< 1 Bitrus 4 >

1 Saboda haka, tunda yake Almasihu ya sha wuya a jiki, muma mu sha damara da wannan ra'ayi. Duk wanda ya sha wuya a jiki ya daina aikata zunubi.
Efterdi da Kristus har lidt i Kødet, saa skulle ogsaa I væbne eder med det samme Sind (thi den, som har lidt i Kødet, er hørt op med Synd),
2 Wannan mutum kuma baya kara zaman biye wa muguwar sha'awar mutumtaka, amma sai dai nufin Allah dukkan sauran kwanakinsa a duniya.
saa at I ikke fremdeles leve den øvrige Tid i Kødet efter Menneskers Lyster, men efter Guds Villie.
3 Gama lokaci ya wuce da zamu yi abin da al'ummai suke son yi, wato fajirci, mugayen sha'awace-sha'awace, da buguwa da shashanci da shaye-shaye da bautar gumaku da abubuwan kyama.
Thi det er nok i den forbigangne Tid at have gjort Hedningernes Villie, idet I have vandret i Uterlighed, Lyster, Fylderi, Svir, Drik og skammelig Afgudsdyrkelse;
4 Suna tunanin bakon abu ku ke yi da ba kwa hada kai tare da su yanzu a yin wadannan abubuwa, sai suna zarginku.
hvorfor de forundre sig og spotte, naar I ikke løbe med til den samme Ryggesløshedens Pøl;
5 Za su bada lissafi ga wanda yake a shirye ya shari'anta masu rai da matattu.
men de skulle gøre ham Regnskab, som er rede til at dømme levende og døde.
6 Shi yasa aka yi wa matattu wa'azin bishara, cewa ko da shike anyi masu shari'a cikin jikunan mutane, su rayu bisa ga Allah a ruhu.
Thi derfor blev Evangeliet forkyndt ogsaa for døde, for at de vel skulde være dømte paa Menneskers Vis i Kødet, men leve paa Guds Vis i Aanden.
7 Karshen dukkan abubuwa yana gabatowa. Saboda haka, ku zama natsatsu, ku natsu cikin tunaninku domin yin addu'oi.
Men alle Tings Ende er kommen nær; værer derfor aarvaagne og ædrue til Bønner!
8 Gaba da kome, ku himmatu wajen kaunar juna, domin kauna bata neman tona zunuban wadansu.
Haver fremfor alt en inderlig, Kærlighed til hverandre; thi „Kærlighed skjuler en Mangfoldighed af Synder.”
9 Ku yi wa juna bakunta da abubuwa nagari ba tare da gunaguni ba.
Værer gæstfrie imod hverandre uden Knurren.
10 Yadda kowanne dayanku ya sami baiwa, kuyi amfani da su domin ku kyautata wa juna, kamar masu rikon amanar bayebaye na Allah, wanda ya ba mu hannu sake.
Eftersom enhver har faaet en Naadegave, skulle I tjene hverandre dermed som gode Husholdere over Guds mangfoldige Naade.
11 Idan wani yana yin wa'azi, ya zamana fadar Allah ya ke fadi, idan wani yana hidima, ya yi da karfin da Allah ya ba shi, domin cikin dukkan abubuwa a daukaka Allah ta wurin Yesu Almasihu. Daukaka da iko nasa ne har abada abadin. Amin. (aiōn g165)
Taler nogen, han tale som Guds Ord; har nogen en Tjeneste, han tjene, efter som Gud forlener ham Styrke dertil, for at Gud maa æres i alle Ting ved Jesus Kristus, hvem Herligheden og Magten tilhører i Evighedernes Evigheder! Amen. (aiōn g165)
12 Ya kaunatattu, kada ku zaci cewa matsananciyar wahalar da ta zo ta gwada ku bakon abu ne, ko kuma wani bakon abu ne yake faruwa a gareku.
I elskede! undrer eder ikke over den Ild, som brænder iblandt eder til eders Prøvelse, som om der hændtes eder noget underligt;
13 Amma muddin kuna tarayya da Almasihu cikin wahalarsa, ku yi murna, domin kuyi farin ciki da murna sa'adda za a bayyana daukakarsa.
men glæder eder i samme Maal, som I have Del i Kristi Lidelser, for at I ogsaa kunne glæde og fryde eder ved hans Herligheds Aabenbarelse.
14 Idan ana zargin ku sabili da sunan Almasihu, ku masu albarka ne, domin Ruhun daukaka da Ruhun Allah ya tabbata a kanku.
Dersom I haanes for Kristi Navns Skyld, ere I salige; thi Herlighedens og Guds Aand hviler over eder.
15 Amma kada kowannen ku ya sha wahala sabo da horon shi mai kisan kai ne, ko barawo, ko mamugunci, ko mai shisshigi.
Thi ingen af eder bør lide som Morder eller Tyv eller Ugerningsmand eller som en, der blander sig i anden Mands Sager;
16 Amma in wani yana shan wahala sabili da shi na Almasihu ne, kada ya ji kunya, amma ya daukaka Allah a wannan sunan.
men lider han som en Kristen, da skamme han sig ikke, men prise Gud for dette Navn!
17 Domin lokaci ya yi da shari'a za ta fara daga gidan iyalin Allah. Idan kuwa za a fara da mu, menene karshen wadanda suka ki biyayya da bisharar Allah?
Thi det er Tiden til, at Dommen skal begynde med Guds Hus; men begynder den først med os, hvad Ende vil det da faa med dem, som ere genstridige imod Guds Evangelium?
18 Idan mutum, “mai adalci ya tsira da kyar, to, me zai faru da marar bin Allah da mai zunubi kuma?”
Og dersom den retfærdige med Nød og neppe bliver frelst, hvor skal da den ugudelige og Synderen blive af?
19 Sabo da haka bari wadanda suke shan wuya bisa ga nufin Allah, su mika rayukansu ga amintaccen Mahalicci suna kuma yin ayyuka nagari.
Derfor skulle ogsaa de, som lide efter Guds Villie, befale den trofaste Skaber deres Sjæle, idet de gøre det gode.

< 1 Bitrus 4 >