< 1 Korintiyawa 6 >

1 Idan wani a cikin ku yana jayayya da wani, to sai ya tafi kotu gaban alkali marar bada gaskiya, a maimakon gaban masu bi?
If one of you has a grievance against an opponent, does he dare to go to law before irreligious men and not before God's people?
2 Ko ba ku sani ba, masubi ne za su yiwa duniya shari'a? Kuma idan ku za ku yi wa duniya shari'a, sai ku kasa sasanta al'amura marasa mahimmanci?
Do you not know that God's people will sit in judgement upon the world? And if you are the court before which the world is to be judged, are you unfit to deal with these petty matters?
3 Baku sani ba mu za mu yiwa mala'iku shari'a? Balle shari'ar al'amuran wannan rai?
Do you not know that we are to sit in judgement upon angels--to say nothing of things belonging to this life?
4 Idan kuna shar'anta al'amuran yau da kullum, don me ku ke kai irin wadannan matsaloli gaban wadanda ba 'yan ikilisiya ba?
If therefore you have things belonging to this life which need to be decided, is it men who are absolutely nothing in the Church--is it they whom you make your judges?
5 Na fadi wannan domin ku kunyata. Babu wani mai hikima a cikin ku ko daya da zai iya sasanta gardama a tsakanin 'yan'uwa?
I say this to put you to shame. Has it come to this, that there does not exist among you a single wise man competent to decide between a man and his brother,
6 Amma kamar yadda yake, mai bi ya na kai karar mai bi a kotu, kuma a gaban mai shari'a wanda ba mai bi ba!
but brother goes to law with brother, and that before unbelievers?
7 Kasancewar rashin jituwa a tsakanin Kirista na nuna cewa kun rigaya kun gaza. Don me ba za ka shanye laifi ba? Don me ba za ka yarda a kware ka ba?
To say no more, then, it is altogether a defect in you that you have law-suits with one another. Why not rather endure injustice? Why not rather submit to being defrauded?
8 Amma kun yi wa wadansu laifi kun kuma cutar su, su kuwa 'yan'uwanku ne!
On the contrary you yourselves inflict injustice and fraud, and upon brethren too.
9 Ba ku sani ba marasa adalci ba za su gaji Mulkin Allah ba? Kada ku gaskata karya. Da fasikai, da masu bautar gumaka, da mazinata, da karuwai maza, da masu ludu,
Do you not know that unrighteous men will not inherit God's Kingdom? Cherish no delusion here. Neither fornicators, nor idolaters, nor adulterers, nor any who are guilty of unnatural crime,
10 da barayi, da masu zari, da mashaya, da masu zage-zage, da 'yan damfara - ba waninsu da zai gaji Mulkin Allah.
nor theives, nor avaricious people, nor any who are addicted to hard drinking, to abusive language or to greed of gain, will inherit God's Kingdom.
11 Kuma da haka wadansu a cikinku suke, amma an tsarkake ku, an mika ku ga Allah, an maida tsayuwar ku dai-dai a gaban Allah a cikin sunan Ubangji Yesu Almasihu, kuma ta wurin Ruhun Allahnmu.
And all this describes what some of you were. But now you have had every stain washed off: now you have been set apart as holy: now you have been pronounced free from guilt; in the name of our Lord Jesus Christ and through the Spirit of our God.
12 Dukkan abu halal ne a gare ni”, amma ba kowanne abu ne mai amfani ba. “Dukan abu halal ne a gare ni,” amma ba zan yarda wani abu ya mallake ni ba.
Everything is allowable to me, but not everything is profitable. Everything is allowable to me, but to nothing will I become a slave.
13 “Abinci don ciki ne, kuma ciki don abinci ne”, amma Allah za ya kawar da su duka. Ba a yi jiki saboda fasikanci ba. Maimakon haka, jiki don Ubangiji ne, kuma Ubangiji zai yi wa jiki tanaji.
Food of all kinds is meant for the stomach, and the stomach is meant for food, and God will cause both of them to perish. Yet the body does not exist for the purpose of fornication, but for the Master's service, and the Master exists for the body;
14 Allah ya tada Ubangiji, kuma za ya tashe mu ta wurin ikonsa.
and as God by His power raised the Master to life, so He will also raise us up.
15 Ba ku sani ba jikunanku gabobi ne na Almasihu? Na dauki gabobin Almasihu in hada su da karuwa? Allah ya sawwake!
Do you not know that your bodies are members of Christ? Shall I then take away the members of Christ and make them the members of a prostitute? No, indeed.
16 Ko baku sani ba dukan wanda yake hade da karuwa, ya zama jiki daya da ita kenan?
Or do you not know that a man who has to do with a prostitute is one with her in body? For God says, "The two shall become one."
17 Kamar yadda Littafi ya fadi, “Su biyun za su zama nama daya.” Amma wanda yake hade da Ubangiji ya zama ruhu daya da shi kenan.
But he who is in union with the Master is one with Him in spirit.
18 Ku gujewa fasikanci! Kowane zunubi mutum yake aikatawa a waje da jikinsa yake, amma mutum mai fasikanci yana zunubi gaba da jikinsa.
Flee from fornication. Any other sin that a human being commits lies outside the body; but he who commits fornication sins against his own body.
19 Ba ku sani ba jikinku haikali ne na Ruhu Mai-tsarki, wanda yake zaune a cikinku, wanda ku ka samu daga wurin Allah? Ba ku sani ba cewa ku ba na kanku ba ne?
Or do you not know that your bodies are a sanctuary of the Holy Spirit who is within you--the Spirit whom you have from God?
20 An saye ku da tsada. Don haka, ku daukaka Allah da jikin ku.
And you are not your own, for you have been redeemed at infinite cost. Therefore glorify God in your bodies.

< 1 Korintiyawa 6 >