< 1 Bitrus 1 >

1 Bitrus, manzon Yesu Almasihu, zuwa ga zababbu wadanda suke baki, a warwatse cikin Buntus, Galatiya, kappadokiya, Asiya, da Bitiniya.
Peter an apostle of Jesus Christ to the strangers who are dispersed through Pontus, Galatia, Cappadocia,
2 Bisa ga rigasanin Allah Uba, Ta wurin tsarkakewar Ruhu, zuwa biyayya da yayyafar jinin Yesu Almasihu. Alheri da salama su yawaita a gareku.
Asia, and Bithynia, chosen according to the fore-knowledge of God, through sanctification of the Spirit, unto obedience, and to the sprinkling of the blood of Jesus Christ, ---may grace and peace be multiplied unto you.
3 Albarka ga Allah Uban Ubangijinmu Yesu Almasihu. Ta wurin jinkansa mai girma, ya maya haihuwarmu zuwa bege mai rai ta wurin tashin Yesu Almasihu daga matattu.
Blessed be the God and Father of our Lord Jesus Christ, who according to his abundant mercy hath regenerated us to a lively hope, by the resurrection of Jesus Christ from the dead,
4 Zuwa gado marar lalacewa, marar baci, ba kuma zai kode ba. Wanda aka kebe a sama dominku.
to an inheritance incorruptible, undefiled, and unfading, reserved in heaven for you,
5 Ku da ikon Allah ya kiyaye ta wurin bangaskiya domin ceto wanda za'a bayyana a karshen zamanai.
who are kept by the power of God through faith unto salvation ready to be revealed in the last time.
6 Cikin wannan kuna murna da yawa, duk da ya ke ya zama wajibi gare ku yanzu ku yi bakin ciki, a cikin jarabobi iri iri.
In which ye rejoice, tho' now for a little while, if need be, ye are grieved through various trials.
7 Wannan kuwa da nufin a iske aunawar bangaskiyarku ne, bangaskiyar da tafi zinariya daraja, wadda takan lalace ko da an gwada ta da wuta. Wannan ya faru domin bangaskiyan nan taku ta jawo maku yabo da girma da daukaka a bayyanuwar Yesu Almasihu.
That the proof of your faith, which is much more precious than of gold, (that perisheth, though tried by fire) may be found unto praise, and honor, and glory, when Jesus Christ shall be revealed:
8 Wanda kuke kauna, ko da yake baku ganshi ba. Ko da yake baku ganinsa yanzu, duk da haka kun bada gaskiya gare shi murnar da ku ke yi kwarai da farin ciki wanda tafi gaban a fadi cike da daukaka.
whom having not seen ye love; in whom, though now ye see Him not, yet believing ye rejoice with joy ineffable and full of glory; receiving the end of your faith,
9 Kuna karbar sakamakon bangaskiyarku, ceton rayukanku.
even the salvation of your souls:
10 Annabawan da su ka yi annabcin ceton da ya zama naku su ka yi bidassa suka bincike kuma da himma.
concerning which salvation the prophets, who prophesied of the grace to be conferred on you, enquired and diligently sought after it:
11 Sun nemi su san ko wanene da kuma kowanne lokaci ne Ruhun Almasihu da ke cikinsu yake bayyana ma su. Wannan ya faru ne sa'adda yake gaya ma su tun da wuri game da shan wahalar Almasihu da kuma daukakar da zata biyo baya.
searching what, or what manner of time the Spirit of Christ in them did declare in testifying beforehand the sufferings that were to come upon Christ, and the glories following them:
12 An kuwa bayyana wa annabawan cewa ba kansu suke hidimtawa ba, amma ku suke yi wa hidima. Wannan shine abin da suke yi game da abin da aka rigaya aka gaya maku, ta wurin wadanda da Ruhu mai Tsarki ya bishe su. Wanda aka aiko daga sama. Wadannan sune abubuwan da mala'iku ma suka yi marmarin a bayyana masu.
to whom it was revealed, that it was not to themselves, but to us they ministered these things, which are now declared unto you by them that have preached the gospel unto you, through the holy Spirit sent down from heaven; which things the angels desire to look into.
13 Domin wannan fa ku natsu. Ku yi dammara a hankalinku. Ku kafa begenku sarai akan alherin da za'a kawo maku a lokacin bayyanuwar Yesu Almasihu.
Wherefore girding up the loins of your mind, be sober, and stedfastly hope for the grace to be conferred upon you at the appearing of Jesus Christ;
14 Kamar 'ya'ya masu biyyaya, kada ku biyewa sha'awoyinku na da a zamanin jahilcinku.
as children of obedience, not conforming yourselves to the former lusts in your ignorance:
15 Amma yadda shi wanda ya kira ku mai tsarki ne, kuma ku zama da tsarki cikin dukkan al'amuranku.
but as He who hath called you is holy, be ye also holy in all your conversation: since it is written,
16 Domin a rubuce yake, “Ku zama da tsarki, gama ni mai tsarki ne.”
Be ye holy, for I am holy.
17 Idan ku na kira bisa gare shi “Uba” shi wanda yake hukuntawa ba da tara ba, amma gwar-gwadon aikin kowane mutum, sai kuyi zaman bakuncinku da tsoro da bangirma.
And if ye call upon the Father, who without respect of persons judgeth according to every man's work, pass the time of your sojourning here in fear:
18 Kun san cewa ba da azurfa ko zinariya mai lalacewa aka fanshe ku ba, daga halinn wauta da kuka gada daga wurin iyayenku.
knowing that ye were redeemed from your vain conversation learned by tradition from your fathers, not with corruptible things, as silver and gold;
19 Maimakon haka an fanshe ku da jinin Almasihu mai daraja, marar aibu kamar na dan rago.
but with the precious blood of Christ as of a lamb without blemish and without spot:
20 An zabi Almasihu tun kafin kafawar duniya, amma a karshen zamanu ya bayyanu a gare ku.
who was indeed appointed before the foundation of the world, but manifested in these last times, for your sakes,
21 Ku da kuka bada gaskiya ga Allah ta wurinsa, wanda ya tashe shi daga matattu ya kuma bashi daukaka domin bangaskiyarku da begenku su kasance cikin Allah.
who through Him trust in God that raised Him from the dead, and gave Him glory, that your faith and hope might be fixed in God.
22 Da shike kun tsarkake rayukanku cikin biyayyar ku ga gaskiya zuwa ga sahihiyar kauna ta 'yan'uwa, sai ku kaunaci junanku da zuciya mai gaskiya.
Having therefore purified your souls by obedience to the truth, through the Spirit, to brotherly love unfeigned, love one another with a pure heart fervently:
23 da shike an sake hai'huwarku ba daga iri mai lalacewa ba amma daga iri marar rubewa, ta wurin maganar Allah wadda take rayuwa ta kuma dawwama. (aiōn g165)
being regenerated not of corruptible seed, but of incorruptible, by the word of God which liveth and abideth for ever. (aiōn g165)
24 Gama “dukkan jiki kamar ciyawa yake, dukkan darajarsa kuwa kamar furen ciyawa take. Ciyawa takan yi yaushi, furenta ya kan yankwane ya fadi,
For all flesh is as grass, and all the glory of man as the flower of grass: the grass withereth, and the flower thereof falleth away;
25 amma maganar Ubangiji tabbatacciya ce har abada. “Wannan ita ce maganar bishara wadda akayi maku wa'azinta.” (aiōn g165)
but the word of the Lord abideth for ever. And this is the word which is preached to you in the gospel. (aiōn g165)

< 1 Bitrus 1 >