< 1 Yohanna 1 >
1 Abin nan da yake tun daga farko, wanda muka ji, wanda muka gani da idanunmu, wanda muka gani hannuwanmu suka kama, a wajen maganar rai.
That which was from the beginning, which we have listened to, which we have seen with our own eyes, and our own hands have handled concerning the Word of Life--
2 Ran kuwa aka baiyyana shi, muka gani, muka bada shaida, muka gaya maku labarin rai na har abada, wanda da yake a wurin Uba, aka kuma sanar da mu. (aiōnios )
the Life was manifested, and we have seen and bear witness, and we declare unto you the Life of the Ages which was with the Father and was manifested to us-- (aiōnios )
3 Wannan da muka gani muka ji muka baku labari, domin kuyi zumunci da mu, zumuncinmu kuwa tare da Uba yake da Dansa Yesu Almasihu.
that which we have seen and listened to we now announce to you also, in order that you also may have fellowship in it with us, and this fellowship with us is fellowship with the Father and with His Son Jesus Christ.
4 Haka nan, muna rubuta maku wadannan abubuwa domin farin cikinmu ya cika.
And we write these things in order that our joy may be made complete.
5 Wannan shi ne sakon da muka ji daga wurinsa mu kuwa muka sanar da ku: Allah haske ne a wurinsa kuwa babu duhu ko kadan.
This is the Message which we have heard from the Lord Jesus and now deliver to you--God is Light, and in Him there is no darkness.
6 Idan mun ce muna zumunci da shi kuma muna tafiya cikin duhu, muna yin karya kuma bama aikata gaskiya.
If, while we are living in darkness, we profess to have fellowship with Him, we speak falsely and are not adhering to the truth.
7 Amma idan muna tafiya cikin haske kamar yadda yake cikin haske, muna zumunci da juna, jinin Yesu Dansa ya wankemu daga dukka zunubi.
But if we live in the light as He is in the light, we have fellowship with one another, and the blood of Jesus, His Son, cleanses us from all sin.
8 Idan mun ce bamu da zunubi, muna rudin kanmu kenan, ba kuma gaskiya a cikinmu.
If we claim to be already free from sin, we lead ourselves astray and the truth has no place in our hearts.
9 Amma idan mun fadi zunubanmu, shi mai aminci ne, mai adalci da zai gafarta mana zunubanmu, ya kuma wankemu daga dukkan rashin adalci.
If we confess our sins, He is so faithful and just that He forgives us our sins and cleanses us from all unrighteousness.
10 Idan mun ce bamu yi zunubi ba, mun mai da shi makaryaci kenan, maganarsa kuma bata cikinmu.
If we deny that we have sinned, we make Him a liar, and His Message has no place in our hearts.