< 1 Korintiyawa 1 >
1 Bulus, kirayayye daga Almsihu Yesu don zama manzo ta wurin nufin Allah, da dan'uwanmu Sastanisu,
Paul, called to be an apostle of Jesus Christ through the will of God, and our brother Sosthenes,
2 zuwa ga Ikilisiyar Allah da ke korinti, zuwa ga wadanda aka kebe su cikin Almasihu Yesu, wadanda aka kira domin su zama al'umma maitsarki. Muna kuma rubuta wa dukan masu kira bisa sunan Ubangijinmu Yesu Almasihu a ko'ina, wato Ubangijinsu da Ubangijinmu kuma.
to the assembly of God which is at Corinth—those who are sanctified in Christ Jesus, called saints, with all who call on the name of our Lord Jesus Christ in every place, both theirs and ours:
3 Bari alheri da salama su zo gare ku daga Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Almasihu.
Grace to you and peace from God our Father and the Lord Jesus Christ.
4 Kodayaushe ina gode wa Allahna domin ku, saboda alherin Allah da Almasihu Yesu ya yi maku.
I always thank my God concerning you for the grace of God which was given you in Christ Jesus,
5 Ya ba ku arziki ta kowace hanya, cikin dukkan magana da dukkan ilimi.
that in everything you were enriched in him, in all speech and all knowledge—
6 Kamar yadda shaida game da Almasihu ta tabbata gaskiya a tsakaninku.
even as the testimony of Christ was confirmed in you—
7 Saboda haka baku rasa wata baiwa ta ruhaniya ba yayinda kuke marmarin jiran bayyanuwar Ubangijinmu Yesu Almasihu.
so that you come behind in no gift, waiting for the revelation of our Lord Jesus Christ,
8 Zai kuma karfafa ku zuwa karshe, saboda ku zama marasa aibi a ranar Ubangijinmu Yesu Almasihu.
who will also confirm you until the end, blameless in the day of our Lord Jesus Christ.
9 Allah mai aminci ne shi wanda ya kira ku zuwa zumunta ta Dansa, Yesu Almasihu Ubangijimu.
God is faithful, through whom you were called into the fellowship of his Son, Jesus Christ our Lord.
10 Ina rokon ku, yan'uwa, cikin sunan Ubangijinmu Yesu Almasihu, ku yarda da juna, kada tsattsaguwa ta kasance tsakanin ku. Ina rokon ku ku zama da zuciya daya da kuma nufi daya.
Now I beg you, brothers, through the name of our Lord, Jesus Christ, that you all speak the same thing, and that there be no divisions among you, but that you be perfected together in the same mind and in the same judgment.
11 Gama mutanen gidan Kulowi sun kawo kara cewa akwai tsattsaguwa a cikin ku.
For it has been reported to me concerning you, my brothers, by those who are from Chloe’s household, that there are contentions among you.
12 Ina nufin: kowannen ku na cewa, “Ina bayan Bulus,” ko “Ina bayan Afollos,” ko “Ina bayan Kefas,” ko “Ina bayan Almasihu.”
Now I mean this, that each one of you says, “I follow Paul,” “I follow Apollos,” “I follow Cephas,” and, “I follow Christ.”
13 Almasihu a rarrabe yake? An gicciye Bulus domin ku? Ko an yi maku baftisma a cikin sunan Bulus?
Is Christ divided? Was Paul crucified for you? Or were you baptized into the name of Paul?
14 Na godewa Allah domin ban yi wa wanin ku baftisma ba, sai dai Kirisfus da Gayus.
I thank God that I baptized none of you except Crispus and Gaius,
15 Na yi wannan saboda kada wani ya ce an yi maku baftisma a cikin sunana.
so that no one should say that I had baptized you into my own name.
16 (Na kuma yi wa iyalin gidan Sitifanas baftisma. Banda haka, ban sani ko na yi wa wani baftisma ba.)
(I also baptized the household of Stephanas; besides them, I do not know whether I baptized any other.)
17 Gama Almasihu bai aiko ni domin yin baftisma ba, amma domin yin wa'azin bishara. Bai aiko ni domin in yi wa'azi da kalmomin hikimar mutum ba, saboda kada giciyen Almasihu ya rasa ikonsa.
For Christ sent me not to baptize, but to preach the Good News—not in wisdom of words, so that the cross of Christ would not be made void.
18 Gama wa'azin gicciye wauta ne ga wadanda su ke mutuwa. Amma cikin wadanda Allah ke ceto, ikon Allah ne.
For the word of the cross is foolishness to those who are dying, but to us who are being saved it is the power of God.
19 Gama a rubuce yake, “Zan watsar da hikimar masu hikima. Zan dode fahimtar masu basira.”
For it is written, “I will destroy the wisdom of the wise. I will bring the discernment of the discerning to nothing.”
20 Ina mai hikima? Ina masani? Ina mai muhawara na duniyan nan? Allah bai juya hikimar duniya zuwa wauta ba? (aiōn )
Where is the wise? Where is the scribe? Where is the debater of this age (aiōn )? Has not God made foolish the wisdom of this world?
21 Tunda duniya cikin hikimarta bata san Allah ba, ya gamshi Allah ta wurin wautar wa'azi ya ceci masu bada gaskiya.
For seeing that in the wisdom of God, the world through its wisdom did not know God, it was God’s good pleasure through the foolishness of the preaching to save those who believe.
22 Gama Yahudawa suna bidar al'ajibai, Helinawa kuma suna neman hikima.
For Jews ask for signs, Greeks seek after wisdom,
23 Amma muna wa'azin Almasihu gicciyayye, dutsen tuntube ga yahudawa da kuma wauta ga Helinawa.
but we preach Christ crucified, a stumbling block to Jews and foolishness to Greeks,
24 Amma ga wadanda Allah ya kira, Yahudawa da Helinawa, muna wa'azin Almasihu a matsayin iko da kuma hikimar Allah.
but to those who are called, both Jews and Greeks, Christ is the power of God and the wisdom of God;
25 Gama wautar Allah tafi mutane hikima, kuma rashin karfin Allah yafi mutane karfi.
because the foolishness of God is wiser than men, and the weakness of God is stronger than men.
26 Dubi kiranku, yan'uwa. Ba dukkan ku ke da hikima a ma'aunin mutane ba. Ba dukkan ku ke da iko ba. Ba dukkan ku ke da haifuwa ta sarauta ba.
For you see your calling, brothers, that not many are wise according to the flesh, not many mighty, and not many noble;
27 Amma Allah ya zabi abubuwan da suke wofi na duniya domin ya kunyatar da masu hikima. Allah ya zabi abin da ke marar karfi a duniya domin ya kunyatar da abinda ke mai karfi.
but God chose the foolish things of the world that he might put to shame those who are wise. God chose the weak things of the world that he might put to shame the things that are strong.
28 Allah ya zabi abinda ke marar daraja da kuma renanne a duniya. Ya ma zabi abubuwan da ake dauka ba komai ba, domin ya wofinta abubuwan da ake dauka masu daraja.
God chose the lowly things of the world, and the things that are despised, and the things that do not exist, that he might bring to nothing the things that exist,
29 Ya yi wannan ne domin kada wani ya sami dalilin fahariya a gabansa.
that no flesh should boast before God.
30 Domin abinda Allah ya yi, yanzu kuna cikin Almasihu Yesu, wanda ya zamar mana hikima daga Allah. Ya zama adalcinmu, da tsarkinmu da fansarmu.
Because of him, you are in Christ Jesus, who was made to us wisdom from God, and righteousness and sanctification, and redemption,
31 A sakamakon haka, kamar yadda nassi ya ce, “Bari mai yin fahariya, ya yi fahariya cikin Ubangiji.”
that, as it is written, “He who boasts, let him boast in the Lord.”