< 1 Bitrus 1 >
1 Bitrus, manzon Yesu Almasihu, zuwa ga zababbu wadanda suke baki, a warwatse cikin Buntus, Galatiya, kappadokiya, Asiya, da Bitiniya.
Peter, an apostle of Jesus Christ, to the elect who are sojourners of the dispersion in Pontus, Galatia, Cappadocia, Roman Asia, and Bithynia,
2 Bisa ga rigasanin Allah Uba, Ta wurin tsarkakewar Ruhu, zuwa biyayya da yayyafar jinin Yesu Almasihu. Alheri da salama su yawaita a gareku.
according to the foreknowledge of God the Father, in the sanctification of the spirit, unto obedience and sprinkling of the blood of Jesus Christ; Grace and peace be multiplied to you.
3 Albarka ga Allah Uban Ubangijinmu Yesu Almasihu. Ta wurin jinkansa mai girma, ya maya haihuwarmu zuwa bege mai rai ta wurin tashin Yesu Almasihu daga matattu.
Blessed be the God and Father of our Lord Jesus Christ, by whose great mercy we have been born anew into a living hope, through the resurrection of Jesus Christ from the dead;
4 Zuwa gado marar lalacewa, marar baci, ba kuma zai kode ba. Wanda aka kebe a sama dominku.
and into an inheritance imperishable and undefiled and fadeless, which has been kept in heaven for you
5 Ku da ikon Allah ya kiyaye ta wurin bangaskiya domin ceto wanda za'a bayyana a karshen zamanai.
who, through faith, are continuously guarded by the power of God for a salvation, ready to be revealed in the last days.
6 Cikin wannan kuna murna da yawa, duk da ya ke ya zama wajibi gare ku yanzu ku yi bakin ciki, a cikin jarabobi iri iri.
Exult in this, though now for a brief moment, if need be, you have suffered many hardships.
7 Wannan kuwa da nufin a iske aunawar bangaskiyarku ne, bangaskiyar da tafi zinariya daraja, wadda takan lalace ko da an gwada ta da wuta. Wannan ya faru domin bangaskiyan nan taku ta jawo maku yabo da girma da daukaka a bayyanuwar Yesu Almasihu.
These are in order that the test of your faith, more precious than gold that is perishable and yet is tested by fire, may redound to praise and glory and honor, at the revelation of Jesus Christ.
8 Wanda kuke kauna, ko da yake baku ganshi ba. Ko da yake baku ganinsa yanzu, duk da haka kun bada gaskiya gare shi murnar da ku ke yi kwarai da farin ciki wanda tafi gaban a fadi cike da daukaka.
Him you love, though you have never seen him; in him you ever believe, though even now you see him not, and you are rejoicing with joy unspeakable and full of glory,
9 Kuna karbar sakamakon bangaskiyarku, ceton rayukanku.
as you continually receive the reward of your faith, even the salvation of your souls.
10 Annabawan da su ka yi annabcin ceton da ya zama naku su ka yi bidassa suka bincike kuma da himma.
Concerning this salvation the Prophets who prophesied regarding the grace intended for you, diligently sought and searched.
11 Sun nemi su san ko wanene da kuma kowanne lokaci ne Ruhun Almasihu da ke cikinsu yake bayyana ma su. Wannan ya faru ne sa'adda yake gaya ma su tun da wuri game da shan wahalar Almasihu da kuma daukakar da zata biyo baya.
They were searching to know to what time, or to what manner of time the Spirit of Christ which was in them kept pointing, when he ever testified beforehand concerning the sufferings of Christ and the glories that would follow.
12 An kuwa bayyana wa annabawan cewa ba kansu suke hidimtawa ba, amma ku suke yi wa hidima. Wannan shine abin da suke yi game da abin da aka rigaya aka gaya maku, ta wurin wadanda da Ruhu mai Tsarki ya bishe su. Wanda aka aiko daga sama. Wadannan sune abubuwan da mala'iku ma suka yi marmarin a bayyana masu.
It was revealed to them that it was not for themselves, but for you, that they were ministering the truths which have now been announced to you, by those who preached the gospel to you, through the help of the Holy Spirit sent forth from heaven - truths into which angels long to look.
13 Domin wannan fa ku natsu. Ku yi dammara a hankalinku. Ku kafa begenku sarai akan alherin da za'a kawo maku a lokacin bayyanuwar Yesu Almasihu.
So then brace up your minds, be steady in spirit, and fix your hope firmly in the grace that is coming to you, at the revelation of Jesus Christ.
14 Kamar 'ya'ya masu biyyaya, kada ku biyewa sha'awoyinku na da a zamanin jahilcinku.
Like obedient children, do not fashion yourselves according to the former passions of your days of ignorance,
15 Amma yadda shi wanda ya kira ku mai tsarki ne, kuma ku zama da tsarki cikin dukkan al'amuranku.
but become yourselves holy in your whole manner of living, as He who has called you is holy,
16 Domin a rubuce yake, “Ku zama da tsarki, gama ni mai tsarki ne.”
as the Scripture says, You shall be holy, because I am holy.
17 Idan ku na kira bisa gare shi “Uba” shi wanda yake hukuntawa ba da tara ba, amma gwar-gwadon aikin kowane mutum, sai kuyi zaman bakuncinku da tsoro da bangirma.
And since you call upon him as Father, who impartially judges each one according to his deeds, pass the time of your sojourning here in reverence.
18 Kun san cewa ba da azurfa ko zinariya mai lalacewa aka fanshe ku ba, daga halinn wauta da kuka gada daga wurin iyayenku.
For you well know that not with perishable things, with silver or gold, were you redeemed from the emptiness of your manner of life, received by tradition from your ancestors;
19 Maimakon haka an fanshe ku da jinin Almasihu mai daraja, marar aibu kamar na dan rago.
but with precious blood, like that of a lamb without spot or blemish, even the blood of Christ.
20 An zabi Almasihu tun kafin kafawar duniya, amma a karshen zamanu ya bayyanu a gare ku.
He was indeed foreknown before the foundation of the world, but was manifested at the end of the times for your sake.
21 Ku da kuka bada gaskiya ga Allah ta wurinsa, wanda ya tashe shi daga matattu ya kuma bashi daukaka domin bangaskiyarku da begenku su kasance cikin Allah.
Through him you believe in God who raised him from the dead and gave him glory; so that your faith and hope are now in God.
22 Da shike kun tsarkake rayukanku cikin biyayyar ku ga gaskiya zuwa ga sahihiyar kauna ta 'yan'uwa, sai ku kaunaci junanku da zuciya mai gaskiya.
Now that by obedience to the truth you have purified your lives for a brotherly love without hypocrisy, you must love one another from your hearts, fervently.
23 da shike an sake hai'huwarku ba daga iri mai lalacewa ba amma daga iri marar rubewa, ta wurin maganar Allah wadda take rayuwa ta kuma dawwama. (aiōn )
For you have been born anew, not of perishable, but of imperishable seed, by the living, lasting word of God. (aiōn )
24 Gama “dukkan jiki kamar ciyawa yake, dukkan darajarsa kuwa kamar furen ciyawa take. Ciyawa takan yi yaushi, furenta ya kan yankwane ya fadi,
For, All flesh is grass And all its glory like the flower of the grass. The grass fades, The flower falls,
25 amma maganar Ubangiji tabbatacciya ce har abada. “Wannan ita ce maganar bishara wadda akayi maku wa'azinta.” (aiōn )
But the word of the Lord abides forever. And this is the word of the gospel which has been told to you. (aiōn )