< 1 Korintiyawa 7 >

1 Game da abubuwan da kuka rubuto: “Yayi kyau ga mutum kada ya taba mace.”
اَپَرَنْچَ یُشْمابھِ رْماں پْرَتِ یَتْ پَتْرَمَلیکھِ تَسْیوتَّرَمیتَتْ، یوشِتوسْپَرْشَنَں مَنُجَسْیَ وَرَں؛
2 Amma Saboda jarabobi na ayyukan fasikanci masu yawa, ya kamata kowane mutum ya kasance da matarsa, kowace mace kuma ta kasance da mijinta.
کِنْتُ وْیَبھِچارَبھَیادْ ایکَیکَسْیَ پُںسَح سْوَکِییَبھارْیّا بھَوَتُ تَدْوَدْ ایکَیکَسْیا یوشِتو پِ سْوَکِییَبھَرْتّا بھَوَتُ۔
3 Kowanne maigidanci ya ba matarsa hakin ta, kuma kowace mace ta ba maigidan ta hakinsa na saduwa da juna.
بھارْیّایَے بھَرْتْرا یَدْیَدْ وِتَرَنِییَں تَدْ وِتِیرْیَّتاں تَدْوَدْ بھَرْتْرےپِ بھارْیَّیا وِتَرَنِییَں وِتِیرْیَّتاں۔
4 Matan ba ta da iko akan jikin ta amma maigidan ne. Haka ma, maigidan bashi da iko akan jikinsa amma matar ce.
بھارْیّایاح سْوَدیہے سْوَتْوَں ناسْتِ بھَرْتُّریوَ، تَدْوَدْ بھَرْتُّرَپِ سْوَدیہے سْوَتْوَں ناسْتِ بھارْیّایا ایوَ۔
5 Kada ku hana wa junanku saduwa, sai dai da yardar junanku domin wani dan lokaci. Kuyi haka domin ku bada kanku ga addu'a. Daganan sai ku sake saduwa, domin kada Shaidan ya jarabce ku saboda rashin kamun kanku.
اُپوشَنَپْرارْتھَنَیوح سیوَنارْتھَمْ ایکَمَنْتْرَناناں یُشْماکَں کِیَتْکالَں یاوَدْ یا پرِتھَکْسْتھِتِ رْبھَوَتِ تَدَنْیو وِچّھیدو یُشْمَنْمَدھْیے نَ بھَوَتُ، تَتَح پَرَمْ اِنْدْرِیانامْ اَدھَیرْیّاتْ شَیَتانْ یَدْ یُشْمانْ پَرِیکْشاں نَ نَییتْ تَدَرْتھَں پُنَریکَتْرَ مِلَتَ۔
6 Amma ina fada maku wadannan abubuwa ne a matsayin nuni, ba a matsayin umurni ba.
ایتَدْ آدیشَتو نَہِ کِنْتْوَنُجْناتَ ایوَ مَیا کَتھْیَتے،
7 Na so da kowa da kowa kamar ni yake. Amma kowa na da baiwarsa daga wurin Allah. Wani na da irin wannan baiwar, wani kuma waccan.
یَتو مَماوَسْتھیوَ سَرْوَّمانَوانامَوَسْتھا بھَوَتْوِتِ مَمَ وانْچھا کِنْتْوِیشْوَرادْ ایکینَیکو وَرونْیینَ چانْیو وَرَ اِتّھَمیکَیکینَ سْوَکِییَوَرو لَبْدھَح۔
8 Ga marasa aure da gwamraye, Ina cewa, yana da kyau a garesu su zauna ba aure, kamar yadda nike.
اَپَرَمْ اَکرِتَوِواہانْ وِدھَواشْچَ پْرَتِ مَمَیتَنِّویدَنَں مَمیوَ تیشامَوَسْتھِتِ رْبھَدْرا؛
9 Amma idan baza su iya kame kansu ba, ya kamata su yi aure. Gama yafi masu kyau su yi aure da su kuna da sha'awa.
کِنْچَ یَدِ تَیرِنْدْرِیانِ نِیَنْتُں نَ شَکْیَنْتے تَرْہِ وِواہَح کْرِیَتاں یَتَح کامَدَہَنادْ وْیُوڈھَتْوَں بھَدْرَں۔
10 Ga masu aure kwa, ina bada wannan umarni- ba ni ba, amma Ubangiji: “Kada mace ta rabu da mijinta.”
یے چَ کرِتَوِواہاسْتے مَیا نَہِ پْرَبھُنَیوَیتَدْ آجْناپْیَنْتے۔
11 Amma idan har ta rabu da mijinta, sai ta zauna ba aure ko kuma ta shirya da shi. Haka kuma “Kada miji ya saki matarsa.”
بھارْیّا بھَرْتّرِتَح پرِتھَکْ نَ بھَوَتُ۔ یَدِ وا پرِتھَگْبھُوتا سْیاتْ تَرْہِ نِرْوِواہا تِشْٹھَتُ سْوِییَپَتِنا وا سَنْدَدھاتُ بھَرْتّاپِ بھارْیّاں نَ تْیَجَتُ۔
12 Amma ga sauran ina cewa-Ni, ba Ubangiji ba-idan wani dan'uwa yana da mata wadda ba mai bi ba, kuma idan ta yarda ta zauna da shi, to kada ya sake ta.
اِتَرانْ جَنانْ پْرَتِ پْرَبھُ رْنَ بْرَوِیتِ کِنْتْوَہَں بْرَوِیمِ؛ کَسْیَچِدْ بھْراتُرْیوشِدْ اَوِشْواسِنِی سَتْیَپِ یَدِ تینَ سَہَواسے تُشْیَتِ تَرْہِ سا تینَ نَ تْیَجْیَتاں۔
13 Idan kuwa mace tana da miji marar bi, idan ya yarda ya zauna tare da ita, to kada ta kashe aure da shi.
تَدْوَتْ کَسْیاشْچِدْ یوشِتَح پَتِرَوِشْواسِی سَنَّپِ یَدِ تَیا سَہَواسے تُشْیَتِ تَرْہِ سَ تَیا نَ تْیَجْیَتاں۔
14 Gama miji marar bada gaskiya ya zama kebabbe saboda matarsa, sannan mata marar bada gaskiya ta zama kebbiya saboda mijinta mai bi. In ba haka ba 'ya'yanku za su zama marasa tsarki, amma a zahiri su kebabbu ne.
یَتووِشْواسِی بھَرْتّا بھارْیَّیا پَوِتْرِیبھُوتَح، تَدْوَدَوِشْواسِنِی بھارْیّا بھَرْتْرا پَوِتْرِیبھُوتا؛ نوچیدْ یُشْماکَمَپَتْیانْیَشُچِینْیَبھَوِشْیَنْ کِنْتْوَدھُنا تانِ پَوِتْرانِ سَنْتِ۔
15 Amma idan abokin aure marar bi ya fita, a bar shi ya tafi. A irin wannan hali, dan'uwa ko 'yar'uwa ba a daure suke ga alkawarinsu ba. Allah ya kira mu da mu zauna cikin salama.
اَوِشْواسِی جَنو یَدِ وا پرِتھَگْ بھَوَتِ تَرْہِ پرِتھَگْ بھَوَتُ؛ ایتینَ بھْراتا بھَگِنِی وا نَ نِبَدھْیَتے تَتھاپِ وَیَمِیشْوَرینَ شانْتَیے سَماہُوتاح۔
16 Yaya kika sani, ke mace, ko za ki ceci mijinki? ko yaya ka sani, kai miji, ko za ka ceci matarka?
ہے نارِ تَوَ بھَرْتُّح پَرِتْرانَں تْوَتّو بھَوِشْیَتِ نَ ویتِ تْوَیا کِں جْنایَتے؟ ہے نَرَ تَوَ جایایاح پَرِتْرانَں تْوَتّے بھَوِشْیَتِ نَ ویتِ تْوَیا کِں جْنایَتے؟
17 Bari dai kowa ya yi rayuwar da Ubangiji ya aiyana masa, kamar yadda Allah ya kirawo shi. Wannan ce ka'idata a dukkan ikilisiyu.
ایکَیکو جَنَح پَرَمیشْوَرالَّبْدھَں یَدْ بھَجَتے یَسْیانْچاوَسْتھایامْ اِیشْوَریناہْوایِ تَدَنُسارینَیواچَرَتُ تَدَہَں سَرْوَّسَماجَسْتھانْ آدِشامِ۔
18 Mutum na da kaciya sa'adda aka kira shi ga bada gaskiya? Kada yayi kokarin bayyana kamar marar kaciya. Mutum ba shi da kaciya sa'adda aka kira ga bangaskiya? To kada ya bidi kaciya.
چھِنَّتْوَگْ بھرِتْوا یَ آہُوتَح سَ پْرَکرِشْٹَتْوَکْ نَ بھَوَتُ، تَدْوَدْ اَچھِنَّتْوَگْ بھُوتْوا یَ آہُوتَح سَ چھِنَّتْوَکْ نَ بھَوَتُ۔
19 Gama kaciya ko rashin kaciya ba shine mahimmin abu ba. Mahimmin abu shine biyayya da dokokin Allah.
تْوَکْچھیدَح سارو نَہِ تَدْوَدَتْوَکْچھیدوپِ سارو نَہِ کِنْتْوِیشْوَرَسْیاجْناناں پالَنَمیوَ۔
20 Kowa ya tsaya cikin kiran da yake lokacin da Allah ya kira shi ga bada gaskiya.
یو جَنو یَسْیامَوَسْتھایاماہْوایِ سَ تَسْیامیواوَتِشْٹھَتاں۔
21 Kai bawa ne lokacin da Allah ya kirawo ka? Kada ka damu da haka. Amma idan kana da zarafin samun 'yanci, ka yi haka.
داسَح سَنْ تْوَں کِماہُوتوسِ؟ تَنْما چِنْتَیَ، تَتھاچَ یَدِ سْوَتَنْتْرو بھَوِتُں شَکْنُیاسْتَرْہِ تَدیوَ ورِنُ۔
22 Domin wanda Ubangiji ya kira shi lokacin da yake bawa, shi 'yantacce ne na Ubangiji. Hakanan kuma, wanda shike 'yantacce lokacin da aka kira shi ga bada gaskiya, Bawan Almasihu ne.
یَتَح پْرَبھُناہُوتو یو داسَح سَ پْرَبھو رْموچِتَجَنَح۔ تَدْوَدْ تیناہُوتَح سْوَتَنْتْرو جَنوپِ کھْرِیشْٹَسْیَ داسَ ایوَ۔
23 An saye ku da tsada, donhaka kada ku zama bayin mutane.
یُویَں مُولْیینَ کْرِیتا اَتو ہیتو رْمانَواناں داسا ما بھَوَتَ۔
24 Yan'uwa, a kowace irin rayuwa kowannenmu ke ciki lokacin da aka kira mu ga bada gaskiya, bari mu tsaya a haka.
ہے بھْراتَرو یَسْیامَوَسْتھایاں یَسْیاہْوانَمَبھَوَتْ تَیا سَ اِیشْوَرَسْیَ ساکْشاتْ تِشْٹھَتُ۔
25 Game da wadanda basu taba aure ba, ba ni da wani umarni daga wurin Ubangiji. Amma ina bada ra'ayina kamar mutum wanda, ta wurin jinkan Allah, yake yardajje.
اَپَرَمْ اَکرِتَوِواہانْ جَنانْ پْرَتِ پْرَبھوح کوپْیادیشو مَیا نَ لَبْدھَح کِنْتُ پْرَبھورَنُکَمْپَیا وِشْواسْیو بھُوتوہَں یَدْ بھَدْرَں مَنْیے تَدْ وَدامِ۔
26 Don haka, Ina ganin saboda yamutsin dake tafe ba da jimawa ba, ya yi kyau mutum ya zauna yadda yake.
وَرْتَّماناتْ کْلیشَسَمَیاتْ مَنُشْیَسْیانُوڈھَتْوَں بھَدْرَمِتِ مَیا بُدھْیَتے۔
27 Kana daure da mace? Kada ka nemi 'yanci daga gare ta. Baka daure da mace? Kada ka nemi auren mace.
تْوَں کِں یوشِتِ نِبَدّھوسِ تَرْہِ موچَنَں پْراپْتُں ما یَتَسْوَ۔ کِں وا یوشِتو مُکْتوسِ؟ تَرْہِ جایاں ما گَویشَیَ۔
28 Amma idan ka yi aure, ba ka yi zunubi ba. Kuma idan mace marar aure ta yi aure, bata yi zunubi ba. Saidai su wadanda suka yi aure za sha wahalhalu iri-iri a yayinda suke raye, kuma ina so in raba ku da su.
وِواہَں کُرْوَّتا تْوَیا کِمَپِ ناپارادھْیَتے تَدْوَدْ وْیُوہْیَمانَیا یُوَتْیاپِ کِمَپِ ناپَرادھْیَتے تَتھاچَ تادرِشَو دْوَو جَنَو شارِیرِکَں کْلیشَں لَپْسْییتے کِنْتُ یُشْمانْ پْرَتِ مَمَ کَرُنا وِدْیَتے۔
29 Amma wannan nike fadi ya'nuwa: lokaci ya kure. Daga yanzu, bari wadanda suke da mata suyi rayuwa kamar basu da su.
ہے بھْراتَروہَمِدَں بْرَوِیمِ، اِتَح پَرَں سَمَیوتِیوَ سَںکْشِپْتَح،
30 Masu kuka su zama kamar marasa kuka, masu farinciki kamar marasa farinciki, masu sayen abubuwa kamar marasa komai.
اَتَح کرِتَدارَیرَکرِتَدارَیرِوَ رُدَدْبھِشْچارُدَدْبھِرِوَ سانَنْدَیشْچَ نِرانَنْدَیرِوَ کْریترِبھِشْچابھاگِبھِرِواچَرِتَوْیَں
31 Wadanda suke harka da duniya kamar ba su harka da ita, domin ka'idar duniyan nan tana kawowa ga karshe.
یے چَ سَںسارے چَرَنْتِ تَے رْناتِچَرِتَوْیَں یَتَ اِہَلےکَسْیَ کَوتُکو وِچَلَتِ۔
32 Ina so ku kubuta daga damuwa mai yawa. Mutum marar aure yana tunani akan al'amuran Ubangiji, yadda zai gamshe shi.
کِنْتُ یُویَں یَنِّشْچِنْتا بھَویتیتِ مَمَ وانْچھا۔ اَکرِتَوِواہو جَنو یَتھا پْرَبھُں پَرِتوشَییتْ تَتھا پْرَبھُں چِنْتَیَتِ،
33 Amma mai aure yana tunani akan al'amuran duniya, yadda za ya gamshi matarsa,
کِنْتُ کرِتَوِواہو جَنو یَتھا بھارْیّاں پَرِتوشَییتْ تَتھا سَںسارَں چِنْتَیَتِ۔
34 hankalinsa ya rabu. Mace marar aure ko budurwa tana tunanin al'amuran Ubangiji, yadda za ta kebe kanta a jiki da ruhu. Amma mace mai aure tana tunanin al'amuran duniya, yadda za ta gamshi mijinta.
تَدْوَدْ اُوڈھَیوشِتو نُوڈھا وِشِشْیَتے۔ یانُوڈھا سا یَتھا کایَمَنَسوح پَوِتْرا بھَویتْ تَتھا پْرَبھُں چِنْتَیَتِ یا چوڈھا سا یَتھا بھَرْتّارَں پَرِتوشَییتْ تَتھا سَںسارَں چِنْتَیَتِ۔
35 Ina fadar wannan domin amfaninku ne, ba domin in takura ku ba. Na fadi wannan domin abinda ke daidai, yadda zaku bi Ubangiji ba tare da hankalinku ya rabu ba.
اَہَں یَدْ یُشْمانْ مرِگَبَنْدھِنْیا پَرِکْشِپییَں تَدَرْتھَں نَہِ کِنْتُ یُویَں یَدَنِنْدِتا بھُوتْوا پْرَبھوح سیوَنےبادھَمْ آسَکْتا بھَویتَ تَدَرْتھَمیتانِ سَرْوّانِ یُشْماکَں ہِتایَ مَیا کَتھْیَنْتے۔
36 Amma idan wani yana tunani da cewa baya yin abinda ya dace ga budurwarsa- idan ta wuce shekarun aure, kuma hakan ya zama dole- sai yayi abinda yake so. Ba zunubi yake yi ba. Sai suyi aure.
کَسْیَچِتْ کَنْیایاں یَووَنَپْراپْتایاں یَدِ سَ تَسْیا اَنُوڈھَتْوَں نِنْدَنِییَں وِواہَشْچَ سادھَیِتَوْیَ اِتِ مَنْیَتے تَرْہِ یَتھابھِلاشَں کَروتُ، ایتینَ کِمَپِ ناپَراتْسْیَتِ وِواہَح کْرِیَتاں۔
37 Amma idan ya tsaya da karfi a zuciyarsa, idan baya shan wani matsi kuma yana iya kame kansa, har ya kudurta a zuciyarsa yayi haka, wato ya kiyaye budurwarsa da yake tashi, to hakan ya yi daidai.
کِنْتُ دُحکھیناکْلِشْٹَح کَشْچِتْ پِتا یَدِ سْتھِرَمَنوگَتَح سْوَمَنوبھِلاشَسادھَنے سَمَرْتھَشْچَ سْیاتْ مَمَ کَنْیا مَیا رَکْشِتَوْییتِ مَنَسِ نِشْچِنوتِ چَ تَرْہِ سَ بھَدْرَں کَرْمَّ کَروتِ۔
38 Don haka, shi wanda ya auri budurwarsa yayi daidai, sannan shi wanda ya zabi yaki yin aure yafi yin daidai.
اَتو یو وِواہَں کَروتِ سَ بھَدْرَں کَرْمَّ کَروتِ یَشْچَ وِواہَں نَ کَروتِ سَ بھَدْرَتَرَں کَرْمَّ کَروتِ۔
39 Mace tana a daure ga mijinta a duk tsawon rayuwarsa. Amma idan mijin ya mutu, tana da 'yanci ta auri duk wanda take so ta aura, amma a cikin Ubangiji.
یاوَتْکالَں پَتِ رْجِیوَتِ تاوَدْ بھارْیّا وْیَوَسْتھَیا نِبَدّھا تِشْٹھَتِ کِنْتُ پَتْیَو مَہانِدْراں گَتے سا مُکْتِیبھُویَ یَمَبھِلَشَتِ تینَ سَہَ تَسْیا وِواہو بھَوِتُں شَکْنوتِ، کِنْتْویتَتْ کیوَلَں پْرَبھُبھَکْتاناں مَدھْیے۔
40 Amma a ganina, za ta fi farinciki idan za ta zauna yadda take. Kuma ina tunanin ni ma ina da Ruhun Allah.
تَتھاچَ سا یَدِ نِشْپَتِکا تِشْٹھَتِ تَرْہِ تَسْیاح کْشیمَں بھَوِشْیَتِیتِ مَمَ بھاوَح۔ اَپَرَمْ اِیشْوَرَسْیاتْما مَماپْیَنْتَ رْوِدْیَتَ اِتِ مَیا بُدھْیَتے۔

< 1 Korintiyawa 7 >