< 1 Bitrus 3 >
1 Haka ku kuma da kuke matan aure, kuyi biyayya da na ku mazajen, domin in har wadansunsu basa biyayya da maganar Allah, halin matansu ya shawo kansu ba tare da magana ba,
Ye women likewise, be subject to your own husbands, that if any believe not the word, they may yet without the word be gained over by the deportment of the wives,
2 Domin sun ga tsattsakan halinku da ladabinku.
beholding your chaste conversation in the fear of God.
3 Haka ma adonku kar ya zama na kwalliyar waje kitson kai, kayan zinariya ko tufafi masu kawa.
Whose adorning, let it not be that without, of plaiting the hair, and putting on of gold, or wearing fine clothes;
4 Amma bari adon ya zama na mutum na cikin zuciya, kuma adon ya zama kyan nan marar dushewa, na kamun kai da natsatsen ruhu, wanda yake da daraja a gaban Allah.
but the hidden man of the heart, in the incorruptible ornament of a meek and quiet spirit, which is in the sight of God of great price.
5 Haka tsarkakan mata su ka yi ado kamar haka. Suka dogara ga Allah suka yi biyayya ga mazajensu.
For so also formerly the holy women, who hoped in God, adorned themselves, being submissive to their husbands; as Sarah obeyed Abraham, calling him her lord:
6 Ta haka Saratu ta yi biyayya ga Ibrahim ta kira shi “ubangiji”. Yanzu ku 'ya'yantane in dai kun yi aiki nagari, idan kuma ba ku ji tsoron wahala ba.
whose daughters ye are, if ye do well, and are not terrified with any sinful fear.
7 Kamar yadda na fada wa matan aure haka ma mazaje, ku zauna da mata da sanin su raunana ne abokan tarayya ne na karbar baiwar rayuwa. Ku dinga yin haka domin a rika jin addu'oinku.
Ye husbands likewise, dwell with them according to knowledge, yielding due respect to the wife as the weaker vessel, and as joint-heirs of the grace of life; that your prayers be not hindered.
8 Daga karshe, dukanku ku hada hankulanku, ku zama masu juyayi, masu kauna kamar 'yan'uwa, masu taushin zuciya, masu tawali'u.
Finally, my beloved, be unanimous, be sympathizing, love as brethren, be compassionate, be courteous:
9 Kada ku rama mugunta da mugunta ko zagi da zagi. A maimakon haka ku cigaba da sa albarka, gama sabili da haka ne musamman aka kiraye ku, domin ku gaji albarka.
not returning evil for evil, or reproach for reproach: but on the contrary blessing even those that curse you: knowing ye are called unto this, that ye may obtain a blessing.
10 “Wanda duk yake so ya more a rayuwarsa ya kuma ga kwanaki masu alheri, to fa, ya kame harshen sa daga mugunta da lebensa daga maganganun yaudara.
"For he that would desire life, and see good days, let him refrain his tongue from evil, and his lips that they speak no guile;
11 Ya rabu da mugunta ya aikata abin da ke nagari. Bari ya nemi zaman salama ya kuma dimanceta.
let him turn away from evil, and do good:
12 Idanun Ubangiji suna duban adalai, kunnuwansa kuma suna sauraron roke rokensu. Amma fuskar Ubangiji tana gaba da masu aikata mugunta.”
let him seek peace, and pursue it: for the eyes of the Lord are upon the righteous, and his ears are open to their prayer: but the face of the Lord is against them that do evil."
13 Wanene ya isa ya cuce ku idan kun himmatu ga yin abin da ke nagari?
And who will hurt you, if ye be imitators of Him that is good?
14 Amma idan kuna shan wuya saboda adalci, ku masu albarka ne. Kada ku ji tsoron abin da su ke tsoro. Kada ku damu.
But if ye should even suffer for righteousness sake, happy are ye: and therefore be not afraid of their menaces, neither be troubled; but sanctify the Lord God in your hearts:
15 Maimakon haka, ku kebe Ubangiji a cikin zukatanku cewa shi mai tsarki ne. Kullum ku zauna da shiri domin ku amsa wa mai tambayar ku dalilin sa begenku ga Allah. Amma fa kuyi haka tare da tawali'u da bangirma.
and be always ready to answer every one that asketh you a reason of the hope that is in you, with meekness and reverence:
16 Ku zama da tsatsakan lamiri domin mutanen da ke zargin rayuwarku mai kyau cikin Almasihu, su ji kunya domin suna maganar gaba da ku kamar ku mugaye ne.
having a good conscience, that whereas they speak against you as evil-doers, they may be ashamed who calumniate your good conversation in Christ.
17 Ya fi kyau, a sha wuya akan aiki nagari, idan nufin Allah ne, da a sha wuya sabili da mugun aiki.
For it is better (if it be the will of God) to suffer for doing good than for doing evil.
18 Almasihu ya sha wahala sau daya tak sabili da zunubai. Shi da ya ke mai adalci ya sha wahala domin mu marasa adalci, domin ya kawo mu ga Allah. Aka kashe shi cikin jiki, amma aka rayar da shi cikin Ruhu.
As Christ also once suffered for sins, the just for the unjust (that He might introduce us to God) being indeed put to death in the flesh, but raised to life by the Spirit:
19 A Ruhu ne, ya je ya yi wa'azi ga ruhohin da ke a yanzu cikin kurkuku.
by which also He went and preached to the spirits now in prison;
20 Sun yi rashin biyayya ne sa'adda hakurin Allah yake jiransu a lokacin Nuhu a zamanin sassaka jirgin ruwa, sai Allah ya tsirar da mutane kalilan wato rayuka takwas daga cikin ruwa.
who of old were disobedient, when the long-suffering of God waited in the days of Noah, while the ark was preparing; wherein a few, that is eight souls, were saved by water.
21 Wannan kwatancin baftismar da take cetonmu yanzu ne, ba kamar ta wanke Dauda daga jiki ba, sai dai ta rokon Allah da lamiri mai kyau ta wurin tashin Yesu Almasihu daga matattu.
The resemblance of which, even baptism, doth also now save us, (not the outward cleansing of filth from the flesh, but the answer of a good conscience towards God) by the resurrection of Jesus Christ,
22 Ya hau sama. Yana dama ga Allah. Mala'iku, da mulkoki da masu iko dole su yi masa biyayya.
who is gone into heaven and is at the right hand of God, angels and authorities and powers being made subject to Him.