< 1 Bitrus 1 >
1 Bitrus, manzon Yesu Almasihu, zuwa ga zababbu wadanda suke baki, a warwatse cikin Buntus, Galatiya, kappadokiya, Asiya, da Bitiniya.
Petrus, Jesu Christi Apostel, dem utkoradom främlingom, som bo här och der i Ponto, Galatien, Cappadocien, Asien, och Bithynien,
2 Bisa ga rigasanin Allah Uba, Ta wurin tsarkakewar Ruhu, zuwa biyayya da yayyafar jinin Yesu Almasihu. Alheri da salama su yawaita a gareku.
Efter Guds Faders försyn, genom Andans helgelse, till lydnona och Jesu Christi blods stänkelse. Nåd och frid föröke sig i eder.
3 Albarka ga Allah Uban Ubangijinmu Yesu Almasihu. Ta wurin jinkansa mai girma, ya maya haihuwarmu zuwa bege mai rai ta wurin tashin Yesu Almasihu daga matattu.
Välsignad vare Gud, och vårs Herras Jesu Christi Fader, som oss för sin stora barmhertighet hafver födt på nytt till ett lefvandes hopp, genom Jesu Christi uppståndelse ifrå de döda;
4 Zuwa gado marar lalacewa, marar baci, ba kuma zai kode ba. Wanda aka kebe a sama dominku.
Till oförgängeligit, obesmittadt, och ovanskeligit arf; hvilket i himmelen förvaradt är till eder.
5 Ku da ikon Allah ya kiyaye ta wurin bangaskiya domin ceto wanda za'a bayyana a karshen zamanai.
Som med Guds magt bevarens genom trona till salighet, hvilken beredd är, att hon skall uppenbar varda i den yttersta tiden;
6 Cikin wannan kuna murna da yawa, duk da ya ke ya zama wajibi gare ku yanzu ku yi bakin ciki, a cikin jarabobi iri iri.
I hvilkom I eder fröjda skolen, I som nu en liten tid liden bedröfvelse, i margahanda försökelse, hvar så behöfves:
7 Wannan kuwa da nufin a iske aunawar bangaskiyarku ne, bangaskiyar da tafi zinariya daraja, wadda takan lalace ko da an gwada ta da wuta. Wannan ya faru domin bangaskiyan nan taku ta jawo maku yabo da girma da daukaka a bayyanuwar Yesu Almasihu.
På det edor tro skall rättsinnig och mycket kosteligare befunnen varda, än det förgängeliga guld som pröfvas med eld, till lof, pris och äro, när Christus Jesus blifver uppenbar;
8 Wanda kuke kauna, ko da yake baku ganshi ba. Ko da yake baku ganinsa yanzu, duk da haka kun bada gaskiya gare shi murnar da ku ke yi kwarai da farin ciki wanda tafi gaban a fadi cike da daukaka.
Hvilken I älsken, ändock I icke sen honom; den I ock nu tron uppå, och dock icke sen; så skolen I fröjda eder med osägeliga och härliga glädje;
9 Kuna karbar sakamakon bangaskiyarku, ceton rayukanku.
Och få edor tros ändalykt, nämliga själarnas salighet;
10 Annabawan da su ka yi annabcin ceton da ya zama naku su ka yi bidassa suka bincike kuma da himma.
Efter hvilken salighet Propheterne hafva sökt och ransakat, som propheterat hafva om den tillkommande nåd till eder;
11 Sun nemi su san ko wanene da kuma kowanne lokaci ne Ruhun Almasihu da ke cikinsu yake bayyana ma su. Wannan ya faru ne sa'adda yake gaya ma su tun da wuri game da shan wahalar Almasihu da kuma daukakar da zata biyo baya.
Och hafva ransakat, på hvad eller hurudana tid Christi Ande utviste, den i dem var, och tillförene hade betygat de lidande, som i Christo äro, och den härlighet, som derefter följa skulle,
12 An kuwa bayyana wa annabawan cewa ba kansu suke hidimtawa ba, amma ku suke yi wa hidima. Wannan shine abin da suke yi game da abin da aka rigaya aka gaya maku, ta wurin wadanda da Ruhu mai Tsarki ya bishe su. Wanda aka aiko daga sama. Wadannan sune abubuwan da mala'iku ma suka yi marmarin a bayyana masu.
Hvilkom det ock uppenbaradt var: ty de hafva icke sig sjelfvom, utan oss, dermed tjent; hvilke stycker eder nu förkunnad äro, genom dem som eder Evangelium predikat hafva, genom den Helga Anda som sändes af himmelen, hvilket Änglomen ock lyster se.
13 Domin wannan fa ku natsu. Ku yi dammara a hankalinku. Ku kafa begenku sarai akan alherin da za'a kawo maku a lokacin bayyanuwar Yesu Almasihu.
Derföre, begjorder edor sinnes länder, och varer nyktre, och sätter fullkomligit hopp till den nåd som eder tillbuden varder, genom Jesu Christi uppenbarelse,
14 Kamar 'ya'ya masu biyyaya, kada ku biyewa sha'awoyinku na da a zamanin jahilcinku.
Såsom lydaktig barn; och ställer eder icke såsom tillförene, då I uti fåvitsko lefden, efter begärelsen;
15 Amma yadda shi wanda ya kira ku mai tsarki ne, kuma ku zama da tsarki cikin dukkan al'amuranku.
Utan, efter honom, som eder kallat hafver, och helig är, varer ock I helige uti all edor umgängelse.
16 Domin a rubuce yake, “Ku zama da tsarki, gama ni mai tsarki ne.”
Ty det är skrifvet: I skolen vara helige; ty jag är helig.
17 Idan ku na kira bisa gare shi “Uba” shi wanda yake hukuntawa ba da tara ba, amma gwar-gwadon aikin kowane mutum, sai kuyi zaman bakuncinku da tsoro da bangirma.
Och efter I åkallen honom för en Fader, som dömer efter hvars och ens gerning, och hafver intet anseende till personen, så ser till att I, uti detta edart elände, vandren i räddhåga.
18 Kun san cewa ba da azurfa ko zinariya mai lalacewa aka fanshe ku ba, daga halinn wauta da kuka gada daga wurin iyayenku.
Och veter, att I icke med förgängeligit silfver eller guld igenlöste ären ifrån edart fåfänga lefverne, efter fädernas sätt;
19 Maimakon haka an fanshe ku da jinin Almasihu mai daraja, marar aibu kamar na dan rago.
Utan med Christi dyra blod, såsom med ett menlöst och obesmittadt lambs;
20 An zabi Almasihu tun kafin kafawar duniya, amma a karshen zamanu ya bayyanu a gare ku.
Hvilken väl föresedd var för verldenes begynnelse; men uppenbarad i de yttersta tiderna, för edra skull;
21 Ku da kuka bada gaskiya ga Allah ta wurinsa, wanda ya tashe shi daga matattu ya kuma bashi daukaka domin bangaskiyarku da begenku su kasance cikin Allah.
Som genom honom tron på Gud; den honom uppväckt hafver ifrå de döda, och gifvit honom härlighet; på det I skullen hafva tro och hopp till Gud.
22 Da shike kun tsarkake rayukanku cikin biyayyar ku ga gaskiya zuwa ga sahihiyar kauna ta 'yan'uwa, sai ku kaunaci junanku da zuciya mai gaskiya.
Och görer edra själar kyska, i sanningenes lydno genom Andan, till oskrymtad broderlig kärlek; älsker eder storliga inbördes af rent hjerta;
23 da shike an sake hai'huwarku ba daga iri mai lalacewa ba amma daga iri marar rubewa, ta wurin maganar Allah wadda take rayuwa ta kuma dawwama. (aiōn )
Såsom de, som födde äro på nytt; icke af någor förgängelig säd, utan af oförgängelig, som är, af lefvandes Guds ord, det evinnerliga blifver. (aiōn )
24 Gama “dukkan jiki kamar ciyawa yake, dukkan darajarsa kuwa kamar furen ciyawa take. Ciyawa takan yi yaushi, furenta ya kan yankwane ya fadi,
Ty allt kött är såsom gräs, och all menniskos härlighet såsom blomster på gräset; gräset är vissnadt, och blomstret är affallet;
25 amma maganar Ubangiji tabbatacciya ce har abada. “Wannan ita ce maganar bishara wadda akayi maku wa'azinta.” (aiōn )
Men Herrans ord blifver evinnerliga; och det är det ord, som predikadt är ibland eder. (aiōn )