< 1 Bitrus 1 >
1 Bitrus, manzon Yesu Almasihu, zuwa ga zababbu wadanda suke baki, a warwatse cikin Buntus, Galatiya, kappadokiya, Asiya, da Bitiniya.
Peter, an apostle of Jesus Christ, to the elect sojourners of the Dispersion of Pontus, Galatia, Cappadocia, Asia, and Bithynia,
2 Bisa ga rigasanin Allah Uba, Ta wurin tsarkakewar Ruhu, zuwa biyayya da yayyafar jinin Yesu Almasihu. Alheri da salama su yawaita a gareku.
according to the foreknowledge of God the Father, through sanctification of the Spirit, unto obedience and sprinkling of the blood of Jesus Christ. Grace to you, and peace, be multiplied.
3 Albarka ga Allah Uban Ubangijinmu Yesu Almasihu. Ta wurin jinkansa mai girma, ya maya haihuwarmu zuwa bege mai rai ta wurin tashin Yesu Almasihu daga matattu.
Blessed is the God and Father of our Lord Jesus Christ, the one having according to his great mercy begotten us again into a living hope through the resurrection of Jesus Christ from the dead,
4 Zuwa gado marar lalacewa, marar baci, ba kuma zai kode ba. Wanda aka kebe a sama dominku.
unto an inheritance incorruptible, and undefiled, and never fading, having been kept in the heavens unto you,
5 Ku da ikon Allah ya kiyaye ta wurin bangaskiya domin ceto wanda za'a bayyana a karshen zamanai.
who are preserved by the power of God through faith unto the salvation ready to be revealed in the last time.
6 Cikin wannan kuna murna da yawa, duk da ya ke ya zama wajibi gare ku yanzu ku yi bakin ciki, a cikin jarabobi iri iri.
In whom you rejoice, if however it is needful, being grieved a little while among manifold temptations: in order
7 Wannan kuwa da nufin a iske aunawar bangaskiyarku ne, bangaskiyar da tafi zinariya daraja, wadda takan lalace ko da an gwada ta da wuta. Wannan ya faru domin bangaskiyan nan taku ta jawo maku yabo da girma da daukaka a bayyanuwar Yesu Almasihu.
that the trial of your faith, which is more precious than gold that perishes, however being tried by the fire, may be found unto praise and glory and honor in the revelation of Jesus Christ:
8 Wanda kuke kauna, ko da yake baku ganshi ba. Ko da yake baku ganinsa yanzu, duk da haka kun bada gaskiya gare shi murnar da ku ke yi kwarai da farin ciki wanda tafi gaban a fadi cike da daukaka.
whom you not seeing, love with divine love; on whom, not looking, but believing, you rejoice with joy unspeakable and full of glory:
9 Kuna karbar sakamakon bangaskiyarku, ceton rayukanku.
receiving the end of your faith, the salvation of your souls.
10 Annabawan da su ka yi annabcin ceton da ya zama naku su ka yi bidassa suka bincike kuma da himma.
Concerning which salvation the prophets, who prophesied concerning the grace towards you, sought out and investigated,
11 Sun nemi su san ko wanene da kuma kowanne lokaci ne Ruhun Almasihu da ke cikinsu yake bayyana ma su. Wannan ya faru ne sa'adda yake gaya ma su tun da wuri game da shan wahalar Almasihu da kuma daukakar da zata biyo baya.
searching into what, or what kind of time the Spirit of Christ who was in them, witnessing the sufferings towards Christ, and the glories after these, did show:
12 An kuwa bayyana wa annabawan cewa ba kansu suke hidimtawa ba, amma ku suke yi wa hidima. Wannan shine abin da suke yi game da abin da aka rigaya aka gaya maku, ta wurin wadanda da Ruhu mai Tsarki ya bishe su. Wanda aka aiko daga sama. Wadannan sune abubuwan da mala'iku ma suka yi marmarin a bayyana masu.
to whom it was revealed, because they were ministering not these things for themselves, but for you, which are now proclaimed unto you by those who preach to you the gospel with the Holy Ghost having been sent from heaven; into which things the angels desire to look down.
13 Domin wannan fa ku natsu. Ku yi dammara a hankalinku. Ku kafa begenku sarai akan alherin da za'a kawo maku a lokacin bayyanuwar Yesu Almasihu.
Therefore having girded up the loins of your minds, being perfectly sober, hope unto the grace which is conferred on you in the revelation of Jesus Christ.
14 Kamar 'ya'ya masu biyyaya, kada ku biyewa sha'awoyinku na da a zamanin jahilcinku.
As children of obedience, not being fashioned after your former lusts in ignorance:
15 Amma yadda shi wanda ya kira ku mai tsarki ne, kuma ku zama da tsarki cikin dukkan al'amuranku.
but according to the Holy One who has called you. Be ye also holy in all your deportment;
16 Domin a rubuce yake, “Ku zama da tsarki, gama ni mai tsarki ne.”
because it has been written, Ye shall be holy; because I am holy.
17 Idan ku na kira bisa gare shi “Uba” shi wanda yake hukuntawa ba da tara ba, amma gwar-gwadon aikin kowane mutum, sai kuyi zaman bakuncinku da tsoro da bangirma.
And if you call upon the Father, the One judging without respect of persons according to the work of each, pass the time of your sojourn with fear,
18 Kun san cewa ba da azurfa ko zinariya mai lalacewa aka fanshe ku ba, daga halinn wauta da kuka gada daga wurin iyayenku.
knowing that you have been redeemed from your depraved character transmitted from your ancestors, not by corruptible things, silver or gold,
19 Maimakon haka an fanshe ku da jinin Almasihu mai daraja, marar aibu kamar na dan rago.
but by the precious blood of Christ, as a lamb without blemish and spotless:
20 An zabi Almasihu tun kafin kafawar duniya, amma a karshen zamanu ya bayyanu a gare ku.
foreknown indeed before the foundation of the world, but having been made manifest at the last of the times for the sake of you,
21 Ku da kuka bada gaskiya ga Allah ta wurinsa, wanda ya tashe shi daga matattu ya kuma bashi daukaka domin bangaskiyarku da begenku su kasance cikin Allah.
who through him are faithful toward God, who raised him from the dead, and gave him glory; so that your faith and hope are toward God.
22 Da shike kun tsarkake rayukanku cikin biyayyar ku ga gaskiya zuwa ga sahihiyar kauna ta 'yan'uwa, sai ku kaunaci junanku da zuciya mai gaskiya.
Having purified your souls through obedience of the truth unto unhypocritical, brotherly love, fervently from the heart love one another with divine love:
23 da shike an sake hai'huwarku ba daga iri mai lalacewa ba amma daga iri marar rubewa, ta wurin maganar Allah wadda take rayuwa ta kuma dawwama. (aiōn )
having been begotten again, not of corruptible seed, but incorruptible, through the word of God, who lives and abides. (aiōn )
24 Gama “dukkan jiki kamar ciyawa yake, dukkan darajarsa kuwa kamar furen ciyawa take. Ciyawa takan yi yaushi, furenta ya kan yankwane ya fadi,
Therefore all flesh is as grass, and all its glory as the flower of grass: the grass is withered, and the flower fell off;
25 amma maganar Ubangiji tabbatacciya ce har abada. “Wannan ita ce maganar bishara wadda akayi maku wa'azinta.” (aiōn )
but the word of the Lord abides forever. And this is the word which has been preached unto you. (aiōn )