< 1 Tessalonikawa 1 >

1 Bulus, Sila, da Timoti zuwa ga Ikilisiyar Tassalonikawa cikin Allah Uba da Ubangiji Yesu Almasihu. Alheri da Salama su kasance a gare ku.
Paulus og Silvanus og Timotheus til Thessalonikernes Menighed i Gud Fader og den Herre Jesus Kristus. Nåde være med eder og Fred!
2 Kullum muna bada godiya ga Allah domin ku dukka, kamar yadda muke ambaton ku a addu'o'in mu.
Vi takke Gud altid for eder alle, når vi komme eder i Hu i vore Bønner,
3 Muna tunawa da ku ba fasawa a gaban Allahn mu da Ubanmu kuma ayyukanku na bangaskiya, da kauna. Da hakurin bege na abinda ke gaba cikin Ubangijinmu Yesu Almasihu.
idet vi uafladelig mindes eders Gerning i Troen og eders Arbejde i Kærligheden og eders Udholdenhed i Håbet på vor Herre Jesus Kristus for vor Guds og Faders Åsyn,
4 'Yan'uwa kaunatattu na Allah, Mun san kiran ku,
efterdi vi kende eders Udvælgelse, I af Gud elskede Brødre,
5 yadda bishararmu ta zo gare ku ba ta magana kadai ba, amma da iko, ta wurin Ruhu Mai Tsarki, haka kuma tawurin tabbatarwa. Ta haka kuma, kun san irin mutanen da muke acikin ku kuma domin ku.
at vort Evangelium ikke kom til eder i Ord alene, men også i Kraft og i den Helligånd og i fuld Overbevisning, som I jo vide, hvorledes vi færdedes iblandt eder for eders Skyld.
6 Kun zama masu koyi da mu da kuma Ubangiji, kamar yadda kuka karbi kalmar cikin tsanani mai yawa da murna tawurin Ruhu Mai Tsaki.
Og I ere blevne vore Efterfølgere, ja, Herrens, idet I modtoge Ordet under megen Trængsel med Glæde i den Helligånd,
7 Sakamakon haka, kuka zama abin misali ga dukkan wadanda ke Makidoniya da na Akaya wadanda suka bada gaskiya.
så at I ere blevne et Forbillede for alle de troende i Makedonien og Akaja;
8 Gama daga gare kune maganar Allah ta bazu ko ina, ba kuwa Makidoniya da Akaya kadai ba. A maimako, har ma zuwa ko ina bangaskiyarku cikin Allah ta kai. Don haka, bama bukatar muce maku komai.
thi fra eder har Herrens Ord lydt ud, ikke alene i Makedonien og Akaja, men alle Vegne er eders Tro på Gud kommen ud, så at vi ikke have nødig at tale derom.
9 Domin su da kansu suna bada labarin irin zuwan mu gare ku. Suna fadin yadda kuka juyo ga Allah daga bautar gumaka don ku bautawa Allah mai rai.
Thi de forkynde selv om os, hvordan en Indgang vi vandt hos eder, og hvorledes I vendte om til Gud fra Afguderne for at tjene den levende og sande Gud
10 Suna bayyana cewa kuna jiran bayyanar Dansa daga sama, wanda ya tasar daga matattu. Wannan shine Yesu, wanda ya 'yantad da mu daga fushi mai zuwa.
og vente på hans Søn fra Himlene, hvem han oprejste fra de døde, Jesus, som frier os fra den kommende Vrede.

< 1 Tessalonikawa 1 >