< 1 Tessalonikawa 4 >
1 A karshe, 'yan'uwa, muna karfafa ku kuma muna yi maku gargadi cikin Ubangiji Yesu. Yadda kuka karbi umarni a garemu game da yadda dole za kuyi tafiya kuma ku gamshi Allah, kuma a cikin wannan hanya ku tafi, ku kuma wuce haka.
Saa bede vi eder i øvrigt, Brødre! og formane eder i den Herre Jesus, at som I jo have lært af os, hvorledes I bør vandre og behage Gud, saaledes som I jo ogsaa gøre, at I saaledes maa gøre end yderligere Fremgang.
2 Domin kun san umarnin da muka baku cikin Ubangiji Yesu.
I vide jo, hvilke Bud vi gave eder ved den Herre Jesus.
3 Gama wannan ne nufin Allah: kebewar ku - cewa ku kauce wa zina da fasikanci,
Thi dette er Guds Villie, eders Helliggørelse, at I afholde eder fra Utugt;
4 Cewa kowannenku ya san yadda zai rike mata tasa cikin tsarki da girmamawa.
at hver af eder veed at vinde sig sin egen Hustru i Hellighed og Ære,
5 Kada kayi mata cikin zautuwar sha'awa ( kamar al'ummai wadanda basu san Allah ba).
ikke i Begærings Brynde som Hedningerne, der ikke kende Gud;
6 Kada wani ya kuskura yaci amanar dan'uwansa akan wannan al'amari. Gama Ubangiji mai ramuwa ne akan dukkan wadannan al'amura, Kamar yadda a baya muka yi maku kashedi kuma muka shaida.
at ingen foruretter og bedrager sin Broder i nogen Sag; thi Herren er en Hævner over alt dette, som vi ogsaa før have sagt og vidnet for eder.
7 Gama Allah bai kira mu ga rashin tsarki ba, amma ga rayuwar tsarki.
Thi Gud kaldte os ikke til Urenhed, men til Helliggørelse.
8 Domin haka, duk wanda yaki wannan ba mutane yaki ba, amma Allah, wanda ya bada Ruhunsa Mai Tsarki a gareku.
Derfor altsaa, den, som foragter dette, han foragter ikke et Menneske, men Gud, som ogsaa giver sin Helligaand til eder.
9 Game da kaunar 'yan'uwa, baku bukatar wani ya sake rubuta maku, gama ku da kanku Allah ya koyar da ku kaunar 'yan'uwa.
Men om Broderkærligheden have I ikke nødig, at jeg skal skrive eder til; thi I ere selv oplærte af Gud til at elske hverandre;
10 Ba shakka, kunayin haka ga dukkan 'yan'uwa wadanda ke cikin dukkan Makidoniya. Amma muna gargadin ku 'yan'uwa, kuyi haka bugu da kari.
det gøre I jo ogsaa imod alle Brødrene i hele Makedonien; men vi formane eder, Brødre! til yderligere Fremgang
11 Kuma muna gargadin ku 'yan'uwa kuyi kokari ku zauna a natse, ku kula da al'amuranku, kuyi aiki da hannuwanku, Yadda muka umarceku a baya.
og til at sætte en Ære i at leve stille og varetage hver sit og arbejde med eders Hænder, saaledes som vi bøde eder,
12 Kuyi haka domin tafiyar ku ta zama dai dai a gaban wadanda basu bada gaskiya ba, kuma ya zama baku cikin bukatar komai.
for at I kunne vandre sømmeligt over for dem, som ere udenfor, og for ikke at trænge til nogen.
13 Bamu so ku zama da rashin fahimta ba, 'yan'uwa, game da wadanda sukayi barci, domin kada kuyi bacin rai kamar sauran wadanda basu da tabbacin abinda ke gaba.
Men vi ville ikke, Brødre! at I skulle være uvidende med Hensyn til dem, som sove hen, for at I ikke skulle sørge som de andre, der ikke have Haab.
14 Domin idan mun bada gaskiya Yesu ya mutu kuma ya tashi, haka kuma tare da Yesu Allah zai maido da duk wadanda suka yi barci a cikinsa.
Thi naar vi tro, at Jesus er død og opstanden, da skal ogsaa Gud ligesaa ved Jesus føre de hensovede frem med ham.
15 Gama muna fada maku wannan daga maganar Ubangiji, cewa mu da muke a raye, da aka bari har zuwan Ubangiji, babu shakka ba za mu riga wadanda suka yi barci ba.
Thi dette sige vi eder med Herrens Ord, at vi levende, som blive tilbage til Herrens Tilkommelse, vi skulle ingenlunde komme forud for de hensovede.
16 Gama Ubangiji da kan sa zai sauko daga sama. Zai zo da muryar babban mala'ika, da karar kahon Allah, sai matattu cikin Almasihu su fara tashi.
Thi Herren selv skal stige ned fra Himmelen med et Tilraab, med Overengels Røst og med Guds Basun, og de døde i Kristus skulle opstaa først;
17 Sai mu da muke a raye, wadanda aka bari, tare dasu za'a fyauce mu zuwa cikin gizagizai, mu hadu da Ubangiji cikin sararin sama. Haka zamu cigaba da kasancewa da Ubangiji.
derefter skulle vi levende, som blive tilbage, bortrykkes tillige med dem i Skyer til at møde Herren i Luften; og saa skulle vi altid være sammen med Herren.
18 Domin haka ku ta'azantar da juna da wadannan maganganu.
Saa trøster hverandre med disse Ord!