< 1 Korintiyawa 2 >
1 Lokacin da na zo wurin ku, yan'uwa, ban zo da gwanintar magana ko hikima ba yayinda na yi shelar boyayyun bayanai game da Allah [ a yayinda na bada shaida game da Allah].
And so, brothers, when I came to you, announcing to you the testimony of Christ, I did not bring exalted words or lofty wisdom.
2 Domin na kudura a zuciyata kada in san komai lokacin da nake tare da ku, sai dai Yesu Almasihu, gicciyayye.
For I did not judge myself to know anything among you, except Jesus Christ, and him crucified.
3 Ina tare da ku cikin kasawa, da tsoro, da fargaba mai yawa.
And I was with you in weakness, and in fear, and with much trembling.
4 Kuma sakona da shelata basu tare da kalmomin hikima masu daukar hankali. Maimakon haka, sun zo da bayyanuwar Ruhu da iko,
And my words and preaching were not the persuasive words of human wisdom, but were a manifestation of the Spirit and of virtue,
5 saboda kada bangaskiyarku ta zama cikin hikimar mutane, amma cikin ikon Allah.
so that your faith would not be based on the wisdom of men, but on the virtue of God.
6 Yanzu muna maganar hikima ga wadanda suka ginu, amma ba hikima ta duniyan nan ba, ko ta masu mulkin wannan zamani, wadanda suke shudewa. (aiōn )
Now, we do speak wisdom among the perfect, yet truly, this is not the wisdom of this age, nor that of the leaders of this age, which shall be reduced to nothing. (aiōn )
7 Maimakon haka, muna maganar hikimar Allah ta boyayyar gaskiya, boyayyar hikima da Allah ya kaddara kafin zamanin daukakarmu. (aiōn )
Instead, we speak of the wisdom of God in a mystery which has been hidden, which God predestined before this age for our glory, (aiōn )
8 Babu wani mai mulki na zamanin nan da ya san wannan hikimar, domin inda sun gane ta a wancan lokacin, da basu gicciye Ubangijin daukaka ba. (aiōn )
something that none of the leaders of this world have known. For if they had known it, they would never have crucified the Lord of glory. (aiōn )
9 Amma kamar yadda yake a rubuce, “Abubuwan da babu idon da ya gani, babu kunnen da ya ji, babu zuciyar da ta yi tsammanin sa, abubuwan da Allah ya shirya wa wadanda suke kaunarsa.
But this is just as it has been written: “The eye has not seen, and the ear has not heard, nor has it entered into the heart of man, what things God has prepared for those who love him.”
10 Wadannan ne abubuwan da Allah ya bayyana mana ta wurin Ruhu. Gama Ruhu yana bincika komai, har ma abubuwa masu zurfi na Allah.
But God has revealed these things to us through his Spirit. For the Spirit searches all things, even the depths of God.
11 Gama wanene ya san tunanin mutum, sai dai ko ruhun mutumin da ke cikinsa? Haka ma, babu wanda ya san abubuwa masu zurfi na Allah sai dai Ruhun Allah.
And who can know the things that are of a man, except the spirit which is within that man? So also, no one knows the things which are of God, except the Spirit of God.
12 Ba mu karbi ruhu na duniya ba, amma Ruhun da ya zo daga wurin Allah, domin mu san abubuwan da aka bamu a sake daga wurin Allah.
But we have not received the spirit of this world, but the Spirit who is of God, so that we may understand the things that have been given to us by God.
13 Muna maganar wadannan abubuwa da kalmomin da hikimar da mutum baza ta iya koyarwa ba, amma wadanda Ruhu ke koyar da mu. Ruhu yana fassara kalmomi na ruhaniya da hikima ta ruhaniya.
And we are also speaking of these things, not in the learned words of human wisdom, but in the doctrine of the Spirit, bringing spiritual things together with spiritual things.
14 Mutum marar ruhaniya ba ya karbar abubuwan da suke daga Ruhun Allah, gama wauta suke a gareshi. Ba zai iya sanin su ba domin Ruhu ne yake bayyana su.
But the animal nature of man does not perceive these things that are of the Spirit of God. For it is foolishness to him, and he is not able to understand it, because it must be examined spiritually.
15 Shi wanda yake mai ruhaniya yana shari'anta dukan abubuwa, amma shi baya karkashin shari'ar sauran mutane.
But the spiritual nature of man judges all things, and he himself may be judged by no man.
16 “Wa zai iya sanin zuciyar Ubangiji, da zai iya ba shi umarni?” Amma mu muna da lamiri irin na Almasihu.
For who has known the mind of the Lord, so that he may instruct him? But we have the mind of Christ.