< 1 Bitrus 1 >
1 Bitrus, manzon Yesu Almasihu, zuwa ga zababbu wadanda suke baki, a warwatse cikin Buntus, Galatiya, kappadokiya, Asiya, da Bitiniya.
Peter, Apostle of Jesus Christ, to the newly-arrived elect of the dispersion in Pontus, Galatia, Cappadocia, Asia, and Bithynia,
2 Bisa ga rigasanin Allah Uba, Ta wurin tsarkakewar Ruhu, zuwa biyayya da yayyafar jinin Yesu Almasihu. Alheri da salama su yawaita a gareku.
in accord with the foreknowledge of God the Father, in the sanctification of the Spirit, with the obedience and the sprinkling of the blood of Jesus Christ: May grace and peace be multiplied for you.
3 Albarka ga Allah Uban Ubangijinmu Yesu Almasihu. Ta wurin jinkansa mai girma, ya maya haihuwarmu zuwa bege mai rai ta wurin tashin Yesu Almasihu daga matattu.
Blessed be the God and Father of our Lord Jesus Christ, who according to his great mercy has regenerated us into a living hope, through the resurrection of Jesus Christ from the dead:
4 Zuwa gado marar lalacewa, marar baci, ba kuma zai kode ba. Wanda aka kebe a sama dominku.
unto an incorruptible and undefiled and unfading inheritance, which is reserved for you in heaven.
5 Ku da ikon Allah ya kiyaye ta wurin bangaskiya domin ceto wanda za'a bayyana a karshen zamanai.
By the power of God, you are guarded through faith for a salvation which is ready to be revealed in the end time.
6 Cikin wannan kuna murna da yawa, duk da ya ke ya zama wajibi gare ku yanzu ku yi bakin ciki, a cikin jarabobi iri iri.
In this, you should exult, if now, for a brief time, it is necessary to be made sorrowful by various trials,
7 Wannan kuwa da nufin a iske aunawar bangaskiyarku ne, bangaskiyar da tafi zinariya daraja, wadda takan lalace ko da an gwada ta da wuta. Wannan ya faru domin bangaskiyan nan taku ta jawo maku yabo da girma da daukaka a bayyanuwar Yesu Almasihu.
so that the testing of your faith, which is much more precious than gold tested by fire, may be found in praise and glory and honor at the revelation of Jesus Christ.
8 Wanda kuke kauna, ko da yake baku ganshi ba. Ko da yake baku ganinsa yanzu, duk da haka kun bada gaskiya gare shi murnar da ku ke yi kwarai da farin ciki wanda tafi gaban a fadi cike da daukaka.
For though you have not seen him, you love him. In him also, though you do not see him, you now believe. And in believing, you shall exult with an inexpressible and glorious joy,
9 Kuna karbar sakamakon bangaskiyarku, ceton rayukanku.
returning with the goal of your faith, the salvation of souls.
10 Annabawan da su ka yi annabcin ceton da ya zama naku su ka yi bidassa suka bincike kuma da himma.
About this salvation, the prophets inquired and diligently searched, those who prophesied about the future grace in you,
11 Sun nemi su san ko wanene da kuma kowanne lokaci ne Ruhun Almasihu da ke cikinsu yake bayyana ma su. Wannan ya faru ne sa'adda yake gaya ma su tun da wuri game da shan wahalar Almasihu da kuma daukakar da zata biyo baya.
inquiring as to what type of condition was signified to them by the Spirit of Christ, when foretelling those sufferings that are in Christ, as well as the subsequent glories.
12 An kuwa bayyana wa annabawan cewa ba kansu suke hidimtawa ba, amma ku suke yi wa hidima. Wannan shine abin da suke yi game da abin da aka rigaya aka gaya maku, ta wurin wadanda da Ruhu mai Tsarki ya bishe su. Wanda aka aiko daga sama. Wadannan sune abubuwan da mala'iku ma suka yi marmarin a bayyana masu.
To them, it was revealed that they were ministering, not for themselves, but for you those things which have now been announced to you through those who have preached the Gospel to you, through the Holy Spirit, who was sent down from heaven to the One upon whom the Angels desire to gaze.
13 Domin wannan fa ku natsu. Ku yi dammara a hankalinku. Ku kafa begenku sarai akan alherin da za'a kawo maku a lokacin bayyanuwar Yesu Almasihu.
For this reason, gird the waist of your mind, be sober, and hope perfectly in the grace that is offered to you in the revelation of Jesus Christ.
14 Kamar 'ya'ya masu biyyaya, kada ku biyewa sha'awoyinku na da a zamanin jahilcinku.
Be like sons of obedience, not conforming to the desires of your former ignorance,
15 Amma yadda shi wanda ya kira ku mai tsarki ne, kuma ku zama da tsarki cikin dukkan al'amuranku.
but in accord with him who has called you: the Holy One. And in every behavior, you yourself must be holy,
16 Domin a rubuce yake, “Ku zama da tsarki, gama ni mai tsarki ne.”
for it is written: “You shall be holy, for I am Holy.”
17 Idan ku na kira bisa gare shi “Uba” shi wanda yake hukuntawa ba da tara ba, amma gwar-gwadon aikin kowane mutum, sai kuyi zaman bakuncinku da tsoro da bangirma.
And if you invoke as Father him who, without showing favoritism to persons, judges according to each one’s work, then act in fear during the time of your sojourning here.
18 Kun san cewa ba da azurfa ko zinariya mai lalacewa aka fanshe ku ba, daga halinn wauta da kuka gada daga wurin iyayenku.
For you know that it was not with corruptible gold or silver that you were redeemed away from your useless behavior in the traditions of your fathers,
19 Maimakon haka an fanshe ku da jinin Almasihu mai daraja, marar aibu kamar na dan rago.
but it was with the precious blood of Christ, an immaculate and undefiled lamb,
20 An zabi Almasihu tun kafin kafawar duniya, amma a karshen zamanu ya bayyanu a gare ku.
foreknown, certainly, before the foundation of the world, and made manifest in these latter times for your sake.
21 Ku da kuka bada gaskiya ga Allah ta wurinsa, wanda ya tashe shi daga matattu ya kuma bashi daukaka domin bangaskiyarku da begenku su kasance cikin Allah.
Through him, you have been faithful to God, who raised him up from the dead and gave him glory, so that your faith and hope would be in God.
22 Da shike kun tsarkake rayukanku cikin biyayyar ku ga gaskiya zuwa ga sahihiyar kauna ta 'yan'uwa, sai ku kaunaci junanku da zuciya mai gaskiya.
So chastise your souls with the obedience of charity, in fraternal love, and love one another from a simple heart, attentively.
23 da shike an sake hai'huwarku ba daga iri mai lalacewa ba amma daga iri marar rubewa, ta wurin maganar Allah wadda take rayuwa ta kuma dawwama. (aiōn )
For you have been born again, not from corruptible seed, but from what is incorruptible, from the Word of God, living and remaining for all eternity. (aiōn )
24 Gama “dukkan jiki kamar ciyawa yake, dukkan darajarsa kuwa kamar furen ciyawa take. Ciyawa takan yi yaushi, furenta ya kan yankwane ya fadi,
For all flesh is like the grass and all its glory is like the flower of the grass. The grass withers and its flower falls away.
25 amma maganar Ubangiji tabbatacciya ce har abada. “Wannan ita ce maganar bishara wadda akayi maku wa'azinta.” (aiōn )
But the Word of the Lord endures for eternity. And this is the Word that has been evangelized to you. (aiōn )