounds in us, so also, through Christ, does our consolation abound.
6 Amma fa idan muna shan wuya, domin ta'aziyarku ne da cetonku. Haka kuma in mun ta'azantu, domin ta'aziyarku ne. Ta'aziyarku tana aiki ne sosai yayinda kuka jure da irin shan wuyar da mu ma muke sha.
So, if we are in tribulation, it is for your exhortation and salvation, or if we are in consolation, it is for your consolation, or if we are exhorted, it is for your exhortation and salvation, which results in the patient endurance of the same passion which we also endure.
7 Kuma gabagadinmu game da ku tabbatacce ne. Mun kuwa sani kamar yadda kuke tarayya cikin shan wahalhalun, haka kuma za ku yi tarayya cikin ta'aziyyar.
So may our hope for you be made firm, knowing that, just as you are participants in the suffering, so also shall you be participants in the consolation.
8 Gama ba mu so ku rasa sani, 'yan'uwa, game da tsananin da ya same mu a Asiya. An murkushe mu gaba daya har fiye da karfin mu, har ma mun fidda zuciya za mu rayu.
For we do not want you to be ignorant, brothers, about our tribulation, which happened to us in Asia. For we were weighed down beyond measure, beyond our strength, so that we became weary, even of life itself.
9 Hakika, mun ji hukuncin mutuwa akan mu. Amma wannan ya faru ne domin kada mu dogara ga kanmu, sai dai ga Allah, wanda ke tada matattu.
But we had within ourselves the response to death, so that we would not have faith in ourselves, but in God, who raises the dead.
10 Ya kubutar da mu daga wannan mummunan hatsari na mutuwa, kuma zai sake kubutar da mu. Mun kafa begenmu gare shi cewa zai sake kubutar da mu.
He has rescued us, and he is rescuing us, from great peril. In him, we hope that he will continue to rescue us.
11 Zai aikata wannan yayinda kuka taimake mu da addu'ar ku. Sa'an nan da dama za su bada godiya a madadin mu don tagomashin alheri da aka yi mana ta wurin addu'o'in mutane masu yawa.
And you are assisting, with your prayers for us, so that from many persons, by that which is a gift in us, thanks may be given through many persons, because of us.
12 Muna kuwa alfahari da haka: wato shaidar lamirinmu. Gama da kyakkyawan nufi da aminci da ke zuwa daga Allah muka tafiyar da rayuwarmu a Duniya. Mun yi wannan ne musamman tare da ku-ba kuwa cikin hikimar Duniya ba, amma ta wurin alherin Allah.
For our glory is this: the testimony of our conscience, which is found in simplicity of heart and in sincerity toward God. And it is not with worldly wisdom, but in the grace of God, that we have conversed with this world, and more abundantly toward you.
13 Bamu rubuta maku abinda ba za ku iya karantawa ko fahimta ba. Ina fata za ku fahimce mu baki daya,
For we write nothing else to you other than what you have read and understood. And I hope that you will continue to understand, even unto the end.
14 kamar yadda kuka fahimce mu kadan yanzu. Daganan a ranar Ubangijinmu Yesu za mu zama dalilinku na alfahari, kamar yadda za ku zama namu.
And just as you have acknowledged us in our role, that we are your glory, so also you are ours, unto the day of our Lord Jesus Christ.
15 Saboda gabagadin da nake da shi game da haka, naso in zo gare ku da farko, domin ku amfana da ziyara sau biyu.
And with this confidence, I wanted to come to you sooner, so that you might have a second grace,
16 Ina da shirin ziyaratar ku a kan hanyata ta zuwa Makidoniya. Daga nan kuma ina da yi niyyar in sake ziyartar ku, a tafiya ta daga Makidoniya, domin ku aike ni a hanyata ta zuwa Yahudiya.
and through you to pass into Macedonia, and to return to you again from Macedonia, and so be led by you on my way to Judea.
17 Yayinda nake irin wannan tunani, ina shakka ne? Ina shirya abubuwa ne bisa ga magwajin mutum, ta yadda har zan ce “I, i” da “A, a, a, a” a lokaci guda?
Then, although I had intended this, did I act lightly? Or in the things that I consider, do I consider according to the flesh, so that there would be, with me, both Yes and No?
18 Amma kamar yadda Allah yake amintacce, ba ma fadin ''I'' da ''A'a'' a lokaci guda.
But God is faithful, so our word, which was set before you, was not, in him, both Yes and No.
19 Gama Dan Allah, Yesu Almasihu, wanda Silbanus da Sila, da Ni muka shaida maku, ba “I” da “A, a” ba ne. Maimakon haka, Shi “I” ne a kodayaushe.
For the Son of God, Jesus Christ, who was preached among you through us, through myself and Sylvanus and Timothy, was not Yes, and No; but was simply Yes in him.
20 Gama dukan alkawaran Allah 'I' ne a cikin sa. Haka kuma ta wurin sa muna cewa ''Amin'' zuwa ga daukakar Allah.
For whatever promises are of God are, in him, Yes. For this reason, too, through him: Amen to God for our glory.
21 Yanzu dai Allah ne ya tabbatar da mu da ku a cikin Almasihu, ya kuma kebe mu.
Now the One who confirms us with you in Christ, and who has anointed us, is God.
22 Ya sa hatiminsa a kan mu ya kuma ba mu Ruhu a zuciyar mu a matsayin tabbacin abinda zai bamu daga baya.
And he has sealed us, and he has placed the pledge of the Spirit in our hearts.
23 Maimakon haka, na yi kira ga Allah ya zama shaida domina, cewa dalilin dayasa banzo Korintis ba domin in kare ku ne.
But I call God as a witness to my soul, that I was lenient with you, in that I did not return to Corinth:
24 Ba muna kokarin mu sarrafa yadda bangaskiyar ku za ta zama ba ne. Maimakon haka, muna aiki tare da ku ne domin farincikinku, yayinda kuke tsaye cikin bangaskiyarku.
not because we have dominion over your faith, but because we are assistants of your joy. For by faith you stand.

< 2 Korintiyawa 1 >