< 1 Korintiyawa 15 >
1 Yanzu ina tunashshe ku 'yan'uwa, game da bisharar nan da nake shelarwa, wadda kuka karba kuke kuma dogara da ita.
Now I declare to you, brothers, the Good News which I preached to you, which also you received, in which you also stand,
2 Da wannan bishara aka yi maku ceto, idan kuka rike wa'azi da na yi maku da karfi, sai in dama kun gaskanta a banza.
by which also you are saved, if you hold firmly the word which I preached to you—unless you believed in vain.
3 Domin na baku muhimmin sako kamar na farko da na karba: cewa Almasihu ya mutu domin zunubanmu, bisa ga nassosi,
For I delivered to you first of all that which I also received: that Christ died for our sins according to the Scriptures,
4 cewa kuma an bizne shi, ya kuwa tashi daga matattu a rana ta uku bisa ga nassosi.
that he was buried, that he was raised on the third day according to the Scriptures,
5 Cewa kuma ya bayyana ga Kefas, sa'an nan ga sha biyun.
and that he appeared to Cephas, then to the twelve.
6 Daga nan ya bayyana ga 'yan'uwa sama da dari biyar a lokaci guda. Wadanda mafi yawan su na da rai har yau, amma wasun su sun yi barci.
Then he appeared to over five hundred brothers at once, most of whom remain until now, but some have also fallen asleep.
7 Daga nan ya bayyana ga Yakubu, da kuma ga manzannin duka.
Then he appeared to James, then to all the apostles,
8 A karshe, sai ya bayyana a gare ni, kamar dan da aka haifa bakwaini.
and last of all, as to the child born at the wrong time, he appeared to me also.
9 Gama ni ne mafi kankanta a cikin manzanni. Ban cancanci a kira ni manzo ba, domin na tsanantawa ikklisiyar Allah.
For I am the least of the apostles, who is not worthy to be called an apostle, because I persecuted the assembly of God.
10 Amma saboda alherin Ubangiji ina matsayin da nake a yau, kuma alherin sa da ke ciki na ba a banza yake ba. A maimako, nayi aiki tukuru fiye da su duka. Amma duk da haka ba ni bane, amma alherin Allah da ke tare da ni.
But by the grace of God I am what I am. His grace which was given to me was not futile, but I worked more than all of them; yet not I, but the grace of God which was with me.
11 Saboda haka ko nine ko Su, haka mukayi wa'azin, haka kuma kuka gaskata.
Whether then it is I or they, so we preach, and so you believed.
12 To idan anyi shela a matsayin cewa Yesu ya tashi daga matattu, tayaya wadansunku su ke cewa babu tashin matattu?
Now if Christ is preached, that he has been raised from the dead, how do some among you say that there is no resurrection of the dead?
13 Amma idan babu tashin matattu, Almasihu ma ai ba a tashe shi ba kenan.
But if there is no resurrection of the dead, neither has Christ been raised.
14 idan kuwa ba a tashi Almasihu ba, wa'azin mu ya zama banza kenan, haka kuma bangaskiyar ku ta zama banza.
If Christ has not been raised, then our preaching is in vain and your faith also is in vain.
15 Mun kuma zama shaidun karya game Allah kenan, muna shaida akan Allah cewa ya tashi Almasihu daga matattu alhali ko bai tashe shi ba.
Yes, we are also found false witnesses of God, because we testified about God that he raised up Christ, whom he did not raise up if it is true that the dead are not raised.
16 Domin idan babu tashin matattu, kai, ko Almasihu ma ba a tashe shi ba kenan.
For if the dead are not raised, neither has Christ been raised.
17 Idan har ba a tashi Almasihu ba, bangaskiyar ku a banza take, har yanzu kuma, kuna cikin zunuban ku.
If Christ has not been raised, your faith is vain; you are still in your sins.
18 To wadanda suka mutu cikin Almasihu kuma sun hallaka kenan,
Then they also who are fallen asleep in Christ have perished.
19 idan a wannan rayuwa ce kadai muke da bege cikin Almasihu, to cikin dukkan mutane munfi kowa zama abin tausayi.
If we have only hoped in Christ in this life, we are of all men most pitiable.
20 Amma yanzu, Almasihu ya tashi daga matattu, wanda ya sa shi ya zama nunar fari cikin tashi daga matattu.
But now Christ has been raised from the dead. He became the first fruit of those who are asleep.
21 Domin yadda mutuwa ta shigo duniya ta hanyar mutum guda, hakkan nan ma tashi daga matattu.
For since death came by man, the resurrection of the dead also came by man.
22 Gama kamar yadda a cikin Adamu duka suka mutu, haka kuma a cikin Almasihu za a rayar da duka.
For as in Adam all die, so also in Christ all will be made alive.
23 Amma kowanne da tsarinsa: Almasihu, nunan fari, sannan su wadanda ke na Almasihu za a rayar da su lokacin zuwansa.
But each in his own order: Christ the first fruits, then those who are Christ’s at his coming.
24 Sa'an nan karshen zai gabato, lokacin da Almasihu zai mika mulkin ga Allah Uba. sa'an nan ne zaya kawar da dukkan mulki, martaba da iko.
Then the end comes, when he will deliver up the Kingdom to God the Father, when he will have abolished all rule and all authority and power.
25 Gama mulkinsa zai habaka har sai ya sa dukkan makiyansa a karkashin sawayen sa.
For he must reign until he has put all his enemies under his feet.
26 Mutuwa kuwa, ita ce makiyi na karshe da za'a hallaka.
The last enemy that will be abolished is death.
27 Domin “yasa dukkan komai a karkashin ikonsa,” Amma da aka ce” yasa dukkan komai a karkashin ikonsa,” a sarari yake cewa wannan baya hada da wanda yasa dukan komai a karkashin ikonsa ba.
For, “He put all things in subjection under his feet.” But when he says, “All things are put in subjection”, it is evident that he is excepted who subjected all things to him.
28 Idan dukan abu na karkashin mulkinsa, to Dan da kansa zaya kasance a karkashin ikon shi wanda yasa komai a karkashin ikonsa. Wannan zaya kasance ne saboda Allah Uba ya zama dukkan komai cikin dukkan komai.
When all things have been subjected to him, then the Son will also himself be subjected to him who subjected all things to him, that God may be all in all.
29 ko kuma me zai faru da wadanda ake yi wa baftisma domin matattu? Idan kuwa babu tashin matattu sam sam, ina amfanin yi masu baftisma domin su?
Or else what will they do who are baptized for the dead? If the dead are not raised at all, why then are they baptized for the dead?
30 Kuma me yasa muke cikin hadari kowace sa'a?
Why do we also stand in jeopardy every hour?
31 Ina mutuwa kullum. Wannan nake furtawa ta wurin fahariya, 'yan'uwa, wadda nake da ita cikin Almasihu Yesu Ubangijinmu.
I affirm, by the boasting in you which I have in Christ Jesus our Lord, I die daily.
32 Menene ribata, a idanun mutane, idan nayi kokowa da bisashe a Afisa, idan babu tashin matattu? “bari mu ci mu sha, domin gobe zamu mutu.”
If I fought with animals at Ephesus for human purposes, what does it profit me? If the dead are not raised, then “let’s eat and drink, for tomorrow we die.”
33 Kada fa a yaudare ku, domin “tarayya da mugaye takan bata halayen kirki.”
Do not be deceived! “Evil companionships corrupt good morals.”
34 “Ku natsu! kuyi zaman adalci! kada ku cigaba da zunubi. Domin wasunku basu da sanin Allah. Ina fadar wannan domin in baku kunya.
Wake up righteously and do not sin, for some have no knowledge of God. I say this to your shame.
35 Amma wani zaya ce, “Yaya za'a yi tashin matattu? Wane irin jiki kuma zasu tashi da shi?
But someone will say, “How are the dead raised?” and, “With what kind of body do they come?”
36 Ku jahilai ne sosai! Abinda ka shuka ba zaya fara girma ba sai ya mutu.
You foolish one, that which you yourself sow is not made alive unless it dies.
37 Abinda ka shuka ba jikin da zaya kasance bane, amma kwayar irin ne kawai. Wanda zaya zama alkama ko wani abu daban.
That which you sow, you do not sow the body that will be, but a bare grain, maybe of wheat, or of some other kind.
38 Amma Allah zaya bashi jiki yadda ya zaba, ga kowane kwayar iri da nashi jikin.
But God gives it a body even as it pleased him, and to each seed a body of its own.
39 Ba duka jiki ne yake iri daya ba. A maimako, akwai jiki irin na mutane, akwai kuma wani irin na dabbobi, kuma wani jikin irin na tsuntsaye, kuma da irin na kifi.
All flesh is not the same flesh, but there is one flesh of men, another flesh of animals, another of fish, and another of birds.
40 Akwai kuma jikina na samaniya da jikina na duniya. Amma daukakar jikin samaniya wata daban ce kuma daukakar jikin duniya daban ce.
There are also celestial bodies and terrestrial bodies; but the glory of the celestial differs from that of the terrestrial.
41 Akwai daukaka irin ta rana, da kuma wata daukakar irin ta wata, da kuma wata daukakar irin ta taurari. Domin wani tauraron ya bambanta da wani wajen daukaka.
There is one glory of the sun, another glory of the moon, and another glory of the stars; for one star differs from another star in glory.
42 Haka yake a tashin matattu. Abinda aka shuka mai lalacewa ne, wanda aka tayar marar lalacewa ne.
So also is the resurrection of the dead. The body is sown perishable; it is raised imperishable.
43 An shuka shi cikin rashin daraja; an tayar da shi cikin daukaka. An shuka shi cikin rauni; an tayar da shi cikin iko.
It is sown in dishonor; it is raised in glory. It is sown in weakness; it is raised in power.
44 An shuka shi jiki na zahiri; an tayar da shi jiki na ruhaniya. Idan akwai jiki na zahiri, to akwai jiki na ruhaniya.
It is sown a natural body; it is raised a spiritual body. There is a natural body and there is also a spiritual body.
45 Haka kuma aka rubuta, “Adamu na farko ya zama rayayyen taliki.” Adamu na karshe ya zama Ruhu mai bayar da rai.
So also it is written, “The first man Adam became a living soul.” The last Adam became a life-giving spirit.
46 Amma na ruhaniyar ba shine ya fara zuwa ba amma na zahirin, daga nan na ruhaniyar.
However, that which is spiritual is not first, but that which is natural, then that which is spiritual.
47 Mutumin farkon ai daga turbaya ya fito, wato na duniya. Amma shi na biyun daga sama yake.
The first man is of the earth, made of dust. The second man is the Lord from heaven.
48 kamar yadda mutumin ya fito daga turbaya haka ma wadanda aka halitta da turbaya. kamar yadda mutumin yake daga sama haka ma wadanda ke na sama.
As is the one made of dust, such are those who are also made of dust; and as is the heavenly, such are they also that are heavenly.
49 Kamar yadda muke dauke da jiki mai kamannin turbaya, haka ma zamu kasance da kamannin mutumin sama.
As we have borne the image of those made of dust, let’s also bear the image of the heavenly.
50 To wannan na fada, 'yan'uwa, cewa nama da jini ba za su gaji mulkin Allah ba. Haka kuma mai lalacewa ba za ya gaji marar lalacewa ba.
Now I say this, brothers, that flesh and blood cannot inherit God’s Kingdom; neither does the perishable inherit imperishable.
51 Duba! ina gaya maku asirtacciyar gaskiya: Ba dukanmu zamu mutu ba, amma dukanmu za a canza mu.
Behold, I tell you a mystery. We will not all sleep, but we will all be changed,
52 Za a canza mu nan da nan, cikin keftawar ido, a kaho na karshe. Domin za a busa kaho, kuma za a tada matattu marasa lalacewa, kuma za a canza mu.
in a moment, in the twinkling of an eye, at the last trumpet. For the trumpet will sound and the dead will be raised incorruptible, and we will be changed.
53 Domin wannan jiki mai lalacewa dole ya sanya jiki marar lalacewa, kuma wannan jiki mai mutuwa dole ya sanya marar mutuwa.
For this perishable body must become imperishable, and this mortal must put on immortality.
54 Amma idan wannan jiki mai lalacewa ya sanya marar lalacewa, kuma wannan jiki mai mutuwa ya sanya marar mutuwa, sai abinda aka rubuta ya cika, “An hadiye mutuwa cikin nasara.”
But when this perishable body will have become imperishable, and this mortal will have put on immortality, then what is written will happen: “Death is swallowed up in victory.”
55 “Mutuwa, ina nasararki? Mutuwa, ina dafinki?” (Hadēs )
"Death, where is your sting? Hades (Hadēs ), where is your victory?"
56 Gama dafin mutuwa zunubi ne, kuma ikon zunubi shari'a ce.
The sting of death is sin, and the power of sin is the law.
57 Amma godiya ga Allah, wanda ya bamu nasara ta wurin Ubangijinmu Yesu Almasihu!
But thanks be to God, who gives us the victory through our Lord Jesus Christ.
58 Saboda haka, ya ku 'yan'uwana kaunatattu, ku dage kuma kada ku jijjigu. Ko yaushe ku habaka da aikin Ubangiji, domin kun san cewa aikinku cikin Ubangiji ba a banza yake ba.
Therefore, my beloved brothers, be steadfast, immovable, always abounding in the Lord’s work, because you know that your labor is not in vain in the Lord.