< 1 Yohanna 3 >

1 Dubi irin kaunar da Allah ya bamu, har da za a kira mu 'ya'yan Allah, haka muke kuwa. Saboda wannan dalili ne duniya bata san muba, saboda bata san shi ba.
Think what love the Father has shown us in allowing us to be called ‘Children of God’; as indeed we are. The reason why the world does not know us is that it has not learned to know him.
2 Kaunatattu, yanzu mu 'ya'yan Allahne, kuma ba a bayyana mana yadda zamu zama ba tukuna, mun sani sa'adda Almasihu zai bayyana, zamu zama kamarsa, domin zamu ganshi kamar yadda yake.
Dear friends, we are God’s Children now; what we shall be has not yet been revealed. What we do know is that, when it is revealed, we shall be like Christ; because we shall see him as he is.
3 Dukkan wanda yake da wannan bege game da gidan gobe ya kan tsarkake kansa, kamar yadda shima yake da tsarki.
And every one who has this hope with regard to Christ tries to make himself pure — as Christ is pure.
4 Dukkan wanda yaci gaba da yin zunubi yana ketare shari'a kenan. Gama zunubi ketare shari'a ne.
Every one who lives sinfully is living in violation of Law. Sin is violation of Law.
5 Kun sani Almasihu ya bayyana domin ya dauke zunubai ne. Kuma a cikinsa babu zunubi.
And you know that Christ appeared to take away our sins; and in him Sin has no place.
6 Ba wanda zai kasance a cikinsa da zai cigaba da yin zunubi. Ba wanda zai ci gaba da aikata zunubi da zai ce ya sanshi, ko kuma ya ganshi.
No one who maintains union with him lives in sin; no one who lives in sin has ever really seen him or learned to know him.
7 'Ya'yana kaunatattu, kada ku bari kowa ya baudar da ku, wanda yake aikata adalci shi adali ne, kamar yadda Almasihu yake adali.
My Children, do not let any one mislead you. He who lives righteously is righteous — as Christ is righteous.
8 Wanda yake aikata zunubi na ibilis ne, gama ibilis yayi zunubi tun daga farko. Dalilin haka ne Dan Allah ya bayyana, domin ya rushe ayyukan ibilis.
He who lives sinfully belongs to the Devil, for the Devil has sinned from the first. It was for this that the Son of God appeared, that he might undo the Devil’s work.
9 Duk wanda aka haife shi daga Allah ba ya yin zunubi, saboda irin Allah na cikinsa. Ba zaya iya ci gaba da yin zunubi ba domin an haife shi daga wurin Allah.
No one who has received the new Life from God lives sinfully, because the very nature of God dwells within him; and he cannot live in sin, because he has received the new Life from God.
10 Ta haka ne ake bambanta 'ya'yan Allah da 'ya'yan ibilis. Dukkan wanda baya aikata adalci ba na Allah bane; haka kuma wanda ba ya kaunar dan'uwansa.
By this the Children of God are distinguished from the Children of the Devil — No one who lives unrighteously comes from God, and especially the man who does not love his Brother.
11 Domin wannan shine sakon da kuka ji tun daga farko: cewa mu kaunaci junanmu,
For these are the Tidings that we heard from the first — that we are to love one another.
12 ba kamar Kayinu ba wanda yake na shaidan kuma ya kashe dan'uwansa. Me yasa ya kashe shi? Saboda ayyukansa miyagu ne, na dan'uwansa kuma masu adalci ne.
We must not be like Cain, who belonged to the Evil One and killed his brother. And why did he kill him? It was because his life was bad while his brother’s was good.
13 Kada kuyi mamaki 'yan'uwana, idan duniya ta ki ku.
Do not wonder, Brothers, if the world hates you.
14 Mun sani mun ratsa mutuwa zuwa cikin rai, saboda muna kaunar 'yan'uwa. Dukkan wanda ba ya yin kauna, shi matacce ne.
We know that we have passed out of Death into Life, because we love our Brothers. The man who does not love remains in a state of Death.
15 Dukkan wanda yake kin dan'uwansa, mai kisan kai ne. Kun kuma sani babu rai na har abada a cikin mai kisankai. (aiōnios g166)
Every one who hates his Brother is a murderer; and you know that no murderer has Immortal Life within him. (aiōnios g166)
16 Ta wurin haka muka san kauna, da ya ke Almasihu ya bayar da ransa saboda mu. Mu ma ya kamata mu bada ranmu saboda 'yan'uwamu.
We have learned to know what love is from this — that Christ laid down his life on our behalf. Therefore we also ought to lay down our lives on behalf of our Brothers.
17 Amma duk wanda yake da kayan duniya, ya ga dan'uwansa cikin bukata, kuma bai ji tausayinsa ba, ta yaya kaunar Allah ke cikinsa?
But, if any one has worldly possessions, and yet looks on while his Brother is in want, and steels his heart against him, how can it be said that the love of God is within him?
18 'Ya'yana kaunatattu, kada muyi kauna ta fatar baki kawai, amma muyi aikin kauna da gaskiya.
My children, do not let our love be mere words, or end in talk; let it be true and show itself in acts.
19 Ta wurin haka mun sani mu masu gaskiya ne kuma mun tabbatar da zuciyarmu a gabansa.
By that we shall know that we are on the side of the Truth; and we shall satisfy ourselves in God’s sight,
20 Gama idan zuciyarmu bata kayar damu ba, Allah ya fi zuciyarmu girma, kuma yana sane da kome.
that if our conscience condemns us, yet God is greater than our conscience and knows everything.
21 Kaunatattu, idan zuciyarmu bata kashe mu ba, muna da gabagadi a gaban Allah.
Dear friends, if our conscience does not condemn us, then we approach God with confidence,
22 Kuma duk abin da muka nema zamu samu a wurinsa, saboda muna kiyaye dokokinsa, muna yin abubuwan da suka gamshe shi.
and we receive from him whatever we ask, because we are laying his commands to heart, and are doing what is pleasing in his sight.
23 Kuma ummurninsa kenan: mu bada gaskiya ga sunan Dansa Yesu Almasihu, mu yi kaunar juna kuma kamar yanda ya bamu wannan doka.
His Command is this — that we should put our trust in the Name of his Son, Jesus Christ, and love one another, in accordance with the Command that he gave us.
24 Duk wanda yake kiyaye umarnin Allah, yana cikinsa, Allah kuma yana cikin mutumin. Ta haka muka gane cewa yana cikinmu, Ta wurin Ruhu, wanda ya bamu.
And he who lays his commands to heart maintains union with Christ, and Christ with him. And by this we know that Christ maintains union with us — by our possession of the Spirit which he gave us.

< 1 Yohanna 3 >